Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 2
tafara kamuwa da soyayyarta. Yau gashi Sadiq yasamu Fatima adalilin Hajiya Murja. Zanci gaba.....HAJIYAR BUK PART 11 Sadiq inaso insanar dakai abinda najima ina boyewa azuciyata kasancewar abin yazomin ta yanda banyi tsammaninsaba Sadiq Hajiyar BUK dakake ganin numberta awayata Bawani alaka dake tsakaninmu da ita illa Takasance cikin Halin jarraba daga ubangiji Allah yajarrabeta da Ciwon So azuciya soyayyar Dan dake sa'a da dan cikinta Hajiyar Buk Takamu da soyayyata azuciyarta takasa danne zuciyarta wanda takai har ta furtamin da bakinta cewar zata aureni matukar zan amincemata tunda hakan bai sabawa Shari'aba. Cikin tsananin Kaduwa da razana Sadiq yamike zumbur tamkar an tsikareshi da allura yace Aure Ina Sam hakam bamai yihuwabane wallahi bazaiyihuba bazantaba goyama baya ka auri Sa'ar mamanmu ba Ita batada hankali take wannan furucin sam batamasan abinda ke damuntaba. Allah sarki Sadik da ka tina da yanda Allah ke kadartawa bawa al'amarinda baiyi zatoba da bakai saurin rantsewaba abinda nake sakawa kenan azuciyata Nace Sadik kwantar da hankalinka ka tsaya kasaurareni sannan sai ka yanke hukunci da kake tinanin yankewa nakwantar dakai ina rarrashinsa amma shikam tamkar ankara tunzurashi yasake fusata sai babatu yake Indai ina tare dakai inasonka da gaskiya bazan barka kakai kanka inda same cutarda kankaba Tsohuwacefa kada kadaukomana rigimar da zatazam fitina agaremu wallahi hajiya zanje nafadama idonsa cike da kwalla yajuya zai fita. Nace Sadik tsaya kaji sadik sadik ina tuni yakama hanyar ficewa daga falon da muke zaune yanufi cikin gida Dakarfi nace Sadik Fatiman ka Ya ce awajen hajiya murja katsaya kasaurareni Chakk yaja birki yatsaya Yajuyo afirgice idonsa cike da hawaye yace mekace Nace Fatimanka yace awajen hajiya murja Itace yar Autanta. HAJIYAR BUK PART 12 Sadik Fatimanka yace awajen hajiya murja Chakka yaja yatsaya yajuyo afirgice idanu cike da kwalla Yayan hajiya uku Biyu Maza suna dangin mahaifinsu wajen Baffansu tun bayan rasuwar abbansu Fatimace yar auta itace ke tare da Hajiya Murja Ka kwantar da hankalinka kazauna kafahimceni kasani nima wannan abu ba san raina yafaruba Allah ne yakaddara haka Sadik kasani bantabajin kaunar hajiya arainaba dai dai da kiftawar ido hajiya takansance cikin wani mawuyacin hali Allah ne yajarrabeta da soyayyata wanda dagani har ita bawanda yasan dalilin hakan hajiya tanasona soyayya ta gaskiya har cikin zuciyarta. Tanada burin aurena koda zata rasa dukkan abinda ta mallaka Hajiya batajin fidda kudi wajen hidimtamin tana kashemin konawa nabukata a yan kwanakinnan duk wanda yasanni inya dubeni yasan rayuwata tachanja ina kashe kudi yanda nakeso kayansawa kala kala tamkar dan wani hamshakin mai kudi agida antambayeni nace ninake siya da kudina kadancewar sunsan mai gidana hamshakin dankasuwane basu mamakin hakanba Sadik haryau har gobe babu wani dan uwana ko abokina dayasan muna tare da hajiya sai kai ina mai tabbatarmaka bazan taba iya auren hajiyaba sbd ina kallonta amatsayin mahaifiyata don babu abinda Mama tafita baxan iya auran sa'ar mamanaba wallahi Sadik baxan iyaba Kwalla taciko a idanuna Sadik dakansa yamatso inda nake yace nafahimci damuwarka abokina kada katashi hankalinka na yarda da kai abokina i trust in you. Sadik nayima alkawarin sada zuciyarka da masoyiyarka Fatima wannan shine dalilin kasancewata da hajiya murja nai ma alkawari dazarar ka mallaki Fatima nikuma zannesanta kaina da hajiya murja.HAJIYAR BUK PART 13 Yamma tayi misalin karfe 4:30 babu jama 'a sosai kasancewar garin da yanayin Sanyi Sanyi bishiyune rai rass sai kadawa suke suna rausaya yau Jami'ar bayero tamkar anyi yasa bakaji sautin komai sai kukan tsintsaye da ganyen bishiyu dake kadawa muna tafe nida abokina Sadik gidansu yusrah muka nufa mintina kadan suka sadamu da quaters din su yusrah kanin Yusrah Dake wasa aharabar gidan ne yafara hangomu da sauri yashiga ciki yan kiran antynsa ga ya Abba ga ya Abba cikin matsanin shauki yusrah na gaba salman na biye da ita mukai kicibus take Wani yanayin farinciki yalullube kyakykyawar fuskar yusrah tai ajjiyar zuciya tana murmushi muna hada idanu da ita Kwarjinina yabugi fuskarta take wata bakuwar kunya tai saukar gaggawa cikin xuciyarta nan takasa motsawa kanta kasa hankalinta yadawo jikinta bata kula da Sadik ba sai da yaiwa Salman magana tana kallonsa takoma ciki da gudu yanayin ni kaina yamatukar chanja lissafina take na basar nace Salman oyooyo ya gida ya mum yace mummy batanan nace ayya ina tatafi yace suntafi unguwa da Mubarakh nace to muje ciki Sadik yace Abokina Agaskiya Yusrah na cikin wani bakon yanayi wanda yakasa boyuwa daga xuciyarta har idanunta sukan makance bata ganin kowa agabanta bayan kai nace hmm sadik kenan ita gayama haka ai basai ta fadaba labarin zuciya.... Nan namanta da batun Sadik muka shiga daga ciki yusrah tasaukemu afalonsu taimana tarba cikin girmamawa munjima muna hira sadik na tare da kannen yusrah suna lesson Yusrah tace Yayanah Umma tabani sako wajenka nace to inajinki tai shiru da alamun amsar bata gamsar da itaba duk da na fahimci wani abun sai na basary yusrah tace ina waje batajira amsar dazan bataba tafice farfajiyar gidan tabarmu a falo nakalli inda sadim yake sai naga yana Natashi na fita ina zuwa naga yusrah zaune kan kujerar roba Woww bazan iya kwatanta yanda naga yusrah takara kyau da haskeba kwalliyar datai taimatakyau sosai kallonta nai muka hada ido Masha Allah Fatabarakallahu ahsanil khaliqin take naji wani sinadarin yaratsa kasan fatar kirjina yashige direct ma'adanar so da kauna kuzarina yakaru namanta da tinanin komai Yusrah kawai nake kallo agabana. Sannu yayanah fatan nasameka cikin koshin lfy dafatan kowa yana lfy nabata amsa cikin tausasa murya kowa yana lfy Yayana natambayekah kwanaki bakabani amsaba kuma yauma zan karamaka da wata tambayar yayah meyasa nake yawaita tinanika azuciyata ko amakaranta sai naji bana jindadin komai bana bukatar kowa illah inganka yayanah meyasa inkazo gidanmu sau daua sai adade sosai kake sake zuwa yayana meyasa kake zuwarmin amafarki yayanah kasan ni yarinyace karama kuma kanwarka wadda batasan komaiba meyasa innatambayeka kan abinda bansaniba baka bani amsa kuma na tabbata kai kasan komenene ke damuna Amma inna tambayeka baka bani amsa Take naji tausayin yusrah ya lullube zuciyata Yusrah yarinya karama batasan komai game da soyayyaba burin mahaifinta shine tai karatu mai zurfi Yusrah takatse tinanina da fadin Yayanah nakaranta wani novel yau domin insamo amsar abinda ke sanyani yawan tinaninka acikin labarin nasami amsar da zuciyata takasa ganomin ita Yayanah Menene So menene Soyayya don Allah kadaure kabani amsar tambayata. Take naji SO kuma? SOYAYYA wace irin Soyayya kuma??HAJIYAR BUK PART 14 yusrah ke tambayata yayinda idanunta yakada ya chanja kala nan take Shiru yabiyo bayan tambayarta na tsawon dakika 2 maganganun Yusrah tabbas gaskiyane amma sai dai ina fargabar halinda xata tsinci kanta aciki Lamarin SO ba abune kankaniba musamman ga Yarinya Karama yar makaranta wadda babanta baida burin yimata auren wuri Yusrah tabbas duk abinda kika fada gaskiyane SO halittane da Allah yahalicceshi azuciyar dukkan abin halitta mutum da aljan dabbobi da tsuntsaye So wani sinadarine dayake karama rayuwa armashi dajin dadi sannan wani matakine dake cefa rayuwar abin halitta ga abubuwa guda biyu Farin ciki da bakin ciki Idan Kakamu da son ya mace amatsayinka na da namiji wannan macen zatakasance agareka abar bukatuwarka kwatankwacin yanda kifi ke bukatar ruwa don gudanar da rayuwarsa zatakasace jindadinka farin ciki nutsuwa da walwala agareka dukkanin abinda Kasan kishiyane ga wadannan abubuwa to rashinta zaikasance kishiyar wadannan abubuwa zakazam cikin damuwa rashim nutsuwa bakin ciki tashin hankali wanda inyayi yawa zai iya zama illa ga ratuwar kowane mahaluki Dukkanin abinda zuciyarki takamu dashi nima nakamu dashi inasonki yusrah Soyayya ta gaskiya inajin sonki cikin dukkan sassan jikina musamman bargo da zuciyata aduk sanda muke tare farin ciki da jindadu ke yalwatuwa azuciyata aduk sanda bama tare bakin ciki damuwa da kunci nake tsintar kaina aciki na boye hakan sbd inabaki dama amatsayinki na daliba bansan kihada soyayya da karatu ina kishinki ina tausayamiki dukkanin abinda xai zam damuwa agareki bana fatan inkasance nine silar faruwarsa wannan yasani yanke shawawar kin bayyanawa agareki Yayanah kalamanka suna da matukar tasiri ga zuciyata sunshige kowane sakon zuciyana dawani sinadari wanda bansan yanayinsaba naimaka alkawarin komai wuya komai rintsin da zanshiga ardalilin soyayyarka bazan taba yin rauniba zaka sameni mai karfin guywa da juriya Soyayyarka ni nagani nadauka kuma zan killaceka kai kadai azuciyata dakai nafara dakai zankare adalilinka nafara sanin SO adalilin ka zan kasance cikin rayuwar farin ciki da jindadi Inasonka yayanah inakaunarka Har abada Yayanah yaya Abba Nabaka amanar xuciyata kai zakam mai yimin talafi kasani akan hanya ni bakuwace asoyayya wadda batasan komaiba Sai dai inason sani daga hamshakin masanin hakikanin sirrin SO da Kauna YayanahHAJIYAR BUK INTERMISSION Yusrah takashemin jiki da dadadan kalaman da tunda nake bantabajin kwatankwacin irinsuba dani daita muntsinci kanmu cikin rayuwar farin ciki da jindadi bamu rabuba harsai da mamanta tadawo muka gaisa sannan mukai sallama Yusrah tarakomu bakin garden ananma tamkar bazamu rabuba Allah sarki soyayya dadi idan kai dace da masoyin gaskiya Ahaka muka rabu muna kewar juna tunda wannan rana soyayyarmu tai karfi nida Yusrah kusan duk sati sai naje gidansu don muga juna Sai dai kullum zuciyana cike da fargabar kada Abbanta yasan da wannan lamari don nayi Imanin inyasani Lamarin bazai mana dadiba burinsa akan Yusrah tayi karatu tazam babbar Likita gashi Yusrah tafada tarkon Soyayya matsananciya Abangaren Hajiya Murja muwa kullum wutar soyayya dada ruruwa take azuciyarta koda yaushe bukatarta ta ganni muna tare da ita yauma dai kamar yanda tasaba ta matsamin inje muhadu niko ban amsa mataba yanda naji yanayinta tana magana awaya shiyatabbatarmin da cewa Soyayyar ta motsa mata nace mata ganinan zanzo da yamma tace to yau da wuri nakeso naje gidan hajiya indawo da wuri sabd anjima akwai kallon ball karfe 3pm ina gidan hajiya sai dai kash anyi rashin sa'a hajiya batanan Sallamata keda wuya Aka amsa da murya sassanya Fatimace tabudemin kofa tana ganina tahade rai fuska aturbeni tace menene Makalemata mekazoyi gidanmu yau hajiya batanan sai ka juya kakoma inda kafito ranta abace taci gaba da fadin wai wani kankanin yaro dakai kaizaka auri mamana ai wallahi danaji kunya da duniya tatsaneni ka auri mamana kana Sa'ana Ai wallahi duk yanda zanyi iya karfin ikona da Allah yabani bazaka auri Hajitaba Wallahi wallahi duk wata hanya dazanbi inga na bata wannan magana walh sai nabi sai dai adalilin haka inrasa numfashina Wallahi bana goyon bayan wannan kazamin al'amari kafice min daga gidan Ubana kakara gaba Sabon tashin hankali raina yabaci kalaman Fatima sun tsoratani matuka Fatima nada zuciya kuma duk abinda tafada zata iya aikatawa batada tsoro ko kankani Kafice nace maka wallahi ko indokama ihun barawo yanzu yanzunnan Cikine yayi sanyi Fatima nada zafin rai ga zuciya Allah sarki Sadik alkawarin dana daukarmaine tafadomin axuciya Anya xan iya shawo kan Fatima tasoshi kuwa duba da yanda nai bakinjini wajenta Azuciyar Fatima kaf duniya babu mahalukin data tsana kamar Abba besst San' auran mai neman auren mamanta Lamarin yasake dagulewa INTERMISSION An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 2 of 2