Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 3
gabansa. A daren ranar da za su yi tafiyar ne, Waziri ya kira su Bakar su goma. Bayan sun gaisa ne sai Waziris ya dubesu ya ce, "Ku yi sani cewa ba komai ne ya sa na taraku nan ba sai don in taimaka muku akan wannan tafiya da za ku yi gobe. Taimakon kuwa shi ne, ina so ne in turaku wajen wasu manya-manyan Malaman hikaya wadanda duniya ta yarda da kwarewarsu a sha'anin sanin hikayoyi. Ina mai tabbatar muku da cewa idan kuka sadu da wadannan Malaman hikaya zaku buge kowa a wannan gasa. Abin da yasa na ce muku haka, na san duk wanda ya lashe gasar daga cikinku wani ba zai yi bakin ciki ba". Suka amsa da cewa, "Haka ne". Waziri ya ci gaba da cewa, "Ku saurareni da kyau zan fara sanar da ku sunan malaman hikayoyin da inda za ku riskesu. Wadannan Malaman hikayoyin duk sun kasance mabiya addinin Musulunci, kuma' suna nahiyar Kasashen bakaken fata. Malami na farko wani fasihin Malami ne mai suna Abdullahi Ibni Mukhtar Al-Yaron Malam, wanda shi babban malami nc masanin hikaya wanda ya yi 23 Hikaya Hamsin Basiru Harande hikayar (Bajakadc). Ya kai Bakar wannan Malami shi na ke so kaje garcshi. Daga wannan nahaiya tamu zuwa nahiyarsu tafiya ce ta kwanaki ashirin ba cin zango. Dan haka sai ka bada himma za ka je ka samu abin da ka je bida ka dawo. Malami na biyu shi ne Abdul-aziz Ibni Sani AlMadaks wanda shi ma babban Malami ne wanda ya yi hikayar Kundin Tsatsuba. Zalum kai ne za ka je wurinsa. Daga nan zuwa kasarsu tafiya ce ta kwana bakwai. Sai malami na uku shi ne Rabi'u ibn Abukakar Al-Sharfadi, wanda hikayoyinsa sun shahara a duniya, cikinsu kuwa har da Hikayar Fairuzasshaha. Ina tabbatar maka da cewa ko wannan hikaya ka koya ta isa ta sa ka lashe wannan gasar. Da'uf kaine wanda za ka je gareshi. Sai Malami na hudu, wani babban Malami ne masanin hikaya mai suna Mukhtar Ibni Isah Al-Kwalisa, wanda wanda ya yi hikayar Gimbiya Zahrà. Itama wannan hikayar ta shahara sosai a duniya. Shafir kai za ka je wurinsa. Malami na biyar shi ne Shehu ibni Usman ibni Muhammad, wanda ya yi hikayar Mazan Fama. Shima masani ne sosai. Hamzi kaine wanda za ka ziyarceshi. Malami na shida shi ne Mubarak Ibni Hamza Al-Gadon Kaya wanda ya yi hikayar Jihadi, shia babban mai ilimi ne. Sagar kai ne za ka je wurinsa. Malami na bakwai kuwa shi ne Abubakar Ibni Tanko Al-lliyas, wanda ya yi hikayar 24 Hikaya Hamsin Basiru Harande Bautar Bayi. Shiam masanin hikaya ne. Samar kaine za ka je wajensa. Malami na takwas shi ne Umar Ibni Lawan Al-Abdul wanda ya yi hikayar Jarmai Sha Yaki. Shima masani ne sosai. Masul kai za ka je wurinsa. Malami na tara shia ne Hassan Ibni Shu'aibu Al-Harande, wanda ya yi wata kasaitacciyar hikiya, wadda ake kira Dan Sarauta. Shima babban masani ne. Gubur kai ne za ka je wurinsa. Malami na cikon goman shi ne Abdul-Salam ibni Shitu Al-Bature, wanda ya yi hikayar Gawurta, shima duniya ta sanshi. Sakar kai nake so kaje wurinsa". Waziri ya kare da cewa, "Na rantse da wuta da zarar kuka isa wurin wadannan manyan masana hikayoyin na duniya ba shakka sai daya daga cikinku ya lashe wannan gasar. Sabo da haka daga yanzu na gama daku, kowa tasa ta fishsheshi". Suka yi godiya kowa ya watse. A cikin daren ne kuma Waziri ya shiga laluben hanyar da zai bi ya cutattama Affan. Duk da ko ko bai san wurin Malamin da Affan din za shi ba. Bayan wani dogon tunani da Waziri ya yi sai kawai ya kyalkyale da wata irin dariyar mugunta, sabo da ya samu hanyar da zai kau da Affan cikin sauki. Nan da nan yasa aka yi masa kiran Affan. Bayan Affan ya shigo cikin turakar da yake zaunc ya gaishe shi, sai Waziri ya dubeshi ya ce, "Ya kai Affan na 25 Hikaya Hamsin Basiru Harande kiraka ne sabo da in taimakeka akan wannan gasa ta HAKAYA HAMSIN, sabo da na ga duk cikinku ka fisu hankali da nutsuwa. Taimakon kuwa shi ne, zan turaka wurin wani Malami masanin hikayoyi. Wannan malami sunansa Basiru Ibni Aliyu Al-Harande. Kuma yana Zaune ne a nahiyar kasashen bakaken fata ma'abota addinin Musulunci a wani birni mai suna Zururi. Daga nan zuwa birnin tafiyar kwanaki goma ce. Ba shakka idan kaje wurinsa zai koyar da kai dadadan hikayoyi wadanda za su kai ka ga lashe wannan gasa. Amma ina so wannan magana da mukai tsakanin ni da kai ta zamo sirri kada ka sanar da wani a cikin 'yan uwanka har ya rigaka zuwa wajen wannan masanin hikayoyi ya lashe gasar". Koda Affan yaji haka sai mamaki ya kamashi sabo da ya san dai Waziri ba kaunarsa yake ba, amma kuma sai ya yi tunanin ko Waziri ya canja halinsa ne. Cikin murmushi Affan ya yi godiya, sannan ya cc, "Na yi alkawari ba zan afdawa kaowa ba. Kuma komai wuya zan je birnin Zururi dan saduwa da wannan ma'abocin hikayoyi." Daga nan Affan ya mike ya shige cikin gida. Affan na shigewa Waziri Kwabis ya rinka kyalkyala wata irin dariyar mugunta, sabo da ya san ya tura Affan wurin Malamin da bai da wata kwarcwa ta fuskar sanin hikayoyi. Kuma ya san ba abin da zai iya 26 Hikaya Hamsin Basiru Harande koyawa Affan sai shirme kawai, sabo da ko shi bai kware ba barc ya koyar da wani. Kai hasalima bai taba rubuta wata shahararriyar hikaya ba bare duniya ta sanshi. Wannan shai ne yasa. Waziri ya yi ta. murna don yana tunanin ya gama da A ffan. Gari na waycwa Affan ya gama shirinsa tsaf yaje ya sallami mahaifiyarsa Zawira, tayi mai fatan samun nasara. Yana fitowa ya kama dokinsa ya hau ya yi masa kaimi ya bi sahun 'yan uwansa wadanda tuni wasu sun yi nisa a daji. Haka yarima Affan ya yi ta tafiya cikin daji yana keta kwazazzabai, koramu da duhuwowi. Kai akan sauri ko zango bai tsayawa ci. Bai gushe ba yana wannan tafiyar ba sai da ya kwashe kwanaki goma cіcif, kuma bai hadu da wani abin tsoro ba. A rana ta goma ne yana cikin tafiya saiai ya hango wata irin ganuwa mai tsananin tsawo. Nan da nan Affan ya yi wa dokinsa kaimi domin cimma ganuwar. Yana isa kofar ganuwar sai ya ga an rubuta 'BIRNIN ZURURI' cikin manyan harrufa. Wannan ne yasa Affan ya gano cewa ya iso birnin da malamin da zai sanar da shi hikayoyi yakc. Murna ta kamashi sabo da ganin ya kusa cimma burinsa. Lokacin da Affan ya shiga cikin kasar Zururi sai ya kasancc cikin mamakin ganin garin yadda bai zata 27 Hikaya Hamsin Basiru Harande ba, ya ga manyan ginc-ginc kawatattu, ga yawan al'umma, ga ya komi na garin cikin tsari yake. Haka dai ya ci gaba da mamakin ganin birnin Zururu kamar an tsaga kara da birninsu na Mahbub. Su kuwa jama'ar birnin duk inda Affan ya bi sai kallonsa kawai suke sabo da basu taba ganin kyakkyawan balaraben mutum kamarsa ba. Musamman ma matan birnin, wadanda sun fi sa masa ido. Koda Affan ya ga rana ta tassama yamma, sai ya fara tambayar mutanen birnin gidan Malam Basiru Ibni Aliyu Al-Harande. Amma duk wanda ya tambaya sai ya ce bai sanshi ba. Saboda dama ba wani sannane bane. Haka dai ya yi ta tambaya wuri-wuri, sai da ya tambayi sama da wuri ashirin amma bai dace ba. Haka ya yi ta aywo cikin garin har ya tsige boni. A cikin yawonsa ne yabi wata hanya inda ya iske cincirindon mutane sun yi da'ira suna shewa, da gani kasan wani abu suke kallo. Nan da nan Affan ya doshi wurin domin ganin irin wainar da ake toyawa. Yana isa sai ya ga wasu mutane ne daddaure cikin śarkoki gabansu kuwa wani basamuden kato ne rike da takobi tsirara, gefensu kuwa wani mutum ne cikin kayan Sarki. Da ganinsa ka san yana da mutunci a garin. Mutumin ya fara magana cikin kakkarfar murya 28 Hikaya Hamsin Basiru Harande da cewa, "Ya ku mutanen birnin Zururi, kuyi sani cewa wadannan mutanc sun kasance daga cikin masoyan mai girma gimbiya Shahriya, kuma suna daga cikin wadanda suka shiga gasar neman aurenta." Mutumin ya ci gaba da cewa, "Dama kun san cewa duk wanda ya shiga wannan gasar an bashi sharadin cewa idan bai ci gasar ba za a kashe shi? Sabo da haka wadannan mutane ba su yi nasara ba, kuma shi yasa gimbiya ta bamu damar kashesu. Kuma yanzu zamu kashe su domin cika umarninta." Mutumin na kawowa nan a zancensa sai ya bawa Hauni umarni ya cika aikinsa. Haunin ya gabata garesu ya daga takobinsa ya sare kan dayan. Koda dayan ya ga haka sai hankalinsa ya tashi ya rika kuka yana kucce-kucce. Da yake Affan ya kasance mutum ne mai tausayi sai abin ya bata masa rai, har ya kai shi ga zubda kwalla. Lokacin da Affana ya ga hauni ya daga takobinsa zai sake sare kan na biyun, sai ya ga ba zai iya bari ayi hakan ba sabo da tausayi. Cikin tsananin zafin nama ya baiyana a gaban haunin ya tunkudeshi. Hakan yasa saran da haunin ya kawo ya sari iska. Wannan lamari ba karamin mamaki ya baiwa duk ilahirin mutanen da ke wajen ba, saboda tun da suke ba a taba zuwa kashe wani ba wani yazi ya kareshi sai 29 yau. Hikaya Hamsin, Basiru Harande Cikin fushi mutumin da ya sa hauni aikinsa mai suna Raizu ya ce, "Ya kai wannan bakon saurayi shin kai wane daga cikin tsageran duniya da za ka hanamu cika umarnin shugabarmu? Ko kana son fushinta ya tabbata a kanka?" Koda Affan yaji haka sai ya ce. "Ni bako ne, kuma ba wai na hanaku cika umarnin shugabarku bane, sai dai tausayin wannan mutumin da ake shirin kashewa ne ya kamani, wannan yasa na ga zan iya sadaukar da rayuwata domin in kubutar da tasa. Sabo da haka na umarceku da ku fada min gasar da ya gaza ci ni zanyi, idan na samu nasara sai ku sakeshi ya tafi, idan kuma ban samu ba sai ku zartar da hukuncin a kaina a madadinsa". Koda Raizu yaji haka sai ya yi murmushi ya ce, "Ya kai wannan bakon saurayi ma'abocin shisshigi, shawarar da zan baka ita ce kada ka sa kanka a cikin wannan lamari, domin ba shakka ba za ka ci nasara akan gasar ba, sabo da haka ka kubutar da wannan kyakkyawar halitta taka kayi tafiyarka". "Koda Affau yaji haka sai ya ce, "Kayi sani cewa ni na sa kaina a wannan lamari, saboda haka na umarceka da kaje ka shaidawa Sarkinku ko ita gimbiyar, idan sun amince zan yi komai rintsi da tsanani". 30 Hikaya Hamsin Basiru Harande Koda Raizu yaji haka sai ya ce, "To shi ke nan, wanda baiji bari ba zai ji hoho! Abind a nake so da kai shi ne, kazo muje wurin Sarki kayi bayani da kanka". Lokacin da Raizu ya kai Affan wurin Sarkinsu mai suna Fakihu sai ya kwashe labarin duk yadda suka yi da shi ya sanar da Sarkin. Koda Sarkin yaji haka zai ya yiwa yarima Affan duban nutsuwa, ya ce, "Ya kai wannan bakon Sadauki, kayi sani cewa masu hasashe sun tabbatar da cewa duk fadin duniya ba mace mai kyau da cikar zati kamar 'yata gimbiya Shahriya. Wannan ne yasa masoya suka yi ma ta ca. Koda na ga haka sai na bukaceta da ta fitar da wanda take so domin in yi ma ta aure, amma sai ta ce ba wanda take so sai wanda ya shiga rijiyar da ke tsakiyar garinnan ya kashe wani tsohon kwado wanda ke hana mutane dcibar ruwan cikin rijiyar sai sati-sati kawai. Kuma shi wannan kwado ya dade a cikin rijiyar, kuma ya hallaka manyan bokaye da manyan Sadauki sama da dari-dari". Sarki Fakihu ya ci gaba da cewa, "Lokacin da gimbiya tayi wannan shawarar sai wasu daga cikin masoyanta suka ce ba za su iya ba, sun janye, wasu kuwa suka ce sunji sun gani. Koda taga haka sai ta се, "Duk wanda ya shiga rijiyar yaji tsoro ya fito ba shakka za a kashe shi". Suka ce "Sun amince". Sarki ya kare da cewa, "Wannan yaron da ka gani yana daya daga cikin wadanda suka shiga rijiyar suka ji tsoro 31 Hikaya Hamsin Basiru Harande suka fito, shi yasa abasu halaka ba. Amma sauran da suka shiga duk sun halaka. Kaji wannan shi ne dalilin sanyawa a hallakasu". Koda Sarki ya kawo dai-dai nan a zancensa sai abin Affan ya ce, "To idan kun amince ni zan shiga rijiyar in kashe kwadon sai aba wannan Sadaukin auren gimbiya. Idan kwadon ya hallakani kuwa shi ke nan na fanshi jininsa". Koda Sarki yaji haka sai ya yi murmushi ya ce, "Ya kai wannan sadauki kar ka jefa wannan kyakkyawar siffa taka cikin bala'i, gwara kayi tafiyarka, ko ka more kyawunka". Affan ya ce, "Shi yaji ya gani". Koda Sarki ya ga alamar bashi da niyyar bari sai ya ce, "To yanzu ka ga rana tana gab da faduwa, sabo da haka zamu baka wuri ka kwana gobe zamu kaika bakin rijiyar ka shiga. Amma idan ka tsorata ka fito ba shakka sai mun kasheka". Affan ya ce, "Na amince da hakan". Gari na wayewa Sarki yasa aka yi shela. Aiko nan da nan jama'a suka yi cincirindo a bakin rijiyar domin kaseh kwarkwatar ido. In kayi duba saman wani mumbari za ka ga Sarki Fakihu da sauran mukarrabansa zaune saman kujeru na kasaita. Gefensa kuwa gimbiya Shahriya ce zaune saman kujera cikin wata shiga irin ta kasaita sai sheki take tamkar rana ya 32 Hikaya Hamsin Basiru Harande yin da tayi tsaka. A gaskiya hankali, tunani, nutsuwa ba za su iya misalta irin tsabagen kyau da cikar zatin da Allah ya yi ma ta ba, sabo da duk da namijin da ya yi arba da fuskarta ba zai sake son kallon wata 'ya mace ba a duniya. Raizu ne ya mike ya fara magana da cewa, "Ya ku jama'ar kasar Zururi da yake dai kowa ya riga ya san abin da ya sake taramu bakin wannan rijiyar.. Ba tare da 6ata lokaci ba muna bukatar wannan bakon Sadaukin ya fito domin cika alkawarinsa na shiga,wannan rijiyar". Koda Jama'a suka ji haka sai kow aya nutsu yana sauraren fitowarsa. Ana cikin haka ne sai gashi ya faso taro ya fito, ya tsaya bakin rijiyar. Tsananin kayu da kwarjininsa tare da cikar zatinsa yasa duk jama'a suka yi shiru suna kallonsa, daga shi sai dogon wanda na fatar damisa, ga alamubn karfi na baiyane a jikinsa. Hannunsa rike yake da takobi tsiraraa kugunsa kuwa akwai igiya ta kai kamu dari. Sadauki Affan ya fara magana da cewa, "Ya mutanen kasar Zururi kuyi sani cewa ni bako ne, kuma na shiga wannan gasa ne ba don ina daga cikin masu neman auren gimbiya ba, a'a sai don in ceci!rayuwar wani wanda tausayinsa ya kamani, sannan idan na ci nasara ba shakka gimbiya za ta zama mallakin wannan jarumi da zan canja". 33 Hikaya Hamsin Basiru Harande Ita ko gimbiya Shahriya tunda ta kyalla ido ta ga Sadauki Affan sai tsananin kyau da kwarjininsa suka daki zuciyarta, ta kura mai ido zuciyarta ta rinka bugawa: Nan da nan ta fara maganar zuci da cewa, "Ashe a duniya akwai da namiji mai kyau kamar wannan? Amma da na sani da ban ce sai an yi gasar neman aurena ba, da sai dai in shiga gasar neman wannan sadaukin ya aureni". Tana cikin haka ne sai ta ga Sadauki Affan ya yi alkafura ya fada cikin rijiyar. Hankalinta ya tashi, ta shiga wasi-wasin ko zai fito ko zai halaka a ciki? Amma ta san idan matukar ya hallaka a ciki ba shakka itama za ta hallaka, saboda tuni kaunarsa ta raunata zuciyarta, kuma ta yanke cewa ko bai ci wannan gasar ba shi za ta aura. Jarumi Kasim shi ne wanda Affan ke wannan fafafutuka sabo da kubutar da rayuwarsa. Shima haka ya kasance cikin wannan wasi-wasi ko Affan zai samu nasara ko zai ji tsoro ya fito a kashesu gaba daya, sabo da ya san bala'in da ke rijiyar. Bayan sa'a biyu da shigar Affan rijiyar sai aka rinka jin wani irin gurnani, ruwan rijiyar suka rika hautsinawa. Ana cikin haka ne sai kasar wurin ta fara girgiza tamkar za ta tsage. Hankalin jama'a ya dugunzuma, musamman gimbiya Shahriya wadda tuni ta fara kukan 34 Hikaya Hamsin Basiru Harande zuci sabo da rashin sanin halin da masoyinta ke ciki. Ana cikin haka ne sai aka ga ruwan cikin rijiyar ya yo tsiri zuwa wajen rijiyar samansa jini ne a malale tare da wani 6angare na jikin dogon wandon da ke jikin Affan. Hakan shi ya dugunzuma hankalin jama'ar gari, kowa jikinsa ya yi sanyi. Gimbiya Shahriya ta rintse ido tare da kwalla kara tayi kasa ta fadi sumammiya domin ta baiwa kanta tabbacin tabbas wannan bakon saurayi da ta kamu da kaunarsa ya hallaka. Jikin dubban jama'ar da ke wajen gaba daya ya yi sanyi. Nima ajiye birona nayi ina jimamin faruwar wannan lamari. INA LABARIN 'YAN UWAN YARIMА AFFAN WADANDA SUKA NUFI SHAHARARRUN MALAMAI MASANA HIKAYOYI? A CIKINSU WAYE ZAI SAMU NASARAR ZAMA SARKIN BIRNIN MAHBUB? A WANNE HALI ZAWIRA MAHAIFIYAR AFFAN DA KISHIYOYINTA KE CIKІ? SHIN AFFAN YA HALLAKA NE KO KUWA YANA RAYE? YA YA RAYUWAR GIMBIYA SHAHRIYA ZA TA KASANCE TUN DA BAKON SAURAYIN DA TA KAMU DÅ KAUNARSA YA HALLAKAА 35 Hikaya Hamsin CIKIN RIJIYA? Basiru Harande Ba a shiga komai a cikin labarin ba, yanzu aka fara. Mu hadu a littafin HIKAYA HAMSIN kashi na biyu dan jin ci gaban wannan kayataccen labari. Mai debe muku kewa, da fatan nishadantar da ku, BASIRU ALIYU HARANDE (ZURU) 08087325348-07066006764. Don Allah ina neman shawarwarinku ko gyarrarrakinku akan wannan littafi, dan adam ne ni ajizi ba abin mamaki bane aga tarin kura-kurai. Littattafan Marubucin: Hikaya Hamsin Bakar Damara Rundunar Daukar Fansa Makomata Harbin zuma Hucin zuciya Kulli Duk daga taskar, BASHIR ALIYU HARANDE ZURU 36 Hikaya Hamsin Basiru Harande Albishirinku Makaranta littattafan Yaki? Ku ce min goro. G awurtaccen shahararren matashin marubucin nan, wanda tauraruwarsa ta fara haske a sararin samaniya, marubucin Azabtarwa, Gasar Ajali, Izaya, Gawurta, Fargabar Bayi, ya kara gwangwajewa, ya baje basirarsa, ya tsara ya shirya, ya rubuta kasaitaccen littafi daya tamkar da dubu, mai suna 'HALAKA! HALAKA!! HALAKA!!!" Labari ne kasaitacce kayatacce, wanda ya zamo bakandamiya a cikin littattafan yaki da suka taba wanzuwa a duniya. Babban abin farin ciki kuma shi ne, wannan littafi babba ne, ma'ana mai yawan shafuka. Káma guda daya-ne jal. Haka zalika akwai babbar garabasa a cikin littafin, ma'ana akwai gagarumar Gasa da aka sanya a cikin littafi domin auna fahimtar makaranta. Littafin Halaka, littafi ne mai dauke da labari mai tsananin kayatarwa, kama daga jarumtaka, soyayya, tsafi, al'ajab da kuma rikitarwa. Abdul-Salam 'Adam Shitu Bature G/Kaya, ba baya bane wajen tsara kayattattun labari ga duk wani ma'abocin karanta littafi ya san yanda yake tsara littafansa cikin tsari da salo mai Kayatarwa. Dole a jinjinawa wannan matshin hazikin fasihin marubuci bisa yanda ya baje hikimarsa ya rubuta wannan littafi, kuma ya kayata aikinsa da aikin mai kyau, kama daga kayataccen bango mai santsi, da hoto mai matukar kyau, farar takarda karanta ka barwa jikokinka tare da tsararrren rubutu kamar a Ingila. Kai dai nemi wannan littafi da zarar va fito. Tuna da sunansa, "Halaka! Halaka!! Halaka!!!" Yana nan tafe! 37 Hikaya Hamsin Basiru Harande KARANTA WANNAN K oda Gimbiya Umla taji haka sai ta dubi Sarki ta се, "Ya kai Abbana shin ka manta da alkawarin da na daukarwa kaina cewa ba zan taba son wani da namiji ba bare har in aurcshi? Kai! ni ina ganin ma So karya ne! In ko ba karya bane me yasa har yanzu ban ji son wani da namiji ya shigeni ba? Sabo da haka ya Abbana ina so duk wanda ya kara cewa yana sona kasa a kamashi a kulleshi a cikin kurkukun duhu ayi ta gana masa nau'ikan azabobi har kala dari tara da casa'in da tara, har sai ya mutu sabo da tsananin ukuba. Matukar ka yi hakan na tabbata kai mai kaunata ne, idan kuwa ba ka aikata hakan ba lallai kai makiyi ne a gareni. Kuma na rantse da darajar karagar mulkinka sai na kashe kaina!!". Koda Sarki yaji haka sai ya yi murmushi ya ce, "Ya ke 'yata, ba wai na mance da wannan alkawari da kika ďaukarwa kanki bane, sai dai ina ganin har yanzu kuruciya na cinki. Kuma ita kalmar "So" da kika ji ana ambata har kike karyatata, wata shu'umar kalmace mai shammatar zuciya, wadda babu wata halitta da ke rayc a ban kasa da zai ce ya san lokacin da take shammatarsa ta shigeshi ba. Ina tabbatar miki da cewa matukar baki bi a sannu ba, kin hanu ga aibata kalmar So da karyatata, sai kin tsinto zuciyarki a cikin kuncin matsanaiciyar soyayya mai wajigarwa....Ki tsinto kanki a cikin yanayin kaskantar da kai ga wanda kika kamu da soyayyarsa, ya yin da shi kuma zai nuna halin ko-in-kula a garcki....Lallai zuciyarki za ta yi soyayyar da ba a taba yin irinta ba a tarihin duniya..." Wannan kadan ke nan daga cikin littafin RUNDUNAR DAUKAR FANSA, wanda ke tafe nan ba da jimawa ba. Daga Taskar, Basiru Aliyu Harande. 38 bnsa6H inias8 Hikaya Hamsin nlzmeH Gужн Baslru Harande TRY ABANIEW E ab B 18W srinis gts 7628M adabbs ab sinc sy sanads IS Kadan daga littafin Kwan Sihiri ATEW E 8182 em my t СTES PIaloQ Labari ne akan wata yar Sarki, Ita wannan "yar Sarki kyakkyawa ce ta gaban kwatance, domin har wasu na ganim ccwa ba mutum bace aljana ce ke siffantuwa da siffar mutane, sabo da tsananin tsabagen tsubin kyawunta. Kyawu ne da idanuwa basu taba ganin koda kwatankwacinsa ba. Kyawu ne da ke saurin fuskar zukata izuwa ga shagaltuwa da kaunar ma'abociyar kyawun. Hakan yasa labarin kyanta ya watsu a lardinan duniya. Fatake suka rinka yadashi ga manyan dauloli da manyan Sarakuna da Attajirai, bokaye suka ringa kwadaitawa 'ya'yansu da 'ya'yayen isassun Sarakuna. Sai dai kash! Duk da tsananin wannan kyawu na ban mamaki da wannan 'yar Sarki ke da shi, tana da wata lalura mai abin mamaki, lalurar da manyan bokaye da masana magunguna suka gaza gano takamaimai wacce irin cuta ce. Ta kai cewa wannan 'yar Sarki ko kofar dakinta bata iya zuwa sabo da tsananin lalurar, An yi magani da tsatsube-tsatsuben, amma abin ya ci tura. Ana cikin wannan yanayi ne wani ani shahararren boka ya baiyana daga wata nahiya daga cikin nahiyoyn da suke wanze a duniya da labarin hanyar da za a bi a samu maganin da zai warkar da wannan lalura ta wannan kyakkyawar 'yar Sarki. Hanyar kuwa ita ce, sai an je wani kungurmin bakin daji mai dauke da miyagun hadarurruka, an dauko wani katafaren Kwai wanda ake kiransa da suna 'KWAN SIHIRI'. Wannan KWAN SIHIRI yana bangon duniya barin yamma karkashin tsaron wadansu miyagun maridan aljanu wadanda tsafi da kaifi baya tasiri a kansu. Ba su san komai ba 39 Hikaya Hamsin Basiru Harande face hallakar da bakuwar halittar da ta ziyarci nahiyar da suke. Matukar aka samo wannan Kwai aka dafawa wannan 'yar Sarki ta ci za ta warke daga wannan muguwar cuta da ke addabar rayuwarta". Ya yin da mahaifinta yaji wannan batu sai hankalinsa ya dugunzuma, har sai da ya zubar da hawaye, domin yana ganin cewa babu wata halitta da za ta iya dauko wannan kwai. Yana cikin halin tsananin bakin ciki wannan boka da ya kawo labarin Kwan ya shawarceshi da cewa ya tura sadaukan kasarsa ya turasu dauko wannan Kwai, idan aka taki sa'a sai wani daga cikinsu ya SAI nasara. Nan take ya tarasu ya sanar da su bukatarsa, tare da yi musu alkawarin duk wanda ya dauko wannan kwan sihiri za a aura masa wanann 'yar Sarki tare da raba kasarsa biyu ya bashi rabi ya mulka. Runduna guda ce tayi gagarumin shiri ta nufi bangon duniya dauko wannan kwai. Gaba dayansu sun rasa rayukansu, da kyar da sidin goshi wani matashin jarumi mai karancin shekaru ya sau pasarar dauko wannan kwai bayan ya rasa raytuwarsa, ya samu nasarar tsira da miyagun raunika. Ya yin da ya kawo wannan Kwai aka dafawa wannan 'yar Sarki ta ci, sai ta mike tamkar ma bata taba yin wata lalura ba. Wani babban abin aľajabi shi ne, irin tsananin kiyayyar da wannan 'yar Sarki ta nuna ga wannan jarumi da ya sai da rayuwarsa ya dauko wannan Kwai.... Dan jin yadda za ta kasance, nemi wannan Kayataccen littafi mai suna 'KWAN SIHIRI da yake gab da fitowa. Yana dauke da labari mai tsananin nishadantarwa da ban al'ajabi. Daga, Hassan Shu'afbu Harande. 40 AKARA CITY BOOKSHOP LITTATTAFAN MARUBUCIN HIKAYA HAMSIN RUNDUNAR DAUKAR FANSA FARMAKIN ABOKAN GABА KOGON HALAКА ABDULSALAM ADAM SHI (BATURE) G/KAYA A.A. ABDULSALAM ADAM SHITU (BATURE) G/KAYA BATURE PUBLISHERS G/KAYA KANO 07041591141 08162707231, 08124173211 Cover illustration: Anka-Graphics Fagge. 07030319787 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking

Chapter 2 of 3