Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 3
yanzu, shin ko soyayya dole ce? Kc kuwa ke mayya cc wai? To na rantse da darajar iyayena idan baki fita daga sha'anina ba duk ranar da kika shiga hannuna sai kin gane kurenki". Koda gimbiya Shahriya taji haka sai tayi murmushi ta matso daf da shi sannan ta cc, "Ya kai masoyina kayi sani cewa ba komai yasa na ziyarceka ba a yanzu sai domin in ga fuskarka saboda idan ban ganta ba ba zan iya bacci ba, kuma kayi sani cewa 21 Hikaya Hamsin Basiru Aliyu Harande shi so ba dole banc, amma daga gareni za ka fara soyayyar dolc. Kuma ba komai ni ke so gareka ba illa ka bani aron zuciyarka domin ta zamowa tawa zuciyar jagora wurin ci gaba da rayuwarta. Hakan ne yasa na sa aka dauko min littafinka wanda ka fifita akaina, kuma ba zan baka shi ba har sai ka amince da bukatata". Tana kawowa nan a zancenta sai ta kai baki da niyyar ta sumbaceshi. Cikin sauri Affan ya kauda kansa, abinda ya sa gimbiya Shahriya tayi murmushi ke nan ta juya ta fice ta barshi nan yana hucin bakin ciki * * Haka dai ya kasance cıkın kurkukun har tsawon kwanaki bakwai. Lokacin ya yi kuka, ya yi bakin ciki sannan ya yi nadamar zuwa ceton Kasim da ya yi har gimbiya Shahriya ta ganshi har ma idan ya tuno cewa bai gama karatun littafin hikaya ba kuma gashi lokacin da aka basu ya kare ko yanzu ya koma ba za a bari ya shiga gasar ba, wannan ne yasa tuni ya debe 1ansa da tunaninsa a cikin masu gasar. Abinda kawai yake tunani yanzu shi ne, hanyar da zai kubuta ya shiga gidan sarautar ya kamo gimbiya Shahriya ya yi ma ta kisan wulakancin da ko a tarihi 22 Hikaya Hamsin Basiru Aliyu Harande a a taba yiwa wani mahaluki irin sa ba, domin ya wanke takaicin bakin cikin da ta cusa masa. Kansa sunkuyc yana wannan tunanin kawai sai yaji an bude kofa da karfi. Koda ya daga kai ya duba sai ya ganshi. Cikin mamaki Affan ya ce, "Ya kai Malam Basiru ya aka yi ka samu damar shigowa wannan wurin?" Koda Malam Basiru yaji haka sai ya се, "Yanzu ba lokacin wani zance bane". Cikin sauri ya sa makulli ya kwanceshi suka fita. Fitowarsu ke da wuya sai Affan ya kama hanya da niyyar shiga gidan sarautar. Cikin sauri Malam Basiru ya rikoshi ya ce, "Ina kuma za ka?" Ya amsa da cewa, "Zan je wurin gimbiya in amso littafina na hikaya". Koda Malam Basiru yaji haka sai ya dauko littafin ya mika masa ya ce, "Gashi na dauko maka". Cikin matukar mamaki da murna ya karbi littafin ya rungumeshi sannan Malam Basiru ya ja hannunsa suka rika sanda gare da tsallake masu gadin da ke kwance suna ta sharar bacci. Duhun dare ya suturtasu, har suka fito gidan ba wanda ya gansu. Suna fitowa suka iske sadauki Kasim na jiransu da dawakai guda uku. Nan da nan suka kama dawakan suka haye suka zaburesu cikin matsanaicin gudu suka rika tafiya har suka fita daga kasar Zururi suka kama daji. 23 Hikaya Hamsin Basiru Aliyu Harande Sai da suka kwana suka wuni suna tafiya da wani azababben gudu tamkar wadanda za su bar duniya baki daya. Suka wanzu suna cikin kcta kwazazzabai, duhuwowi, koguna, tudu da gangare, sai da suka kwana uku suna tafiya ba tare da cin zango ba, kuma ba su haďu da wani abu, mai cutarwa ba. A rana ta uku ne da la'asar likis sai suka fahimci cewa dawakanku sun galabaita kamar yadda suma suka galabaita musamman Malam Basiru wanda bai da jimirin wahala. Nan da nan ya yi umarnin da a yada zango domin hutawa. Koda Affan yaji haka sai hankalinsa ya tashi ya dubi Malam Basiru ya ce, "Haba Malam ya za ka ce mu yada zango tun yanzu bayan ka san tafiyar da ke gabanmu bata wasa bace?" Cikin fushi Malam Basiru ya dubeshi ya се, "Kai Affan shin ko baka da hankali ne? Kwanaki uku muna tafiya ba cin zango sannan ka ce kada mu tsaya? Shin ko bamu da jini a jiki ne? To ka yi sani cewa duk mai rai dole ne ya ba ransa hakkinta wato (hutu) kuma zafin nema baya kawo samu. Kuma ka yi sani cewa in dai ba sihiri garemu ba ba yadda za a yi mu iya isa kasar Mahbub cikin lokacin da muke so, sai idan mun isa duk bala'in da za a yi sai ka shige wannan gasar saboda haka mu kan sai mun huta". 24 Hikaya Hamsin Basiru Aliyu Harande Yana kawowa nan a zancensa sai suka fara sauke kaya shi da Kasim suka bar Affan a tsaye yana tunani, can shima sai ya sa hannu suka sauke kayan tare da kafa tanti. Bayan sun gama kafa tantin ne sai suka dauko guzurinsu suka shiga ba Ciki hakkinsa. Haka suka kasance wurin har rana ta fadi duhu ya shigo, Kasim da Affan suka je suka samo Itace suka hada wuta domin jin dumi sakamakon sanyin dake bugawa awurin, suna cikin hakane sai Affan ya dubi Mallam Basiru ya ce "Ya kai Mallam ka yi min alkawarin cewa idan muka samu nutsuwa za ka fadamin yadda kayi ka samu damar kubutar dani da yadda ka samu nasarar dauko littafin hikaya a hannun Gimbiya Shahriya." Koda Mallam yaji haka sai ya yi murmushi ya ce, "Wato wani lokaci Affan taurin kai ne da kai, Lokacin dana bukaci ka bari mu bi abin a hankali, da ka bari da bai kai ga haka ba." Ya ci gaba da cewa, "Lokacin da na ga ka wuni ka kwana ba ka dawo ba, sai na san ba shakka Gimbiya tasa an kama ka. To daga wannan lokacin ne na shiga tunanin hanyar da zan bi in kubutar da kai. Da yake ina da wani aboki mai suna Sami'u. Sami'u ya kasance shi ke dafa ma masu gadin gidan Sarki Fikihu giya, kuma lokaci zuwa lokaci ina ma kai masa ziyara gidan Sarki, 25 Hikaya Hamsin Basiru Aliyu Harande wani lokacin ma ina tayashi aikin wurin dafa giyar. Wannan ne yasa ko masu tsoron kofar gidan Sarki sun ganni basa hanani shiga saboda sun san wurin Sami'u ni ke zuwa. Ranar da ka cika kwana bakwai ne na kaima Sami'u ziyara gidan Sarki, kuma na umarci Kasim da ya yi shiri domin zamu bar garin da daddare. Ina isa gidan Sarki sai na iske Sami'u yana cikin aikin dahuwar giya, mamaki ya kamani saboda na ga kullum ana dafa duro uku ne amma yau na ga sama da diro shida. Bayan mun gaisa da Sami'u sai ya ce, "Kai Malam Basiru amma ka zo dai-dai lokacin da nike bukatarka saboda yau kan aiki ya yi min yawa ina so ka taimaka min". Koda na ji haka sai na yi murmushi na ce, "Ai na ga alama saboda yau kan na ga diro shida ne. Shin wai mi za a yi da su ne haka, ko har da dawakan gidan sun fara shan giyar ne?" Sami'u ya yi murmushi ya ce, "Ba kowa ya sa a kara yawan giyar ba face gimbiya Shahriya, saboda gobe za a yi ma ta bikin baiko da wani bakon sadauki wanda ya samu nasarar - kashe Kwadon Rijiya, shi ya sa ta ce in dafa mata duro uku na gobe, ukun kuwa na yau ne za a sha su." 26 Hikaya Hamsin Basiru Aliyu Harande Koda naji haka sai hankalina ya tashi don na san ba kowa bane face kai. Cikin yaudara na fara bugun cikinsa da cewa, "Shin ba ance sadaukin ya gudu ba? Ya aka yi ya dawo?". Sami'u ya ce, "Ban san da wannan ba, abinda na sani shi ne kwanakin bakwai da suka wuce gimbiya Shahriya ta tara dukkan masu gadin gidan nan ta ce da su idan sun ga wani sadauki mai siffa ka za-da-ka za kada a hanashi shigowa, kuma kada wani ya ce da shi kala. Ai ko ba ta jima da yin wannan maganar ba sai ga wanıan sadaukin ya shigo yana cikin tafiya ne kwatsam s. na ga an sako raga an kamashi an yi kurkuku da shi". Koda naji haka sai na cewa Sami'u, "Kai baka zaton akwai abinda gimbiya ta daukar ma wannan sadaukin har tasa ya dawo dole?" Sami'u ya ce, "Б. shakka akwai lokacin da na je kaima wasu Askarawa giya na ji wani cikin su na cewa, "Ai ba don gimbiya ta sa mun dauko mai littafin ba da ba zai kawo kanshi ba, kuma ta ce ba shakka idan bai yarda an yi musu baiko ba ba za ta bashi littafin ba." Koda naji haka sai hankalina ya dada tashi don na san al'adar kasar mu idan aka yiwa namiji baiko da mace to ba a bari yaje ko ina sai an daura musu aure. Kawai sai na kudurci yaudara a zuciyata na fakaici idon Sami'u na rika jefa kololon Banju a 27 Hikaya Hamsin Basiru Aliyu Harande cikin diron giyar sai da na saka banju a kowanne diron sannan muka ci gaba da matsa giyar. Bayan giyar ta dafu sai muka shiga aikin rabawa masu gadi ita. A lokacin da dare ya yi sai da na tabbatar da cewa na shayar da dukkan wadanda za su kawo min matsala wajen kubutar da kai ciki ko har da Sami'u bai tsira ba giya mai banju,. Bayan dan wani lokaci sai na tashi na shiga zagayen lungu-lungu, sako-sako na gidan duk inda na bi sai in yi arba da dakaru sun zube kasa suna sharar barci. Sai da na tabbatar da kowa ya yi bacci a gidan sannan na shiga sanda da labebe duhun dare ya suturta ni har na isa inda dakin gimbiya yake. Ina zuwa sai na leka wata 'yar karamar taga kawia sai na yi arba da ita zaune saman gadonta ta tasa littafin hikaya gaba tayi tagumi. Nan ne naji tana cewa, "Sadauki Affan ina sonka kuma ba shakka gobe za a yi mana baiko da kai ko kana so ko baka so. Kamar yadda Abbana ya alkawarta min." Koda naji haka sai na fada tunanin yadda zan rabata da littafin. Can sai na dauko garin banju na hura cikin tagar na koma gefe na make. Bayan 'yan dakiku sai na leka na ganta tuni banju ya gama ma ta aiki, wato ta bingire da bacci, ina ganin haka sai na sadada na bude kofar dakin na shiga na dauko littafin hikaya. Ai ko da fitowata sai 28 Hikaya Hamsin Basiru Aliyu Harande sako-sako tamkar farin dango suna cewa, "Affan oyoyo! oyoyo!!' Kafin ka ce kwabo tuni wurin ya cika da al'umma ba masaka tsinke. Malam Basiru da Kasimu kuwa mamaki suke ashe haka ake son Affan a kasarsu? To wai mi ya hana a bashi sarautar a huta. Ana cikin haka ne sai Affan ya daga hannu alamar kowa ya saurara, wurin ya yi tamkar ruwa ya ci su, ya fara magana da cewa. "Ya ku al'ummar kasata ina mai yi muku godiya bisa wannan tarba da kuka yi ba, amma sai dai ban ji dadi ba kamar yadda na ga alamar kuna ciki wani hali na tashin hankali, ko mine dalilin hakan?" Koda jama'a suka ji wannan tambayar sai suka yi shiru. Can sai wani tsohon mai yalwar furfura ya ce, "Ya kai Affan ka yi sani cewa dole ne mu shiga cikin tashin hankali saboda tunda mahaifinka ya mutu kai al'ummar wannan kasa ke son ya gajeshi, sai gashi ace sai kun je neman ilimin hikaya." Tsohon ya ci gaba da cewa, "Tun ranar da kuka bar garin nan mutane ke kidayar ranaku tare da fatan ka ri ga kowa dawowa, saboda kada ka zarce kwanakin da-aka dibar muku amma sai gashi kowa ya dawo kuma har ka wuce kwanaki sittin baka dawo ba, kuma kowa ya san cewa ba za a barka ka 31 Hikaya Hamsin Basiru Aliyu Harande shiga gasar ba saboda ka keta doka. Wannan shi ne ya samu cikin tashin hankali don mun san in ba kai ka ci wannan gasar ba to duk wanda ya ci talakawa na cikin matsanaicin bala'i". Kalaman wannan tsoho sai da suka sa Affan zub da hawaye. Cikin tattausar murya ya fara magana da cewa, "Ya ku masoyana mutanen kasata, ina mai baku hakuri akan wannan tsako da na samu. I na wannan tsaikon ya faru ne ba bisa sona ba, sai bisa wani dalili wanda ba zan iya fada muku shi ba anan, amma ina so ku kwantar hankalinku zan je fada yanzu kuma duk yadda zaa yi zan shiga wannan gasar, kuma ba makawa ni zan lashe gasar, saboda haka kowa ya koma ya ci gaba da harkokinsa kamar kullum". Yana kawowa nan a zancensa sai jama'a suka Garke da tafi da shewa suna cewa, "Sai ka yi! Sai ka yi!!" Lokacin da suka isa bakin fadar sai suka iske fadar cikin tsauraran matakan tsaro, duk inda ka duba dakaru ne cikin shirin ko ta kwana. Sannan an kara kawata fadar tayi matsanaicin kyau fiye da tunanin mai tunani. Abinda ya sa Malam basiru da Kasim suka saki baki suna kallo da mamakin yadda fadar ta kawatu haka, saboda tunda suke ba su taba ganin fada mai girma da kyawu kamar wannan ba. 32 Hikaya Hamsin Basiru Aliyu Harande sako-sako tamkar farin dango suna cewa, "Affan oyoyo! oyoyo!!! Kafin ka ce kwabo tuni wurin ya cika da al'umma ba masaka tsinke. Malam Basiru da Kasimu kuwa mamaki suke ashe haka ake son Affan a Kasarsu? To wai mi ya hana a bashi sarautar a huta. Ana cikin haka ne sai Affan ya daga hannu alamar kowa ya saurara, wurin ya yi tamkar ruwa ya ci su, ya fara magana da cewa. "Ya ku al'ummar kasata ina mai yi muku godiya bisa wannan tarba da kuka yi ba, amma sai dai ban ji dadi ba kamar yadda na ga alamar kuna ciki wani hali na tashin hankali, ko mine dalilin hakan?" Koda jama'a suka ji wannan tambayar sai suka yi shiru. Can sai wani tsohon mai yalwar furfura ya ce, "Ya kai Affan ka yi sani cewa dole ne mu shiga cikin tashin hankali saboda tunda mahaifinka ya mutu kai al'ummar wannan kasa ke son ya gajeshi, sai gashi ace sai kun je neman ilimin hikaya." Tsohon ya ci gaba da cewa, "Tun ranar da kuka bar garin nan mutane ke kidayar ranaku tare da fatan ka ri ga kowa dawowa, saboda kada ka zarce kwanakin da aka dibar muku amma sai gashi kowa ya dawo kuma har ka wuce kwanaki sittin baka dawo ba, kuma kowa ya san cewa ba za a barka ka 31 Hikaya Hamsin Basiru Aliyu Harande shiga gasar ba saboda ka keta doka. Wannan shi ne ya samu cikin tashin hankali don mun san in ba kai ka ci wannan gasar ba to duk wanda ya ci talakawa na cikin matsanaicin bala'i". Kalaman wannan tsoho sai da suka sa Affan zub da hawaye. Cikin tattausar murya ya fara magana da ccwa, "Ya ku masoyana mutanen kasata, in mai baku hakuri akan wannan tsako da na samu. I na wannan tsaikon ya faru ne ba bisa sona ba, sai bisa wani dalili wanda ba zan iya fada muku shi ba anan, amma ina so ku kwantar hankalinku zan je fada yanzu kuma duk yadda zaa yi zan shiga wannan gasar, kuma ba makawa ni zan lashe gasar, saboda haka kowa ya koma ya ci gaba da harkokinsa kamar kullum". Yana kawowa nan a zancensa sai jama'a suka Garke da tafi da shewa suna cewa, "Sai ka yi! Sai ka yi!!" Lokacin da suka isa bakin fadar sai suka iske fadar cikin tsauraran matakan tsaro, duk inda ka duba dakaru ne cikin shirin ko ta kwana. Sannan an kara kawata fadar tayi matsanaicin kyau fiye da tunanin mai tunani. Abinda ya sa Malam basiru da Kasim suka saki baki suna kallo da mamakin yadda fadar ta kawatu haka, saboda tunda suke ba su taba ganin fada mai girma da kyawu kamar wannan ba. 32 Hikaya Hamsin Basiru Aliyu Harande Bai wuce saura taku kadan su isa bakin kofar ba sai wani sadauki mai suna Kausar ya sha gabansu. Koda Affan ya ga haka sai ya dubeshi ya ce, "Shin mine ne dalilin ka na tare mana hanya?" Kausar ya amsa da cewa, "Ya shugabana kayi sani cewa tuni Shugaba Waziri Kwabis ya bamu umarnin da kada mu bari kowa ya shiga fadar sai da izininsa saboda bada cikakken tsaro da kariya ga manyamanyan-baki da Malaman Hikaya da kuma dubunan 'yan kallo da suka fito kowanne sako na duniya wadanda yanzu wannan fadar ke karbar bakunci domin shedar wannan gagarumar gasa da za a fara. Koda Affan yaji haka sai ya ce, "Kana nufin dama ba a fara wannan gasar ba?". Kausar ya ce, "Ba a fara ba saboda wasu 'yan matsaloli, amma ko shakka yau za a fara saboda cikin 'ya'yan Sarki kowa ya dawo wurin neman ilimin Hikaya, kai kadai ka rage, kuma tuni alkalan gasar sun halarta. Koda Affan yai cewa ba a fara wannan gasar ba sai murna ta kamashi. Cikin murmushi ya ce, "Ya kai Kausar na umarceka da ka je ka sanar da Waziri cewa gani na iso". Cikin sauri Kausar ya tafi domin cika umarnin Affan. Bayan wani dan lokaci da wucewar Kausar sai ga shi tafe tare da Waziri Kwabis cikin wata irin 33 Hikaya Hamsin Basiru Aliyu Harande shiga ta alfarma tamkar ma shi ne Sarkin kasar Mahbub gaba daya. Tunda suka yi arba da juna sai zuciyar Waziri ta buga, ransa ya 6aci sosai ya fara zancen zuci da ccwa. "Ashe wannan tsinannen yaron da nike zaton ya hallaka yana nan? To yanzu kamata ya yi tunda ya wuce wa'adin da aka dībar musu in yi amfani da wannan damar in kareshi cikin wannan gasar kawai." Can kuma wani 6angare na zuciyarsa ya ce, "Kai ka manta irin makircin da ka kulla masa na turashi wurin Malamin da bai san komai ba? Saboda haka ko ya shiga gasar ba zai iya tabuka komai ba, gara ma ka kyaleshi". Waziri Kwabis na kawowa nan a zancen zucinsa sai ya kyalkyale da dariyar mugunta kuma lokacin ne ya iso daf da su Affan cikin murmushin munafunci, Waziri ya rungume Affan tare da yi mai kalamai irin na dadewa ba a ga juna ba. Bayan sun nutsu ne sai Affan ya gabatar da Malam Basiru da Kasimu wurin Waziri suka gaisa. Bayan sun gama gaisawa ne sai Waziri ya ce, "Ya kai dana ka yi sani cewa bamu da wani isasshen lokaci yanzu saboda ni kadai ake jira a fara wannan 34 Hikaya Hamsin Basiru Aliyu Harande gasar, saboda haka ku shigo mu je fada domin gabatar da ku wurin Alkalan Gasar kafin a fara. Wohoho! Ai lokacin da suka shiga cikin fadar sai Malam Basiru ya saki baki yana kallon irin yadda aka kawata fadar da wasu irin kayan alatu wadanda bai taba gani ko jin labarin su ba. Wannan ne yasa ya zama tamkar wanda ke rayuwa cikin rijiya ya shigo birni. Fadar an kasata zuwa bangaroti uku, bangare na farko shi ne bangaren dubun-dubatar 'yan kallo na ciki da wajen kasar. Bangare na biyu kuwa shi ke dauke da wasu irin kujeru na alfarma wadanda aka sana'anta da ruwan farin zinare aka yi musu ado da farin dimon, kujeru guda hamsin ne kuma 'ya'yan Sarki Gulam su arba'in da tara suna saman kujerun cikin shiga ta alfarma sai sheki, suka yi tamkar taurari kujerar Sadauki Affan kawai ta rage wanda sai yanzu ya iso. Bangare ma uku kuwa, shi ne ke dauke da wasu kujeru wadanda aka kera da ruwan zallan jan zınare, aka yi musu ado da farin zinare, wadannan kujeru guda hamsin ne kuma ba kowa ke zaune kansu ba face manya-manyan mashahuran fitattun Malaman hikaya na duniya su arba'in da tara cikin shiga irin ta alfarma. Bangaren yamma na fadar kuwa wani dan tudu ne mai dauke da matattakala goma wanda ke dauke 35 Hikaya Hamsin Basiru Aliyu Harande da karagar sarautar Kasar Mahbub. Karagar sai Kyalli da walwali kawai take, gefen karagar kuwa wani dan mumbari ne aka samar saboda masu gudanar da gasar. Kai ganin yadda wannan fadar ta kawatu ne yasa Malam Basiru ya yi ajiyar zuciya ya ce, "Ba shakka tafiya mabudin ilimi ce, wanda bai tafiya ba bai sha kallo ba". Bayan Waziri Kwabis ya gabatar da su Affan gaban 'yan kallo da Alkalin Gasar ne sai ya yi musu umarnin da su je su zauna domin fara gasar ne sai ya yi musu umarni da su je su zauna domin fara gasar kai tsaye. Sadauki Affan ya zarce Gangaren da 'yan uwansa suke ya zauna saman kujerarsa abinda yasa suka cika su hamsin dai-dai. Ai ko zamansa ke da wuya sai gaba daya ya dusashe hasken van uwansa ya zame musu tamkar Wata a cikin tadra, wao shi dai ake gani, shima Kasim ya samu wuri cikin 'yan kallo ya zauna. Shi ko Malam Basiru tuni hankalinsa ya tashi jikinsa ya kama kyarma sakamakon nuna masa wurin zamansa inda ya yi arba da manya-manya gawurtattun Malaman Hikaya wadanda duniyar marubuta ke takama da su, kamar su, Abdul'aziz ibini Sani Al-Madaks, Shehu ibini Usman, Abdullahi ibni Mukhtar Al-Yaron Malam, Ibini 36 Hikaya Hamsin Basiru Aliyu Harande Shitu Al-Bature, Hassan Ibini Shu'aibu Al-Harande, Mubarak Ibini Hamza Al-Gadon Kaya, Ibn Isa AlKwalisa, Rabi'u Ibn Abubakar Al-Sharfadi, Abubakar Ibn Tanko, Ibni Tajeri mai Dodo. Da dai sauransu. Nan da nan ya fara maganar zuci da cewa, "Kai, yau asiri na ya tono, da na sani da na yi zamana gidanmu. Kai! Ina ni ina goga kafada da wadannan manyan Malamai a matsayina na karamin Almajiri?" Yana cikin wannan tunani ne har ya iso wurin su yana zuwa sai ya yi zaune dabas a kasa. Koda Malaman suka ga haka sai suka dubi juna, sannan cikin murmushi Malam Abdul'aziz Sani ya ce, "Haba Malam ya za ka zauna a kasa bayan ga kujeru wadanda aka tanadar domin ka?" Cikin rawar murya Malam Basiru ya amsa da cewa, "Haba maigida, kuna saman kujera ina sama ai na yi rashin kunya, a matsayina na almajiri". Cikin murmushi Abdul'aziz ya ce, "Kai ko Malam ai ita baiwa daga Allah ta ke, kuma duk yadda ya baka ita bai kamata ka rainata ba, saboda haka ka zo ka zauna saman kujera duk mun zama daya". Nan dai ta kaddama ta kaure tsakaninsu. Da kyar Abdul'aziz ya shawo kan Malam Basiru sannan 37 Hikaya Hamsin Basiru Aliyu Harande ya zauna saman kujerar suka cika Malamai hamsin ke nan dai-dai. Lokacin da ya tsinci kansa cikin tsakiyar manyan marubutan duniya sai ya yi godiya ga Allah don acewarsa ko zama cikin su ma wani abin alfahari ne". Can kuma Gangaren waziri cikin murya mai karfi ya fara magana da cewa, "Ya ku al'ummar na ciki da wajen kasar, tare da manyan Malaman Hikaya, kuma alkalan wannan gasar, kamar yadda muka tsara dan dan Sarki na farko shi zai fito yanzu ya fara gabatar da nasa hikayoyin, wato babban saboda haka mun zabi Malam Abdulsalam ibini Bature da Abdul'aziz su kasance manyan Alkalan wannan gasar, in ya so M. Shehu ibini Muhammad da M. Mukhtar Al-Yaron Malam su kasance masu kula da maki, sauran Malamai kuwa su kasance masu naziri waziri Kwabis ya kara da cewa, "Da fatan kowa zai yi aikinsa bisa adalci ba tare da son zuciya ba, saboda haka Bakar ga mai fili ga mai doki. BAKAR ya taso cikin 'yan uwansa a natse yana tafiya cikin takama da izza fuskarsa cike da alamun samun nasara. Ganin cewa Malamin da ya koyar da shi wato M. Abdul'aziz Sani ya koyar da shi sosai, 38 Hikaya Hamsin Basiru Aliyu Harande kuma vashu yana bugun gaban shi nc babban dan Sarkı Da haka har ya iso saman mumbarin da aka tanada domin su, ya dubi karagar muikin kasarsu ya dan nisa ya luskanci jama'a wadanda tuni suz vi tsit! shi dai ake sauraro, ya yi gyaran murya ya ce, "Ni ne Bakar daya daga cikin 'ya'yan Sarki Gulam mai burin lashe wannan gasar, saboda haka kowa ya bani aron kunnensa zan fara daga cikin taskar Malamina". Ya fara bada labari da cewa. Kash! mai karatu sai sai a kara hakuri dani, ku nemi littafi na uku domin jin yadda za ta kasance. Shin waziri Kwabis zai samu damar cimma burinsa kuwa na rashin son Affan ya hau karagar mulki? Ku biyoni a HIKAYA HAMSIN kashi na uku. Daga mai kaunarku. BASIRU ALIYU HARANDЕ (Zuru) 07087325348-08163531398. 1 39 ود Rikaya Hamsin DANDANO Basiru Aliyu Harande Har ya juya da niyar wucewa sai ya yı ta riko masa riga ta baya sai ya tsaya. Cikin wata siriryar murya ta fara magana da ccwa, "Haba Samir ina so ka san cewa tun lokacin da na fada ma sirrin zuciyata ka barni cikin wani mawuyacin hali na zullumi saboda rashin amsa min bukatata...." Cikin sauri ya juya ya katseta da cewa, "Don Allah ki yi hakuri ki kyaleni banda lokacin soyayya yanzu, ki barni da irin masifar da mahaifinki ke son jefa rayuwata ita ta isheni. Daga littafin mai suna (MAKOMАTА) BASIRU ALIYU HARANDE ZURU. SANARWA! SANARWA!! SANARWA!!! Shahararren matashi mawakin Hausan nan wato Ibrahim O.C. Sokoto na farin cikin sanar da ma'abota sauraren wakokin Hausa sabon Album dinsa na gab da fitowa, wanda yake dauke da dadaden, zakakan wakokin tsantsagwaron soyayya da sanyaya zukata da sanya shauki ga ma'abota soyayya. Akwai wakokin fadakarwa, ilimintarwa da nishadantarwa, ma za ka nemeshi a kasuwa don wanke kwarkwatar kunnenka. Sunansa 'LAUNIN SOYYAYA ALBUM'.Daga, Ibrahim O/C Sokoto. finaioianint icrorit! 40 AKARA CITY BOOKSHOP LITTATTAFAN MARUBUCIN HIKAYA HAMSIN RUNDUNAR DAUKAR FANSA FARMAKIN ABOKAN GABA KOGON HALAKA ABDULSALAM ADAM SHITU (BATURE) G/KAYA ABDULSALAM ADAM SHITO (BATURE) G/KAYA A.A. BATURE PUBLISHERS An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it

Chapter 2 of 3