Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 3
ko, kuma bana son dayarku ta yi min karya ku sanar da ni iyaka gaskiyarku. KodaShadilatda Gimbiya Lushmaira suka ji wannan batu daga Sarkin sai suka durkusa bisa gwiwoinsa sannan suka ce, "Ya shugabana muna rokanka alfarma a bisa kyata maka doka da muka yi ka yi sani ba mu yi haka dan komai ba sai dan mu je zuwa wannan filin daga domin idanuwanmu ya gane mana irin jarumtakar da Jarumi Zaiyan da 30 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI kuma kai zaku nuna, a wannan gurin. Koda Sarki ya ji su da wannan ba tu sai ransa ya yi mutukar faci ya dube su ya כ ce, "Amma dai kun cika sakarai a wanne dalili ne kuna mata ma'abota rauni zaku biyo sawunmu zuwa wannan bakin yamutsin da ko a tarihin ban taba jin irin azababbin yakin da zamu yi mu da wadannan Sakarai uku da suka hadu a kanmu, tabbas sai kun koma gida domin kuwa bazan taba lamunta na yi tafiya daku 36 zuwa wannan yaki ba. Koda yazo nan a batunsa sai su duka suka sauke kawunansu Kasa suna masu nadama zuwa dan su taimakawa masa hakan ya jawo masa asarar tafiyarsu. Sim sim suka juya suka sauka daga kan tsaunin, cikin rashin kwarini jiki. Sarki ya biyo bayan su, duk jikinsa yakushe ne gaa jini koda Sarkin yaki Safwan ya ga kyawawan 'yan mata daga saman tsaunin sun sauko kafin ya gane 31 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI su waye sai ya zare makami koda suka yi kasa ya gano su Lushmaira ne sai ya yi sak ya kuma cika da tsananin mamaki, kafin su iso kasa sai ga Sarki shima ya nufo su koda ya hango Sarki cikin mawuyacin halin sai ya nufo shi. "Ya shugabana lafiya mai ya faru da kai haka.?" Sarki Abu zaiyan ya dube shi batare da ya tsaya bata lokaci ko inda inda ba ya kwashe duk abinda ya faru a tsakaninsa da zakuna da kuma taimakon da su Shadilat da Lushmaira suka kawo masa, amma sai ya rufe Sarkin yaki da fadan yanda a ka bar su Shadilat da Lushmaira suka biyo bayansu. Nan da nan Sarkin yaki ya kama rantsuwa yana nuna rashin saninsa da wannan al'amari ana wannan abu sai ga Zaiyanu ya iso gurin ganin su Lushmaira da Shadilat ya yi mutukar ba shi mamaki 32 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI kai tsaye ya dubi Sarki ganin halin da yake ciki ya ce. "Ya mahaifina shin mai yake faruwa da kai haka ina dalilin ganin raunika a jikinka, kuma wadannan daga ina suke.?" Koda Sarki ya ji wannan ba tu sai ya ce, "Bana son Su Shadilat su kara koda sa'a daya anan lallai a shiryasu su koma can gida domin kuwa ba zamu yi wannan tafiya da su. Koda jin wannan ba tu sai yarima ya dube shi cikin tsawa ya ce, "Mai yasa kuka biyo mu, ta wace hanya kuka biyo bayanmu, koda ya kurawa Shadilat idanu sai ya ce, "Tabba na gane ki ba ta ko wace hanya ko ka biyo ba face ta hanyar Likita Zauwad ba kuma na nufin shi ya yi muku hanyar biyo mu ba kun bata cikin jama'arsa kun biyo mu.' Su dai basu iya cewa komai domin dukkanin zuciyoyinsu cike suke da fargabaa, da tashin hankali muddin suka 33 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI koma cikin birnin to babu shakka cuta damuwa zata iya sanadin haifar musu da wata matsalar. Sim-sim suka dinga hada komatsansu, Sarki ya sa aka basu dawakai biyu da 'yan rakiya mutun biyar ya yi وو umarni da a raka su. Koda Lushmaira da Shadilat suka ga an hada su da 'yan rakiya sai Lushmaira ta je gaban Sarki ta durkosa gabansa cikin dauriya idanuwanta na zubbar da hawaye, ta ce, "Ya Mahaifina za mu koma kamar yanda umarninka ya zartar akanmu, sai dai ina mai son shaida maka, zuciyarmu tana tsananin son zuwa wannan fili na yaki da za'a yi wanda bana tunanin akwai wani yaki a nan gaba da za'a yi wanda yafi girman wannan yaki, hakika wannan yaki ne da wanda yaje kallonsa shi kansa ya tabbata a girmamashi, a saka shi a sawon babban jarumi a wannan duniya, ya Abbana hakika ina mai bakin cikin 3 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI rashin zuwa na wannan yaki, sai dai ina mai bakin cikin sanar da kai tunda har na kasance babu ni a cikin wannan tafiya to babu shakka ni da aure sai dai a cikin aljanna fiddausi. Koda Lushmaira ta zo nan a cikin batunta sai ta mike ta ja da baya, izuwa ga 'yar uwarta da kuma abokan rakiyarsu. Shi kuwa Sarki Abu Zaiyan sai ya nitse cikin tunanin maganganun Lushmaira daya bayan daya, bai gushe yana tunani ba har sai da ya ga sun kama hanya suna shirin tafiya sannan ya mike ya nufo inda take abisa dokin tana mai kokarin sakar masa linzami ya yinda suke kallon, kallon da Yarima Zaiyan. Sarki ya dubeta sosai kafin ya ce komai sai daga bisani ya ce, "Ya ke wannan 'ya tawa mai biyayya ina son ki sanar dani dalilin da zai hanaki yin aure alhalin kina sane da cewar da aure ne zaki samu cikar burinki na duniya wato da, ko 35 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI 'ya ina son ki sani babu mamaki dan da zaki haifa ya zamu cikon farin cikinki ya zamo yayewar rasa mahaifinki da ki kai tun yarintarki, ina mai son ki gagggauta kawar da wannan kudiri nake na kin yin aure domin na shirya yin bikinki ta zarar mu dawo daga wannan yaki. Koda jin wannan batu sai Lushmaira ta dago da idanuwanta da mamaki ta dubi Sarki Abu zaiyan, shi ma ita yake kallo cikin kulawa, ta sauke idanuwanta cikin tunani, kamar yaya ayi shagalin bikina alhali a duniya ban ta6a ganin namajin da naji ina so ba, kada dai Sarki ya ce ya yi min mijin, in kuwa haka ne tabbas zan taba bijire masa domin kowa in har ban je wannan yakin ba na hadu da jarumin da yafi kowane jarumi yin kwazo a filin daga to babu shakka bazann taba sauyawa ba, in kuwa naje na gani jarumin da yafi kowa jarumtaka to shakka babu shi ne zai zamo mijina, a rashin jarumin da zai soke 36 TURABAR GASKIYA-3 idon Macijiya Burukull Kursum." MADAKI Koda ta kara dago da idanuwanta ya kalli Sarki sai taga dai har a yanzu kallonta yake kuma da dukkan alamu ya karanci abinda zuciyarta ke saka mata, dan haka sai ya yi murmushi, ya се "Za ki aure bayan mun samo nasara mun dawo gida, yake 'yata Jarumi da zai zamo mijinki babu shi a cikin zuciyata, amma ina da tabbacin samun shi kafin dawowarmu." Babu walwala akan fuskarta ta kada linzamin dokinta kai tsaye ta fara tafiya batare da ta bawa Sarki Amsa ba, wannan dalili ne yasa zuciyarsa ta bugo ya ji wani irin a ranshi, nan take ya kwala mata kira. "Ya ke Lushmaira ina dalilin yin biris dani alhalin ina yin magana dake.?" Bata waigo ba ta ce, "Ya Abbana na matsu da nabar wannan guri, bana son na bi abinda zuciyata take kodirtamin, domin kada na bijirewa umarninka, dan haka 37 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI ina mai baka hakuri a bisa abinda na aikata." Nan take suka jera tare da Shadilat kowace fuarta na zubar da hawaye, Sarkin yaki Safwan ya dubi Sarki shi kuwa Sarki sai ya dubi Yarima Zaiyan, a lokacin da Yarima ya kautar da kai ga barin kallon su Shadilat ya ci gaba da al'amarin gabansa domin kuwa abinda Sarki ya yi, ya yi masa dai-dai. Sarki yaki Safwan ya matsa kusa da Sarki cikin girmamawa ya ce, "Ranka shi dade kana ganin barin su su koma yafi tafiya da su alkairi.?" Sarki ya juyo daga barin kallon Yarima ya dubi Sarkin yaki, ya ce, "Nima ina barar shawara gami da hakan, hakika na yi mutukar mamakin yanda suke da jarumta a halin da suka taimake ni a saman tsauni, sai dai ko kadan bana son a ce an fita dasu filin daga domin dalilin son zuwansu bai kwantamin ba." 38 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI Sarkin yaki ya yi murmushi ya се, "Ba na tunanin za su yarda su wuce gida." Sarki Abu Zaiyan ya dube shi, cikin mamaki "Kamar yaya kake nufi zasu iya ,, dawowa ke nan. "Ya shugaba shakka babu domin kowa zuciyarsu bata gida bake daya sun dauke kacokan sun kaita filin daga, ya kake tsammanin Kura da Kare sun tafi neman nama babu Mage?" "A lallai fa zata ji rashin jin dadi to amma mai kake tsammanin zasu yi idan sun je can." Sarkin yaki ya yi murmushi akaro na biyu ya ce, "Ya shugaba kai za a tambaya domin kaga gogewarsu." Sarki ya dan sha mur kana ya ce "А dawo da su, amma da sharadi, sharadin kuwa kada su dinga yawo har sai an isa filin kuma ko da an je filin dasu, kada dayansu ya kuskura ya fito su adana kansu kamar yanda sauran matan da 39 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI muke tafe dasu suka adana nasu kan." Sarkin yaki Safwan ya yi murmushi ya kwalawa wani Babban badakarensa kira wanda shi ne zai jagoranci mai da su gidan" "Ku dawo ya kai Zarfun, Sarki ya bukaci dawowarsu amma kada su sake a cikin dakarun yaki, su mai da kansu kamar dabbobin gida." Gaban yarima Ya yi muguwar faduwa ya dubi Sarkin yaki ya ce. A wane dalili. Da jin haka sai Sarki ya ba shi amsa da cewa "Akwai bukatar su, amma ba a filin yaki ba. Shadilat da Gimbiya Lushmaira suka zo suka fadi gaban Sarki cikin murna suna godiya. Da ganin haka sai Yarima Zaiyan ya turbune fuska, ya bar gurin domin bai so hakan ba. Lokacin da aka cika sa'a biyar a 40 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI wannan gurin sai Runduna ta kara ta shi. Aka ci gaba da tafiya babu ji babu gani. A can 6angaren su Sarki Tamas kowa tuni tafiya ta yi nisa duk kasashen sun hadu guri guda, fushi ne mai tsananin a fuskokinsu cikin tafiyar takama da ihu babu ruwansu da ibadu, dan kuwa babu abinda yake tsayar dasu face gajiya, ko cin abinci Sarakan su uku su kwashe manyan dakarun sun saka su a tsakiya dan kyautata tsaro. A wani fafffadan daji mai yalwar korayen ganyayyaki suka Sarki Tamas ya yi umarni dan a tsaya a kara shiri na sosai domin kuwa sun fara jiyo kamshi abokan gaba. Lokacin da Rundunonin mayaka suka kafa sansuna sai kowa ya fara aiwatar da abinda ke gabansa a can kuwa babbar Tanti da Sarakan uku suka kadaice sai Sarki Tamas ya dubi Sarki Madham da Sarki Husaka ya сe. 41 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI Ya zame mana dole mu yi shirin na sosai kafin a ce sai da muka riske su, tafiyarmu haka kai tsaye ga makiya bata nufin samun nasara kuna sane shi dai yaki dan zambo ne musamman wannan yakin da zamu yi shi da Birnin Lautul Nusur, suna da mayaka masu naci da dagiya wajen ganin sun samu nasara, abinda zuciyata take raya min tun dazu shi ne, ina son mu kasance ciki fatancen shiri ga abokan gabarmu, ma'anar 6atancen shiri shi ne ina son mu ware wata Runduna ta tafi izuwa bisa hanyar da za su nufo, kafin zuwa filin da muke tunanin hadu, su wadannan Dakaru su zamo sun 6oye kawunansu cikin ciyayyai ta yanda babu yanda za'a yi su Sarki Abu Zaiyan su fahincesu a gun. Idan suka wuce su, kafin su yi masu nesa sai su zari masu da kiboyu su yi musu ruwansu, bayan haka sai su yi rufdugu kansu, su yi dauki badadi koda na sa'a 42 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI bakwai ne, na tabbata idan haka ta faru, zasu samu nasarar hallakar da yawa daga cikin Dakarun Sarkin Abu Zaiyan duk da cewar na tabbata babu daya daga ckin Rundunarmu da zasu tsira, ya kuke gani shawarar nan ta yi ko kuwa akwai wanda zai bada wacce ta fita." Da jin hakan Sai Sarki Husaka ya yi ajiyar zuciya ya dubi Sarki Madham ya ce, "Ni dai wanntan shawara ta yi min sai dai kai, ya kake gani.?" Sarkin Madham sai ya tuntsire da dariya ya се. "Babu sake, wannan shawara ta yi, kuma na yaba da kwazo wajen yin wannan zurfin tunani sai dai yanzu kamar yaya za a samar da dakarun da zasu iya yin wannan aiki kasan fa dole a samu masu iya lambo da basaja cikin korayen ciyayi.?' Koda Madhan ya zo nan a batunsa sai Sarki Tamas da Husauka su ka yi shiru daga bisa sai suka dubi juna, Sarki 43 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI Tamas ya yi saurin cewa "Ai babu Rundunar da zamu zaba dan yi mana wannan aikin face Rundunar Sadauki Aksar, ba dan komai ba su ne maharba, kuma duk inda aka san maharbi an san shi da lamfo a bayan bishiya dan haka shi ne zai jagoranci wannan aiki." Nan take sukai na'am da wannan ba tu take aka kira Sadauki Aksar aka sanar dashi abinda ya zai yi. Batare da bata lokaci ba ya aminta cikin gaggawa suka zame jiki daga cikin sahu-sahu na Miliyoyin rundunonin yaki suka bace daga sashin suka nufi hanyar da suka durfafa. A bangaren su Sarki kuwa tun da suka ta shi daga wannan guri sai suka ci gaba da tafiya ba tsayawa ya da zango in har ba sallah ba ko cin abinci, a haka suka kwana hudu, gajiya ta riske wasu daga cikinsu da yawa, lokacin da suka kwana na biyar ne sai murna ta kama wasu su TURABAR GASKIYA-3 MADAKI domin sun san cewar yanzo ne lokacin da za zauna domin a huce gajiya ta tsahon sa'a shida maimakon ta rabin sa'a da suke idan zasu yi sallah ko cin abinci. A wannan rana da rana ta cika na biyar kowa yana sa rai da Umarni Sarki amma Sarki ya yi shiru ya ki ya bada umarni tsayawa, tafiya kawai ake, aka tsaya aka yi sallah Azahar aka ta shi aka ci gaba da tafiya, aka la'asar nan ma aka ci gaba da tafiya, magriba isha'i a sannane Sarki ya yi umarni da a tsaya a nan a huta. Kowa ya fitar da tsammanin hutawa, a ranar irin ta yau, dan haka lokacin da suka ji umarni sai kowa ya cika da farin ciki, kafin ma a fara kafa tanti wasu suka zube kasa, Yarima Zaiyan da Gimbiya Lushmaira da Shadilat kuwa suna jin wannan umarni sai suka cika da tsananin bacin rai domin a san su, ba za'a tsaya ba har sai an isa dajin da za'a fara wannan yaki. 45 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI Dan haka babu wani annuri akan Fuskar Yarima Zaiyan tun daga farin tahowa har zuwa wannan umarni na Sarki takaicensa biyu tafiya da Shadilat, da kuma Lushmaira, ga kuma wannan tsayawar wacce ya fitar da rai da ita. Hadiman da suke masa hidima suka hada masa Tanti, lokacin da suka hattama sai ya yi saurin barin gun, ba ko ina ya nufa ba face Inda su Gimbiya Lushmaira da Shadilat suke. Lokacin da ya isa sai ya şame su, a cikin Tantinsu su biyu zaune, cikin nishadi da walwala, akwai kuyangi biyu da suke masu hidima gabansu kayan marmari ne, sai ruwan inibi a cikin tambula. Koda gabatowar bakin Tantin sai yarima Zaiyan ya yi musu sallama ya shiga cikin tantin koda ganinsa sai suka ci ka da mamaki, Shadilat cikin ladabi da biyayya ta rankwafa ta ce, "Barka da zuwan Yarima, garemu muna fatan 46 TURABAR GASKIYA-3 samun duban goyan baya gareka." MADAKI Koda yarima ya ji wannan daga Shadilat sai ya nemi guri ya zauna, ya kuma dubeta ya ce, "Barkan ki da warhaka, ina fatan komai lafiya.?" Ta yi wani kayataccen murmushi ta kara dora dara-daran idanuwanta akansa, sannan ta ce, "Komai lafiya babu fargaba tunda har Sarki ya ji kanmu ya barmu yin 2, wannan tafiya." Ita kuwa Lushmaira lokacin da ta gan shi cikin dakin sai ranta ya yi mutukar baci, da kyar ta iya bude baki ta ce, "Sannu." A sa'ilin da ya ji yanda ta yi furucin sai da ya dago kai ya dubeta, domin duk rashin jituwar da take tsakaninsu bata tabа nuna masa, a koda yaushe idan zasu hacп zata bashi girmansa amatsayinsa wanda yake gaba da ita. Amma sai ya kanne bai nuna fushinsa ba ya dubi Shadilat ya ce, "Kada ku cire fargabarku, domin а 47 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI kowane lokaci zasu iya komawa gida, domin ni ban lamunci da tafiya da mata ma'abota rauni a cikin irin wannan bakin yaki da zamu durfafa. Koda jin wannan ba tu sai Shadilat ta yi shiru ita kuwa sai Gimbiya Lushmaira ta yamatse fuska cikin kunkuni ta ce, Babu rauni a tare da basadaukiyar mace da zata iya karo da karatan Sadaukai sama da Ashiri kuma ta samu nasara dan haka, ka cire wannan batu a ranka babu halin da zaka mai damu gida. Koda jin wannan batu sai Yarima Zaiyan ya ji ransa ya 6aci da maganar Gimbiya Lushmaira amma sai ya kanne bai bi ta kanta ba, har da dan murmushi ya се. "Sadaukai ko kuma ragwaye, kada ki yi tsammanin ganin kuna yaki a junanku na bajinta ki yi tunanin cewar za ku iya yin bakin yaki da wanda ya taba halarta horon yaki koda na kwana guda ne, dan 48 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI haka ki kiyaye kada ki dauki kan ki a bakin komai, duk bajintar da ku kai a bakin Ruwa na sani bana bukatar ki sanar dani." Koda Gimbiya Lushimaira ta ji wannan ba tu sai ta yi kayataccen murmushi ta ce, "Bana haufi idan akwai jarabawa da zaka auna Sadaukantakarmu, muna saurarenka, in kuma babu abinda zaka jarrabamu da shi, to muna son ka bamu sarari domin mu shaki iska," Cikin tsawa Shaidilat ta doka mata tsawa ta mike tsaye ta ce, "Ya ke Gimbiya kada matsayinki ya dinga mantar dake waye Yarima Zaiyan, kada isa da iko ki manta da isar sa da ikonsa, lallai furucinki haramtaccene a gareshi don haka ki yi biyayya ga yarima Zaiyan." Koda Shadilat ta zo anan acikin zancenta sai ran Gimbiya Lushmaira ya tashi ainu cikin баcin ran ta dubi Shadilat ta nuna ta da yatsa ta ce, "Kada kwarjini 49 TURABAR GASKIY'A-3 MADAKI mulki ya rinjiyi ra'ayinki har ki dinga son farantawa wanda yake son bakantawa zuciyarki, ina son ki sani Ina daukar kaina a matsayin Jaruma Basadaukiya 'yar na gada, dan haka babu wani namijin da jarumtarsa bata taka kara ta karya ba da zai nuna min isa da iko, girman Mulki, kyau, takama basa tasiri a gareni face kawai girman Sadaukantakaа." Lokacin da Lushmaira take sanar da Shadilat wadan nan maganganun sai Ran Zaiyan ya yi mutukar baci zuciyarsa ta hau tafarfasa, da sauri ya matsa kusa da ita ya kai mata wani bahagon mari, cikin bajinta Gimbiya Lushmaira ta sunkuya hannunsa ya mari iska. Wannan al'amarin ne ya kara jefa zuciyar Yarima Zaiyan cikin tsananin bakin ciki, ya saka yatsansa a baki cikin tsananin takaici ya ma kasa cewa komai. Ita kuwa Gimbiya Lushmaira sai ta fashe da dariya ta се, "Ко aljani ya san 50 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI kaidin dan adam yafi nashi, haka bana ko shakka, akwai shakkar mata a zuciyar maza, don haka ka kula da kanka, ruwa ba sa'an kwando bane." Da fadar haka sai Lushamaira ta doka tsaki ta bar cikin tanti, ita kuwa Shadilat sai mamaki ya cika mata zuciya ita kanda bata taba tunanin rashin jituwar Yarima Zaiyan da Gimbiya Lushmaira ya kai haka ba. Da kyar ta samu ta daure damuwarta ta matsa kusa da shi ta сe. Ka yi hakuri Ya kai Yarima Zaiyan hakika zuciyar Gimbiya a kekashe take, ba wai bata nuna biyayya akan ka bane don rashin tarbiya a'a tana haka ne kawai don ta nuna maka cewar ita ma jarumace tamkar, har kullum daukar kanta take kamar kai." Sa'adda Shadilat ta zo nan a cikin zancenta sai Yarima Zaiyan ya dubeta koda ya tsura mata idanu sai kuma ya bushe da dariya, wannan al'amari shi 51 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI ya jefa zuciyar Shadilat cikin tsananin mamaki har sai da ta yi tsammanin Yarima Zaiyan ya kamu da ciwon damuwa wanda har ya haifar masa da matsala ciwon hauka, amma kafin ta yi aune da tunaninta sai taga ya yi shiru kuma ya kara dubanta ya ce, "Ki je ki kirawo min Gimbiya Lushmaira yanzu ina son zan yi magana da ta Batare da Shadilat ta tambaye shi dalili ba, ta juya ta fice daga cikin Tanti, jim kadan sai ga su sun shigo ciki Gimbiya Lushmaira ta nemi guri ta zauna bata ko kalle shi ba, ita ma Shadilat ta zauna a inda take zaune. Koda ganin haka sai Yarima Zaiyan ya dubi Lushmaira ya matsa kusa da ita ya dan sunkuya dan rage tsaye sannan ya ce, "Wutar daji, tafi kama da masifar da za'a kirata da suna KUBUBUWAR AJALI, sunan mai tarwatsa mazaje, a filin daga Sadauki, ya yinda sunan makashin 52 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI dabba, mafarauci, dan haka kada yaki da dabba ya sa ki girman kai har ki dinga daukar kanki, a matsayin jaruma, koda ganin kashe dabbar da kukai, ban yi tunanin dama ke jaruma ce, na yi tunani kamar haka, ashe dama makaminki mai وو kaifi ne. Koda jarumi Zaiyan ya zo nan a cikin batunsa sai tsananin fushi da takaici ya kama Gimbiya Lushmaira kai ba ma ita ba har Shadilat wato duk irin abin da mu kai nasara tana daga kaifin tsinin masukanmu da takubbanmu, tabbas, ya ma raina musu hankali. Lushmaira ta dago da kai cikin 6acin rai ta ce, "Ku ido da ido da Zakanya sai na mijin gaske, duk wannan maganganun da kake na riga na sani kana yinsu ne domin hassada, ina son ka sani ita hassada tana tauye aikinka na alkari, na aminta da duk irin gwajin da kake tunanin za ka yi min in har haka zai tabbatar maka da 53 TURABAR GASKIYA 3 MADAKI cewar mai hannu daya baifi gurgu ba." Da jin wannan ba tu sai Yarima Zaiyan ya yi murmushi domin dama abinda yake son ke nan ya dubeta ya ce, "Da alama za mu iya kasancewa anan gurin har safiya abin da nake so ku sani shi ne a baya da mu kada, na yi tozali da wata Zakanya da take halin laulayi, Wani bajimin zaki da ya zamo shi ne mijinta yana kewayeta tar da shinshinar jikinta, wannan shi ya tabbatar min shi ne mijinta. Abin da nake so da ku aikata har ya sa na ji cewar kin isa jaruma ki tafi daga idar da sallar Asuba zuwa ga wannan zakanyar ki dauko jaririyar da ta haifa." Koda Lushmaira ta ji wannan umarni daga Yarima Zaiyad sai hankalinta ya dugunzuma ya tashi ainun ta yi shiru, na dan lokaci daga bisani sai ta dago kai ta yi murmushi hade da cewa. Ka dauki batunka kamar ka yi 54 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI rubutu akan dutse in har da rai da lafiya gobe kafin kafin gari ya gama wayewa zan zo maka da jariryar kada, amma ban damu da ka yardar da jarumtakata, ina son ka sani ranar wanka ba'a 6oyon cibi, ranar da zaka gano ma'anar jarumtakata ita ce ranar da jarumtakarka zata dakushe, a idon duk wani jarumi dake cikin kasar Lautul Barus ya zamana ni ake gani a matsayin jarumar da ta kaini, kamar yanda aka rasa jarumin da ya kai mahaifina a duk wannan kasar. Koda fadin hakan sai ta fice daga cikin Tanti ita kuwa Shadilat sai ta cika da tsananin mamaki, ta yaya ake Lushmaira take daukar kanta amatsayin wata uwa a harkar jarumtaka, alhalin ni din nan da muka kara banga wani kumarinta ba. Shi kuwa Yarima Zaiyan sai mamaki ya cika shi, ba komai bane ya sa shi mamaki face irin karfin gwiwar da Lushmaira take da shi, bai san sa'ar da ya 55 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI fice daga cikin Tanti saboda tsananin mamaki. Ita kuwa ku da ta fita daga cikin tanti sai ta nufi can wani guri da babu kowa ya samu guri ta zauna, ta fara tunanin. Lallai na tsokanowa kaina abinda yafi karfina, zaki ku da makami abin lura ne a lokacin da za ka yi yaki da shi, ta yaya zata iya yin yaki da Zaki har ta samu ta daukar masa da, sabuwar haihuwa, sam wannan al'amari ba zai yiwu ba shi kansa Yarima Zaiyan ya yi hakane kawai dan na rasa rayuwata. Kai ba zai so mutuwata ba duk da Kiyayyar da take tsakaninmu, ya yi hakanne dai kawai dan ya kore ni, in kuwa hakane ko da zan salwantar da rayuwata sai na yi shiri da asuba na tunkari gurin wannan zakanyarmo wiw ma 95 1 ah Aikuwa washe gari tun da asuba ana idar da Sallah ko tsayawa yin addu'a 156 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI bata yi ba kamar yanda Sarki yake a lukutan da aka gabatar da sallah, sai ta mike ta sulele ta cikin ciyayi ta bi ta wata siririyar hanya. Ta nufi gurin da Yarima Zaiyan ya sanar da ita, cikin rashin sani kuwa tana barin gurin sai aka shafa addu'a, daga nan sai Sarki ya yi umarni akan a ci gaba da tafiya. Ko yarima bai yi tsammanin hakan ba amma da ya ji wannan sanarwa sai farin ciki ya cika masa zuciya domin ya na ganin lokacin da Lushmaira ta nausa da gudu cikin dawa, ya tabbata koda ta dawO ba zata taba samunsu a hanya ba dole ne ta koma. Shadilat kuwa sai hankalinta ya dugunzuma ta shiga damuwa ainu cikin rashin karfin haka take tafiyar duk ta damuu. Sai da Gim Gimbiya Lushmaira ta yi tafiya mai nisa a sannan ta isa inda Yarima zaiyan ya kwatanta mata sai tawyi tsaye 57 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI tana duban wajen, sai an fada da gani biri zai ci mutum. Dajin ya zamo ma'abocin kwarjini sannan shiru ya mamaye gurin bake daya, dan haka sai ta fara waige waige cikin sanda. Bata ji doriyar wata dabbar ba, dan haka sai ta rasa abinda ya kamata ta yi, domin ta samu ta gano inda Zakanyar take, tana tsaye cikin dube dube sai kawai ta ji gurnani daga can nesa kadan, ko da ta tabbatar da wannan gurnani ba na komai bane face gurnani zaki sai ta gyara tsayuwarta ta kuma kurawa gurin idanu, tana tsaye sai ga wani narkeke Zaki ya fito daga wani kogo na bishiyar darbejiya. Da fitowar wannan Zaki sai ya 'yi girgiza wanda ya haddasar da korar jikinsa ta tashi sama, ya saka kafarsa yana sosa kansa. Da sauri Gimbiya Lushmaira ta koma da baya ta 6oye domin ganin Zakin ya yi mutukar ranata, tabbas ko da ita da Shadilat da kuma Yarima Zaiyan za su hadu ba za su iya da wannan Zakin ba. Tana nan rabe tana son ganinya kauce domin ta sulele ta koma can in 58 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI da ta fito domin ta san wutsiyar Rakumi ta yi nesa da kasa, in ma ba rainin hankalin ba ta yaya za gwada jarumtakar dan adam da Zaki jrin wannan alhalin kuma baka rike da komai, tabbas sai yau ta kara yarda Yarima Zaiyan makiyinta ne kuma baya kaunarta.... Numfashinta ya dauke lokacin da ta hango Zakin ya nufo inda take 6oye gadangadan ta yi sauri janye jikinta dan kada ya lura da ita domin ta fuskanci ba ita ya gano ba a kwai inda ya yi niyar nufa. Tana makale a jikin bishiya ya zo ya wuce, yana gurnani. Yana wucewa Gimbiya Lushmaira ta yi ajiyar zuciya har ta dauki hanya zata koma sai kuma ta tuna da cewa waye mahaifinta ta tuno irin gwagwarmayar da mahaifinta ya yi a duniya kafin ya rasa rayuwarsa, ta tuna irin bajintar da take so ta yi anan gaba na soke idanuwan Macijiya Burukul Kursum. Nan da nan wani irin karfin ya shigeta ta koma da baya ta dubi Zakin da ya yi nesa ya nufi wata fadama dake nesa. Cikin sanda ya juya ta nufi inda 59 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI Zakin ya fito, koda karasawarta sai ta sunkuya ta leka cikin abin da bata zato ba shi ya faru tana lekawa sai taga jariran zakuna gudu

Chapter 2 of 3