Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 3
ya cije, yaki ya jawo shi kuwa Sadauki sai kokarin janshi yake a cikin wannan lokaci ne aka ga jikin Sarki ya saki nan take ya fara yin amai, aikuwa nan Sarki Yaki Safwan da kuma Yarima Yazid suka kamo da tsananin firgici har ya zama sun yi rige rigen tasowa amma Sarki na ankarewa da su sai ya daka musu tsawa da su dakata, shi kuwa wannan Sadaukin 55 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI koda ya jawo Sarki Gaban Sarakan Sai ya cire wani katon gatare daga jikinsa ya daga shi zai sare kan Sarki, har idanuwan jama'a ya rufewa kawai sai gani akai Yarima Yażid ya taho cikin iska ya doki wannan Sadauki ya fadi kaka ya fada kan gatarin ya cire masa makogaro cikin sauri ya dauke Mahaifinsa da yake ta faman a man jini ya kaishi sansaninsu. Kafin ya dawo filin dagar kuma sai suka ji wani irin nishi mai karfi ya karade filin gurin baki daya, wannan al'amari sai ya dugunzuma hankalin duka jama'ar da suke wannan gun, suka saka idanuwan sosai. Aikuwa kafin kiftawar idanuwa Sai ga Macijiya Burukul Kursum ta bayyna cikin tsananin tashin hankali. A nan take Yarima Zaiyan ya dakata da yunkurinsa domin daga zuwanta har ta yabcari kadan daga cikin al'ummarsu ta yi musu loma daya. 56 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI Daga Abdul aziz sani madakin gini mai debe muku kewa akowane lokaci sai mun hadu a cikin littafi na biyar dan jin ci gaban wannan labari na TURBAR GASKIYА SHIN SARKI ABU ZAIYAN ZAI SAMU LAFIYA? WAYE ZAI KARASA KARAWA DA WADANNAN ADAWAN DA SU SARKI HUSAKA SUKA ZO DA SU? SU WAYE ZA SU NASARA A CIKIN WANNAN GAWURTACCEN YAKI A TSAKANIN RUNDUNAR MUSULUNCIN DA KUMA RUNDUNAR KAFURCI? YA YA ZA AKWASHE DA MACIJIYA BURUKUL KURSUM A CIKIN WANNAN HALI. A TSAKANIN SHADILAT DA GIMBIYA LUMSHAIRA WACECE TAFI KAUNAR YARIMA YAZID.? 57 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI WANE NAMJIN КОKARI GIMBIYA LUSHMAIRA ZA TA YI HAR TA ZAMO YARIMA YAZID ZAI AMINTA DA JARUMTAKARTА. Sai mun hadu a littafi na biyu 58 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI TALLLA! TALLA!! TALLA!!! A wani zamani can baya mai tsawo da ya shude bayan shudewar mulkin fir'auna na birnin misra an yi wata azzalumar sarauniya mai suna Zuhaira bin Masrud. Sarauniya zahuira tana mulkin wata babbar kasa ce dake bakin gabar tekun bahar sufiya kuma ta gaji sarautar ne a wajen mahaifinta sarki masrud bin Zaurid Sarki masrud ya kasance gawurtaccen mayaki wanda yai shuhura zamaninsa kuma shi a rayuwarsa babu abinda ya tsana sama da ma'abota addinin musulunci ba komai ne ya haddasa mummunar gaba tsakaninsa da ma'abota addinin musulunci ba face akwai watarana da wadansu fatake ma'abota addinin musulunci da suka zo giftawa ta birninsa, sai suka yada zango a gefen garin domin su yada zango. A wannan lokaci akwai wani takadirin aljani a cikin birni na Sufras wanda muatena ke 59 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI bautawa a matsayin ubangijinsu. A kullum sai an yankawa wannan aljani raguna uku, shanu, uku da rakuma uku, kuma Sarki masrud ne da kansa yake jagorantar wannan hadaya da ake yiwa aljanin mai suna burrata. A ranar da wadannan fatake suka ya da zango a bakin birnin Sufaras ne wata annoba ta zo birnin ya zamana cewa gaba daya dabbobin garin da tsuntsayensu sun kamu da wata irin cuta ta gudawa don haka sai suka rinka mutuwa wasu kuma suka lafke ya zamana cewa ko ta shi basa iya yi. Bisa ka'idar hadayar da ake yiwa aljani burrata ana yanka masa lafiyayyun dabbobi ida kuwa aka kuskura aka yanka masa mara lafiya koda guda daya ne kacal a ranar babu wanda ya isa ya yi barci a garin kuma duk kanannan yar dake garin sai sun kamu da cutar da zasu yi ta mutuwa haka kuma idan aka saba lokaci na yin wannan hadaya to fa sai wannan bala'i ya afko. Sarki marud. yana samun dukkan biyan bukatarsa a wajen aljani Burrata bisa wannan dalili ne baya yarda a sami matsala a ko kadan akan yi masa hadaya. 60 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI Lokacin da ake yin wannan hadaiya ga aljani Burrata da yammaci ne sakaliya daf da magruba tun da rana wannan annoba ta afku a cikin birnin na Sufras al'amarin da ya dugunzuma hankalin Sarki masrud ke nan ya baza dakarunsa ko ina a cikin birane da kauyuka na kusa a kan a nemo lafiyayyun dabbobin da za'a yankawa aljani Burruta kafin rana ta fadi. Ai kuwa har gefen la'asar ba'a sama dabbobinba sai ga Dakarun da aka tura sun dawo cikin gigita da dimauta, shugabansu ya zube kasa a gaban Sarki masrud ya ce, Ya shugaba mun duba ko ina a cikin biranc da kauyuka dake kusa da wannan kasa tamu babu inda wannan annonba bata je ba, mun rasa lafiyayyun dabbobi amma akan hanyarmu ta dawowa mun ga wadansu bakin fatake kuma suna da dabbobi lafiyayyu fiye da adadin da muke bukata. Koda Sarki jin wannan batu sai farin ciki ya lullube Sarki Masrud ya ce, "Maza ku koma wajen wadannan fatake ku siyo daddbobin da muke bukata a wajensu komai tsadarsu kuwa, idan suka ki siyar muku ko kwato su da karfin tsiya ku zo mini da su, domin mu hanzarta zuwa 61 TURBAR GASKIYA --4 dakin bauta. _MADAKIN GINI Koda jin wannan batu sai Shugaban dakaru ya mike tsaye da sauri yana mai cewa an gama ya shugabana, nan take ya jagoranci dakarunsa kimanin su dari biyu suka hau dawakansu suka zaburesu da gudu izuwa gfen gari Su dai wadannan fatake da suka ya da zango a gefen birnin sufras gaba dayansu basu fi su ashirin ba kuma duk zur'a dayane na wani attajiri da ake kira Abu Salhaif. Acikin wannan Zuri'a akwai matarsa guda daya da kuma dansa shima guda daya jal wani matashin saurayii wanda baisfi shekara goma sha hudu ba, shi ake kira da suna Salhif, sauran mutane goma sha bakwan daga kannensa sai matansu, da 'yayansu. Abu Salhif na tsaye tare da dansa Salhif yana koya masa yadda ake yaki wato suna kaiwa junansu sara da suka cikin gwaninta a gefe daya kuma matarsa da sauran abokan tafiyar na tsaye suna kallonsu sai kawai suka hango kura daga can nesa ta turnuke sama, sannu a hankali suka hango dakaru bisa dawakai a sukwane sun 62 TURBAR GASKIYA --4 durfafosu. MADAKIN GINI A zaton su Abu Salhif yanfashi ne suka kawo musu hari, har mazajen cikinsu sun yunkura zasu zare makamansu su tari mahayan sai Abu Salhif ya daka musu tsawa, ya hana su, don haka sai kowa ya tsaya a inda yake har mahayan suka kara so daf da su suka yi turjiya suna sanye cikin kayan yakin dakarun birnin Sufras. Koda Abu Salhif da jama'arsa suka ga cewa ashe dakarun birnin Sufra ne sai hankalinsu ya kwanta suka mayar da takubbansu cikin kufe. Cikin biyayya Abu Salhif ya risina ga shugaban dakarun ya yi gaisuwa sannan ya се, "Ya ku Dakarun Sarki Masrud me kuke bukata daga garemu har da zaku kawo mana ziyarar bazato a irin wannan lokaci alhalin ko shigowa cikin birnin naku ba mu yi ba? Koda jin wannan tambaya sai Shugaban Dakarun ya sauko daga kan dokinsa ya matso daf da Abu Salhif ya ce, "Ya kai wannan attajiri tsohon abokin cini kinmu ka yi sani cewa Sarki ne ya tro mu gareku domin ku siyar mana da raguna uku, shanu uku rakuma daga cikin 63 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI dabbobinkudomin mu bayar da jinin su ga abin bautarmu gunku Burrata." Koda jin wannan ba tu sai hankalin Abu Salhif ya dugunzuma ya ce, "Subhanallahi ya kai wannan badakare ka yi sani cewa mu musulmai ne wadanda suka yi imani da bautar Allah Sarki guda daya wanda shi ne ya halicci komai da kowa har da shi gunkun da kuke bautawa, ta yaya zamu bayar da dabbobinmu kuje ku aikata wannan mummunan sabo da su, ai idan muka baku tamkar muma mun yi imani da abin da kuke bautawar ke nan, ku koma ku gayawa Sarki Marud cewa ni attajiri Abu Salhif nace ya yi hakuri ba zamu iya siyar masa da dabbobinmu a, koda jin wannan ba tu sai shugaban dakarun ya tari numfashin Abu Salhif yana mai daka masa tsawa ya ce, "Sarki ya bamu umarni idan har baza ku bamu wadannan dabobbi ba lallai mu karbe su da karfin tsiya koda jin haka sai Mazajen ayarin na Abu Salhif suka zare takubbansu da nufin su yaki dakrun Sarki Masrud, amma sai Abu salhif ya sake daka musu tsawa a karo na biyu ya ce, "Baku da hankali ne ta yaya zaku iya yakar dakarun kimanin dari 64 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI biyu alhalin gaba dayanmu bamu wuce mu goma sha ba." Nan take mazajen suka sake mayar da takubbansu cikin kufe suka koma bayan Abu Salhif suka tsaya a wannan lokacin ne bakin ciki ya lullube Salhif har zuciyarsa ta kama tafarfasa kamar zata kone jikinsa ya kama tsuma koda shugaban dakarun ya lura da halin da Salhif ke ciki sai ya bushe da dariya mugunta sannan ya dafa kafadar Salhif ya се. "Yaro ka yayyafawa zuciyarka uwan sanyi idan ba so kake yanzun nan jini zuri'arku gaba daya ya zube anan ba." Koda jin wannan ba tu sai Saihif ya sake fusata ya yunkura zai kaiwa badakaren Sara da takobin hannunsa amma sai Saihif ya yi wuf ya ruke hannunsa kuma ya zabga masa mari har ya fadi kasa, cikin tsananin mamaki Salhif ya shafe kuncinsa sa'adda hawaye ya zubo masa ya kurawa mahaifinnasa idanu saboda wannane karo na farko da ya taba marinsa amma ko bakar magana bai taba gaya masa ba, nan take Abu Salhif ya dubi Shugaban dakarun ya се. "Za mu baku dabbobin da kuke bukata 65 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI amma ka gayawa Sarki cewa bukatarku ba zata biya ba ta hanyar amfani da da dabbobin ma'abota addinin musulunci koda gama fadin hakan sai Abu Salhif yasa aka kwanto raguna uku shanu uku da rakuma uku aka baiwa dakarun suka tafi da su. Bayan tafiyars ue Abu Salhif ya mikawa Salhif hannunsa ya kama ya tashe shi tsaye sannan ya dube shi ya ce, "Ka yi hakuri ya kai dana inda ban mareka ba bisa kuskuren da ka aikata da tuni an kasheka a gaban idanuna kasani cewa kai ne ka dai a gareni ni da mahaifiyarka don haka ba ma son mu rasaka ku ta shi mu kimtsa mu bar garin nan domin abin da zai biyo baya ba mai kyau bane,." Koda jin haka sai kowa ya ta shi aka hau kimtswa nan da nan kowa aka gama shiri aka kama hanya domin ci gaba da tafiya izuwa birnin na gaba.inda za'a gudanar da harkokin fatauci. Al'amarin Sarki Masurd ana kai masa wadannan dabbobi sai yai shiri ya tafi izuwa dakin bauta aka yanka dabbobin aka bayar a jininsu ga aljani Burrrata kamar yada aka saba Faruwar hakan ke da wuya sai suka ji aljani Burrata ya kwarara uban ihu al'amarin da ya janyo 66 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI dakin bautar ya kama rugujewa, mutane dake ciki suka dimauce suka rinka zubewa kasa sumammu, Cikin firgici Sarki Masrud ya zube kasa gaban gunki Burrata yana tuba. Nan take gunki ya bude baki ya ce, "Maza ka tura dakaru su je su kashe wadannan bakin fatake domin jinin dabbobinsu bai magance mini kishirwata ba face Karuwata kuma ka sani cewa lallai sai an yi asarar dubban rayuwaka a cikin Kasarka saboda fishina idan baka hanzartaa samomin jinin da na saba sha ba ko wa sai ya dandana kudarsa." Koda jin wannan batu sai Sarki masrud ya sake dimaucewa ya mike tsaye zumbur yana mai kwalawa Sarkin yakinsa kira ya fice da gudu. Kadan ke nan daga cikin littafin JAHADI wanda zai zo nan bada jimawa ba. Naku har kullum Abdul'aziz sani madakin gini Dukkan mai son wannan labari da kuma sabon labarina WASIKAR JINI SAI KU SAME SHI A SABON BRANCH NA JAKRA CITY BOOK SHOP DAKE KASUWAR SABON GARI MARKET KUSA DA MADAKIN GINI BOOК SHOP ДБЕМ Sai mun ji daga gareku za a iya samunmu a wannan numer kamar haka 67 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI 08162707231-08069524699 TALLA! TALLA!! TALLA!!! SAKON MUTUWA A tsakar dajin mai yalwar korayen ganyayyaki suke tsaye su biyu a tsakiyar koraye ganyayyaki wasu jibgajibga aljanu suna tsaye a gefensu kowane su rike yake da jariri a hannunsa cikin tsananin farin ciki da ganin juna. Sarakuna ne masu ji da sarauta suturun dake jikinsu kawai zai tabbatar maka da haka kowane yana rike da jariri a hannunsa Sarki 2 Madhan shi ne Sarki kasar Arfat, sai Sarki Azkam shi ne Sarkin kasar Yuhud abokane ne su wadanda aka yi 68 L TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI shelar a duk duniya babu abokai masu kaunar juna da amincin sama da su, sannan babu wasu sarakai masu girman masarauta da tumbatsar arziki face su, kuma duk da sun kasance abokan gugayya a bangaren sarauta dukiya gami da jin kai, basu zame masu yiwa juna bakin ciki ba haka ma shi yafi musu dadi a rayuwa domin basa so ace a cikinsu wane yafi wani, sun fi son su zama suna tafiya daidai da juna. Abu guda ne ya banbanta wadannan Sarakai Sarki Madhan yana mutukar son ganin ya haifi 'ya mace ya yin shi kuma Sarki Azkam kuma ba shi da burin da ya wuce ace ya samu haihuwar da namiji, amma sai aka samu akasi a shekarar da matarsa zata haihu sai ta haifi 'ya mace shi kuma Sarki madhan sai matarshi ta haifi da namiji, wannan dalili ne yasa suka yi wa juna alkawarin musayar yaran ta yanda 69 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI babu wanda ya san da haka, face aljanunsu guda biyu kuma masa rike sirrikansu. Ranar daya lokaci guda aka samu wannan haihuwa a lokaci da matan suka haihu sai Sarki Madhan da Sari Azkam suka badawa matansu hodar banjo sukа kama barci ta wannan yasa suka saka aljanunsu suka kwashe su zuwa wannan daji. Koda Sarki madham da Sarki Azkam suka dubi juna sai farin ciki ya baibaye su, Sarki Madhan ya ce, "Ya kai Aminina hakika godiya ba zata kare ba bisa yanda muke mututta juna kuma muke daraja juna lallai daukakarmu da boyayaryamu ba zata taba rugujewa face an samu ranar da dayanmu zai ji bazai iya rufe sirrin dayanmu ba, dan haka ina mai horonka da ka yi yaki da zuciyarka wajen gujewa wannan, sannan ina mai kara jadda maka akan ka tsare wannan sirrin kamar yanda zaka tsare rayuwaka dana ya zamai naka 'yarka ta zama tawa, har abada 70 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI babu wata rana da zamu saka ido akan wani daukaka da zata biyo baya a lokacin da yaran nan suka girma, in har mun kawar da wannan to babu shakka amincinmu zai cika gaba da daurewa har abada." Koda Azkam ya ji wannan ba tu sai ya mika jaririyar dake hannunsa ga amininsa shi ma amininsa ya mika masa jaririn. Sannan Sarki Azkam ya ce, "Babu wata rana da zuciya ta isa ta kawo mana sukar junamu halas malak na bar maka wannan yarinya kamar yanda halas malak ka barmin wannan yaron, dan haka koda masifar wuta da ruwa zasu cudu a cikin kasata ya zamana bani da maganin wannan masifar face ďanka to ina mai tabbata ba zan taba bukatar shi daga gareka. Da jin haka sai Sarki Madhan ya yi murmushi ya rungume Sarki Azkam suna masu murmushi. Da haka kowannensu ya koma ya haye kan aljaninsa. Suka Bace daga cikin dajin cikin tsananin farin ciki da nishadi. 71 TURBAR GASKIYA --4 MADAKIN GINI n Tirka shi, kirarren labari ne da na ratattako muku shi mai suna SAKON MUTUWA yana nan tafe daga ni Abdulsalam Adam shitu bature gadon kaya D A 08162707231 Ni Abdulsalam ina kara yiwa makarantana tuni da fitowar littafin DAKARU KASHI NA HUDU SANNAN NA BIYAR SHI MA YA FITO TARE DA WANNAN LABARI IN BAKA SAMU GARAZAYA KA NEMI NAКА. MUNA KARIN SANAR DA SHAHARARREN MARUBUCIN YAKIN NAN MARUBUCIN GIMBIYA ZAHRA DA ADDININA WATO MUKTAR KWALISA YA ZO MUKU DA SABON LITTAFI MAI SUNA RANAR GAMO YANA NAN A KASUWA 72 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 3 of 3