Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 3
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels Lokacin da runduna ta nausa bakin birnin L Baitul haural jama'a da suka yo musu rakiya basu koma ba suna biye dasu suna daga masu hannu dan yin bankwana dasu, wasu na yin kuka wasu kuma yin kabbara dan karawa tarin DHOG Dakarun PTRS karfin gwiwa. Shi kuwa Yarima Zaiyan har zuwa wannan lokacin bai daina waigen wannan mai daradaran idanuwa ba, ba komai bane yasa ya damu da dubata sai tunanin da ya cika masa zuciya yana ganin cewar ba yau ya fara saka wadannan kyakyawawan idanuwa ba a cikin nasa idanu. Koda ya fuskanci runduna ta kara yawa nisa tsakaninsa da wadannan matan da suka biyo a yarin likita Zuwad sun yi masa nesa domin tazarar dake tsakaninsu ya kai kimanin Runduna uku, wanda yawansu ya kai kimanin dubu goma da doriya, wannan dalili yasa Yarima Zaiyan ya hakura da waige ya cika gaba da sa kansa gaba tare da yin kabbara kamar yadda daukacin dandazon mayakan kasar suke yi. TURABAR GASKIYA-3 MADAKI Shi kuwa Sarki Abu Zaiyan bai lura ma da halin da Yarima ya shiga ba, gabansa kawai yake kallon yana kiran sunan Allah, da haka har aka zo bakin ganuwar garin, koda zuwa wannan bakin ganuwar sai Sarki ya daga hannu yana mai bankwana da al'ummarsa wannan al'amari ne yasa bake daya jama'ar kasar Baitul Haural suka kaure da kabbar suna masu yi masu fatan samun nasara, da haka har aka fice daga birni aka mai da kofar birni aka rufe jama'a suka koma gidajensu. A wannan lokacin 'yanfashin da suke fakewa cikin dajijjikan da suke hanyar shiga birnin Baitul Haural sai suka ari ta kare suka nausa cikin maboya domin ganin yanda Rundunonin mayaka suka durfafo hanyar, abin da suke zargi shine yau ran Sarki ne ya 6aci da abinda suke aikatawa dan haka ya yi wannanı gagarumar hawa ya zo domin rushe su ya murkoshe su, aikuwa zaman mafakarma sai ya gagari domin ganin irin yawansu suna ganin da an nufo inda suka boye za'a riskesu dan haka suka ta shi 5 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI suka haye dawakansu suka nausa cikin dawą cikin tsananin firgici. Kananun dambobi kuwa da tsuntsaye sai hankulansu ya dugunzuma cikin tsananin firgici suka ta shi daga gidajensu suka arci ta kare. Sawayan dawakai gami da kabbarar da Dakarun kasar Baitul Haural suke yi shi yake saka saka faduwar gaba ga dukkan wani mugu da ya fake dan samun makafa ya cutar da wani. Lokacin da Aka yi sa'a hudu da rabi ana wannan tafiya Sai Sarki Abu Zaiyan ya yi umarni dan a tsaya a yi sallah kana a ci gaba da tafiya. Koda aka saurara da wannan tafiya na kasa da dawakai da rakuma sai suka sauko nan fa aka shiga naura alwala, cikin kankanin lokaci aka kira sallah rashin Ibin Haishan limamin kasar da yake ba shi aka yi wannan tafiya yana gida, hakan ya sa Sarki Abu Zaiyan ya ja sallah. Bayan an 6 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI idar aka thaye dawakai aka ci gaba da tafiya. Sai da aka kwana biyu ana wannan tafiya babu abinda yake tsaida su face yin sallah ko abincin ba fara girkawa ba kowa da dan guzurin da ya taho da shi yake yin amfani. Lokacin da aka kwana biyar ne a cikin dokar daji ana wannan tafiya sai Sarki ya yi umarni da a tsaya a lokacin ba su fi sa'a hudu ba da yin asuba bayan sun yi ta shi daga ibarci, sun yi sallah sun ci gaba da tafiya. Gurin da Sarki ya yi umarni a tsaya guri ne mai koramai da yawan sanyi, guri ne imai kyakyawan yanayi duk da cewar guri ne mai hatsari gaske, domin kuwa ba'a rasa kuraye da zakuna a gun mafi akasari gurin ne ma guri mafi son zaman wadannan dabbobi domin su shakata su huta, amma jin doriyar jama'ar Kasar Baitul Haural yasa suka arce suka nemi TURABAR GASKIYA-3 MADAKI mабoya domin suna zaton tashin alkiyamarsu ya yi, kamar yanda suka sani daga magabatan iyayensu da kakanninsu, akwai ranar da zasu gushe ya zamana babu bakya daya. Lokacin da Rudunoni suka ja dagą suka tsaya sai aka hau kafatantuna domin dama a duk inda aka samu kwana biyar ana tafiya cikin irin wannan tafiya to Sarki sai a irin lokacin yake bukatar a huta musamman idan yaga guri mai yalwar nutsuwa da kuma ya kwanta masa, dan haka suka sauka daga dawakansu. Yarima Zaiyan da Sarki aka kafa musu tanti mafi kusanci da juna Sarkin yaki Safwan tantinsa yana kusa da na Sarki ya zamana sun saka Tantin Sarki a a tsakiya. Koda da wasu tsirarin dakarun da suke biye da shi suka nufo tantin sai Sarki Abu Zaiyan ya dubi Tantinsa dake tsakiya ya kuma dubi Tantin dansa da na TURABAR GASKIYA-3 MADAKI Sarkin yakinsa a gefe da gefensa sai ya dubi Sarkin yaki Safwan ya ce. "Ya kai Sarkin yaki Safwan ina dalilin saka tantina a tsakiya, alhalin kana sane da cewar ban yi umarni da hakan ba.?" Da jin wannan tambaya sai Sarkin yaki Safwan ya sadda kai kas ya dubi Sarki ya ce, "Ya shugabana idan ban yi dai-dai ba ina fatan hucewar zuciyarka, na kuma aikata hakanne dan tsaron lafiyarka, kamar yadda Yarima Zaiyanu ya tsara ni kuma na ga daidai din hakan, ya shugaba tsaron lafiyarka a gareni wajibi na ne, domin ba ni da wani aiki da ya wuce hakan." Koda Sarki ya ji wannan ba tu daga Sarki yaki Safwan sai ya yi murmushi ya ce, "Kada ka manta a lokacin da aka rantsar da kai a matsayinka na Sarkin yaki, ba ka dau alwashin kare lafiya ta ba, ka dauki alwarin kare al'ummata ne iyaka 9 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI gwargwadon ikon, ba ni ba, sanin kanka ne bana bukatar tsoron kuwa face na Ubangiji da ya halicceni, dan haka ina son a dauke wannan tantin a kai min shi can saman wannan tsauni ta yanda zan kasance ni kadai, SIKIU kuma cikin kula da al'ummata. Koda Sarkin yaki Safwan ya ji wannan ba tu sai hankalinsa ya dugunzuma domin gurin da Sarki ya nuna guri ne da baki daya mafaka ce ta mugayen dabbobi masu hatsarin gaske, dan haka ya yi saurin rissana bisa kafafuwansa ya ce. ya shugaba ka yi sani wancan guri da kake nunawa babu komai a bisa saman tsauní face, dabbobi masu hatsarin gaske, BUR ka yi hakuri ka zabi wani guri ba can ba. VSarki Abu Zaiyan sai ya dakawa Safwan tsawa ya ce, "“Ka barni a can din ina sane na zabi can din kuma ba dan komai na zabi gurin ba face na yi gadin al ummata вв na tabbata idan muka 10 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI shagala cikin hutawarmu wadannan dabbobi zasu iya saukowa suka bi bayan wasu daga cikin jama'ata su nemi cutar dasu, amma muddin ina gurin da zarar dabba ta fito ni kuma zan yi karo da ita har sai lokacin da kowa ya gama hutuwa kafin cikar sa'a biyar cif da na dibar mana, dan haka bana son ka kara wata magana yanzu take ka yi umarni a kai min tantina can. Yarima Zaiyan dake zaune a gefe bai iya cewa komai domin ya san in dai Sarki ne akan jama'arsa sai Allah, zai iya cewa yafi son su da shi kansa, dan haka ya ja bakinsa ya yi shiru duk da bai son hatsarin dake gurin ba amma yana iya jiyo hargagin zakuna da kukan wasu da'ikan dabbobin da bai san ko wane iri bane. Shi kuwa Sarkin yaki Safwan take ya yi umarni da wasu dakaru su je gurin su kafawa Sarki Sansani kamar yanda ya bukata, amma ya yi umarni da kada su bar gurin su tsaya su yi gadinsa. 11 TURABAR GASKIYA-3 3-VAIK2V MADAKE n kuma Bangaren Likita Zauwad da jama arsa sat su Shadilat da Lushmaira suka kasande elkintsanadin farin ciki ganim har nukwashenikwanaki Biyar a'na wannan tafnyar dasu batare da anganos ba, ganif haka sui suka saujiki suka shiga harkokinsu San ransu amma duk da haka fuskkokmsarrufo sukesk ak nог вned sар nShadilarta dubi Gimbiya Lushmaira taka wata harika na yi mutakat farckiidand kasanee eikin wannan tallya godiyata ba zatai kare ga Likita Zadwad sdnnan ieAlalyasa mun BawA?iA Rostinlaniyalazan ypa masa kyauta ta mmusamhan, sai dai abiнаа уаkе fadaimita ngaval shi mekyanznidan Yarimko Bansurrgano ind bakys gamin zasw łya sawaalaK 2 sai tbye mnuti shaclat te de; TabbaPidhatsurkiya ganmürzathya dagd mana kafa safedarZai Saka tsaro akanmu 2 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI sosai amma bana jin idan yarima ya ganmu zai barmu take batare da Sanin Sarki ba zai sa a maidamu gida." Da jin wannan ba tu sai gaban Shadilat ya fadi cikin tsananin bugun zuciya ta ce, "Ya ke 'yar uwata aikuwa in haka ne ya zama dole na canza tufafi domin a lokacin da yarima ya dawo kaina domin ya kara bincikena a yayarin da Sarki ya kira shi, ina ganin kamar ya so ya gane ni, domin har muka baro cikin fada muka nufo hanyar waige yake yana dubana ganin haka yasa na sauya gurin tsaiwa duk da haka ina kallonsa yana ci gaba da waigen kan layin da nake, tabbas na san har yanzu bai aminta da zuciyarsa ba zai ci gaba da dubana, dan haka ya zama dole na sauya kayan jikina da wata daga cikin matan da muke tare." Koda Shadilat ta zo nan a cikin batunta sai Gimbiya Lushmaira ta dubeta da kyau ta се, 13 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI "Tabbas duk wanda ya sanki bayan 6oye idanuwanki da kika yi, idan ya ganki cikin wannan mayani na rufe fuska zai iya shaidake ba dan komai ba saboda launin idanuwanki ina mai goyan bayan da ki sauya kayanki yanzu domin a wannan lokacin Yarima zai iya zuwa wannan guri domin ya ci gaba da bincikensa, amma yanzu kada ki tunkari kowa daga cikin wadannan matan bari mu nemo Likita Zauwad." Nan take Shadilat ta amince take Lushmaira ta bi wata hanya ta nemo Likita Zuwad ta zo da shi izuwa in da suke. Batare da 6ata lokaci ba suka kadaita acikin Tantinsu. Lokacin da suka samu guri suka zauna sai Gimbiyar Lushmaira ta kwashe duk abinda Shadilat ta sanar da ita da kuma bukatarta ta sanar shi. Koda gama jin haka sai ya yi shiru na tsawon lokaci daga bisani sai ya dago da kai ya dube su sannan ya ce. 14 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI "Hakika kun saka ni cikin tsaka mai wuya, tabbas idan ban yi wasa ba sai kun sa Sarki ya yi fushi dani, ina son kú sani shi Yarima Zaiyan mutum ne mai tsananin kaifin basira tunda har ya dora zargin akanki babu shakka ko mai zaki yi sai ya nemo ki abinda zai hana ya gano ki kuwa hanya daya ce, wannan hanyar ba wata hanya bace face, zaki kasance cikin tanti daga nan har zuwa lokacin da za mu ci gaba da tafiya muddin zaki fito to babu shakka ko mai zaki sauya sai ya gano ki domin ina da tabbacin zai zo nan a yanzu, idan kina cikin tantinki ba zai taba shigowa ciki ba, amma in har kika fita to zai ganki kuma zai sa amai dake gida, lkawari daya nake so ki daukar min koda a gano ki dan Allah kada ki taba nuna inasa cewa ni ne na sanadinki zuwa nan. Shadilat da jin haka sai ta yi na'am da batunsa take kuma suka mike ya koma bakin aikinsa ita ma Lushmaira sai ta 15 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI fice tabarta cikin tanti lokacin da Lushmaira ta fita sai idanuwanta suka kan wata korama ta da ruwa ki zuba farin ruwa ne fat mai sheki saboda tsananin haske dan haka sai nan take ta ji sha'awa shiga ruwan ta yi wanka ya kamata. Bata tare da ta shawarce kowa ba sai ta nufi bakin ruwan da yake ya yi baya da inda sansanin jama'ar su suke, gadan gadan ta nufi gurin koda zuwanta bakin ruwa sai ta cire mayanin dake rufe da fuskarta, ta kuma cire dogowar rigar da take jikinta ya zamana daga ita sai wani dan bantai da rigar da ta rufe mata mama. Kai tsaye ta daga tsalle ta fada cikin wannan ruwan tsundum. Shi kuwa Yarima koda mahaifinsa ya tafi izuwa saman wannan tsaunin sai nan da nan tunanin wannan da ya gani ya dawo masa nan take sai ya mike tsaye ya nufi sansanin matan da suka taho da su dan yi musu girke girke da kula da lafiyarsu. 16 TURABAR GASKİYA-3 MADAKI Tun daga nesa Likita Zauwad ya hango shi nan take sai ya nufo shi cikin dan murmushi "Barka yarima da wannan Nokaci.ь д Yarima Zaiyan ya dubi likita Zauwad da murmushi akan fuskarsa ya ce, "Barkan babban likita da warhaka, ya jama'ar taka sina fatan dai komai lafiya?' Likita Zauwad ya dubi Zaiyan cikin murmushi ya ce, "Ranka ya dade ai kowa lafiya babu wani abu." Da jin haka sai Yarima Zaiyan ya girgiza kai ya ce, "Haka ake so, amma akwai wani bincike da nake son yi a cikin jama'ar da ka wo dasu ba dan ina zargi ka staho da wasu ba, a'a sai dan ina zargin akwai wata da ta 6adda kama ta shiga cikin jama'arka batare da saninka ba." Dal jin wannan al'amari sai Jikin Likita Zauwad ya kama rawa bakinsa cikin trawa ya се. пoD aр iamo an eA 17 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI "An ya kuwa ya shugaba, amma tun da idanuwanka sun hanga maka ba zan yi maka musu ba, amma da wuya hakan ta faru, domin ko yanzu na duba duk jama'ar da muka taho dasu." Yarima Zaiyan ya ce, "Kada ka damu na san ba lallai ka iya gano hakan ba domin dama a boye take kuma ba zata taba bayyana fuskarta ba. Da jin haka sai Likita Zauwad ya yi shiru Zaiyan ya yi gaba yana duba yanayin jama'ar da suke ta faman aikace aikace, shi kuma zauwad na biye da bayansa, duk tantin da suka nufa suka ji motsi sai Yarima Zaiyan ya ce, "Ayi sallama da na cikin a haka har suka wuce Tantuna kusan goma, ana sha daya ne, Yarima Zaiyad ya tsaya duk da babu motsin kowa a ciki amma sai Yarima ya dubi Zauwad ya ce "Su waye a cikin wannan Tantin.?" Likita Zauwad ya yi shiru batare da ya ce komai ba. Domin kuwa ya san 18 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI cewar Shadilat ce da Lushmaira a cikin, koda Zauwad ya yi shiru sai Yarima ya kara yi masa tambayar. Likita ya ce, Babu mamaki su Haisara ce matar Sarkin yaki." Yarima Zaiyan ya dube shi cikin rashin fahinta ya ce, "Kamar ya ya kana ji, dama akwai wani tanti da baka san ku su waye a ciki ba.?" Likita ya dan yi murmushi ya ce, "Ya shugaba abunne da yawa, amma haka ne wannan tantin Haisara ce, mun kuma barota tana girki a baya." Zaiyan ya dan matsa kusa da dakin ya ce, "Tun da babu kowa bari na leka domin ina zargin wani abu daga cikin wannan tanti, yanda ya zama shiru akwai alamar sirrin 6oye a cikinsa saboda tunda muka taho nake nazarin tantuna idan babu mazauna cikinsa akwai dalilin akwai masu zama, amma shi wannan ya yi kurum kamar kurma, dan haka bari na duba. 19 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI Gadan-gadan Yarima Zaiyan ya nufi cikin Tantin ya leka kansa, shi kuwa Zauwad sai ya yi tsaye sak domin ya riga ya san a sirin Shadilat da Lushmaira ya gama tunowa, bisa mamakinsa sai yaga Yarima ya dawo da kansa waje ya ce. "Da mamaki ace, an kafa tanti babu kowa a ciki haka zalika babu alamar kowa din.?' Da jin wannan batu sai farin ciki ya kama. Likita Zauwad domin ya fuskanci bai yi sa'ar ganinsu ciki ba, nan ya yi hamdala ya kuma dubi Yarima ya ce, "Babu damuwa zan binciki masu zama a cikin kafin mu bar gun" Kafin Yarima ya kara cewa wani abu sai suka ji karar ihun namun dawa daga can bayansu, kodn juyawar Yarima sai yaga an wani zaki ya yi sufa a sarna ya nufi wani 6angare na da koramar nan take, batare da ya jira komai sai ya zare makaminsa ya nufi gurin gauan gadan. Cikin tsananin fusata koda 20 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI ya isa gurin sai ya daka tsalle ya fada farfajiyar gurin ya yi tsaye cikin tsananin mamaki domin koda ya isa sai yaga babu komai a gurin sai gawar wata Kada da zaki da aka soke shi a makoshi. Nan take mamaki ya cika masa zuciya ya fara waige-waige amma bai ga kowa ba, ya isa inda zakin yake kwance matacce sai ya lura da mashin tabbas mashin irin mashin da aka sana'anta shi ne daga kasar su, to waye ya yi wannan aikin. Ga jini yana zuba daga jikin zakin ita kanta Gadar jini ne yake malala a jikinta alamar yanzu yanzu aka aika dasu barzaho. Nan take zargi ya shiga ransa ya fara kewaya gurin sai da ya kusa rabin sa'a yana zaga bakin ruwan nan amma bai ga kowa ba, a sannane Likita Zauwad ya kara so gurin shima ya taya shi dubawa. Har yarima Zaiyan ya juya zai bar gun sai kawai ya hango wasu suturu a makale 21 TURABAR GASKIYA-3 a jikin wata bishiya. MADAKI Koda ganin wadannan suturu sai mamaki ya kama shi take ya nufi suturun ya saka hannun ya dauka kayan mata ne dogayen riguna irin na matan da suka fito da su, nan take hankalinsa ya dugunzuma ya nunawa Zauwad kayan ya се. "Shin za ka iya shaida masu wannan kayan.? Zauwan ya girgiza kai cikin alamun rashin sani ya ce, "Ya shugaba tabbas kayan kaya ne irin na matan da muka zo da su, amma ba zan tantance kayan wacece ba. Zauwad ya gane ko wane kayane ba kayan kowa bane face kayan Lushmaira nan da nan shima ya shiga tsananin mamaki ya dubi Yarima ya kara da cewa "Abinda ya kamata, yanzu ka shaida kayan ko wacece zata zo ta dauka ka ga idan ka gansu a jikinta zaka ganota watakila ita cе TEWEX 22 TURABAR GASKIYA-3 MADAKІ wacce kake zargi da satar hanya ta biyo bayanmu." Koda jin wannan ba tu sai Yarima Zaiyan ya girgiza kai ya ce, "sam haka ba zai yiyiwu ba domin kuwa idan na bar kayan nan a nan dole zata dauka ta canza musu kama, amma yanzu idan na tafi dasu, koda a ce wacce ta biyo ce dolenta ta hakura ta koma tunda ba zata ci gaba da biyo mu tsirara ba, koda ma ta biyo mu farat daya zamu shaidata dan haka mu wuce mu koma cikin al'umma” Koda gama fadan haka Sai Yarima ya yi gaba abinsa shi kuwa Zauwad sai ya bi bayansa cikin matsananciyar damuwa da mamakin Lushmaira da ta iya karawa da wannan narkekiyar dabbobin masu hadarin gaske. Al'amarin Sarki Abu Zaiyan kuwa tun sa'ar da ya nufi saman tsauni ya ga wasu dakaru da Sarkin yaki Safwan ya barsu dan su kula da lafiyar tsaitsaye sai 23 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI ya dube su ya ce, "Ku kuma mai kuke anan.?" Daya daga cikinsu cikin rawar murya ya ce, "Ya shugaba Sarkin yaki ne ya ce mu zo don muyi tsaron lafiyarka, har ka kwanta ka yi barci." Da jin haka sai Sarki ya dube su ya ce, "Kun taba ganin inda Kura tayi tsoron lafiyar Zakin dawa.?" Su duka suka duburburce suka kama kallon juna. Koda Sarki Abu Zaiyan yaga basu fuskanci abinda yake nufi ba sai ya ce, Ina son ku sani Kura ba zata tabа tsoron lafiyar Zaki ba, dan haka ina mai umartarku da ku je ku sanar da shi duk wanda ya kara zuwa nan domin ya tsoron lafiyata to babu shakka sai mun gwabza yaki da shi, domin a bambancin tsakanin aya da tsakowa." Da jin haka sai suka yi sim-sim suka sauka daga kan Tsaunin suka koma 24 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI kasa, koda saukar su sai Sarki ya dubi can nesan saman tsauni sai ya lura a she wasu gungun Zakuna ne sun kai kimanin sun goma sun yi cirko cirko suna kallonsu, ashe abinda ya hane su da zuwa inda wadannan dakaru suke ganin dogayen masu a hannunsu dan haka suna sauka sai suka tada jijiyoyin wuya suka fara harbin iska suna gurnani." Shi kuwa Sarki da yaga haka sai ya fasa shiga cikin tantin ya tsaya yana dubansu, duk irin jarumtaka da Sarki yake takama da shi sai da ya ji shakkar wadannan zakuna domin Kananun cikinsu zasu iya kai girman dan marakin jaki, kuma su biyu ne kananun sauran manya kuwa kowanne zai iya kai girman bajimin Sa. Babu abinda yafi abinda yasa ya kara jin shakkarsu sai ganin yanda suke bude bakunansu wasu irin tsaratan kaifafan hakura suna haskaka masa fuska, 25 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI ga wani yawu yana dalala, koda suka kusa kara sowa sai ya duba jikinsa ashe ya sha'afa ko 'yar karamar wuka bai hawo da ita ba. Aikuwa sai suka kara kaimi suna zagaye shi, wannan al'amari ba karama tada hankalin Sarki ya yi ba amma saboda tsananin jarumta sai yaki ya sauka kasa ya nemi agajin dakarunsa, duk da cewa yasan daga inda yake zuwa saman tsaunin akwai nesa sosai, bare ma ko ba nisa ba zai taba neman taimakonsu ba, nan take sai ya sauke ajiyar zuciya ya dubesu kwanon abincinsa da ya taho dashi sai ya ajiye shi a gefe. Ya murda jikinsa ya bada wani sauti karas. Kafin ya yi aune wadannan Zakuna sun taso masa haikan kuma su duk. Cikin tsananin zafin nama shima ya yi kansu, nan take suka kaceme suka hargitse da tsananin hargitsi mai munin gani, duk irin wannan gunji da suke 26 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI jama'ar kasa basa ji duk da,cewa Sarkin yaki Safwan yana zaune a kasan tsaunin domin ya tabbatar da tsaro amma komai basa jin sai. shiru da yalwata a tunaninsu ma yąnzu haka Sarki ya yi barci. Abin da, basu sani ba ashe Sarki na can yana arțabu da zakuna masu tsananin jin yunwa da da kishirwa, dama haushinsu suke ji sun zo sun mamaye musu guri. Da farko Sarki ya fara kokarin wajen kai musu bugu da hannunsa amma da tsamari ya kai tsamari sai ya fara tsille musu, domin koda ya doke su sai sun yage shi a hannunsa, ko kuma su bangaje shi wanda idan suka bangaje shi sai ya ji kamar wani katon dutse ya bangaza, dan haka cikin Kankanin lokaci suka dimauta shi suka dugunzuma masa lissafi. Ya yi danasanin rashi zuwa da Takobi domin da akwai takobi a tare dashi da tuni ya gama dasu, ko mai gama dasu 27 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI ba da tunanin su faman jin tsananin azaba. Babbar cikinsu ita ce mai tsananin dabara yaki da iya fada, domin sai Kananun sun yunkura suna fafatawa dashi, sai ita kuma ta ja da baya ta dako tsalle sai dai ya ji ta bangaje shi, haka nan suka dinga wannan dabara har Sarki ya fara fita daga haiyacinsa. Da kyar ya samu ya kama Wata zakanya da ta take kokarin cafkar masa hannun ta cinye ya yi tsalle ya dokar mata fuska, ta yi wata kara ta kara nufo shi ya kara yin karfin hali ya kara nausarta nan take ta yin laushi, amma saboda tsananin naci sai da ta kara nufo shi koda ganin irin wannan taurin ran nata sai ya shammace ta na zuwa ya dagata sama ya cillata can nesa da nan take ta rikito izuwa kasa gurin wannan koramar ruwa da Gimbiya Lushmaira take. A wannan lokaci Gimbiya Lushmaira da Shadilat suna boye a 28 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI jikin katangar tsaunin nan sai kawai suka ga wannan zakin ta rikito kasa kuma ta fadi kasa matacciya, sai hankalinsu ya yi sama suna daga kawunansu sai suka hango Sarki Abu Zaiyan yana fafatawa da Zakuna a lokacin da ya yi tsananin jigata da kyar yake iya daga hannu ya kare kansa, nan take suka daka tsalle suka dauke makamansu suka haye saman tsaunin da gudun gaske. Koda suka isa tuni Sarki ya gama galabaita ya zamana da kyar yake iya bude idanuwansa, koda suka hawo saman tsaunin sai suka farwa wadannan Zakuna da suka da sara kafin kace meye wannan tuni sun karar dasu, lokacin da suka gama yakar wadannan dakaru Sai Shadilat da Lushmaira suka nufi hanyar sauka dan kada Sarki ya gane su domin ko a lokacin da suke kwafsawa da wadannan Zakuna suna yi suna rufe fuskokinsu. Har sun bi hanyar sauka sai 29 TURABAR GASKIYA-3 MADAKI دو Sarki ya ce "Ku dakata ya ke 'yata." Koda suka ji maganar Sarki suka tabbatar ya gane su sai suka tsaya suka jiyo a hankali da yake a lokacin Shadilat ta cire dankwalin kanta ta bawa Gimbiyar Lushmaira ta yane jikinta dasu dan haka ba a iya hango jikinsa dai dai kaurikanta. Koda suka tsaya sai Sarki ya mike tsaye da kyar ya ce, "Ku bani labarin yanda aka yi kuka biyo bayanmu alhalin a cikin lissafin tafiyarmu babu

Chapter 1 of 3