Reading TAKOBIN DAUKAKA Chapter 2 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

jama'a na zubewa kasa suna kwasar gaisuwa cikin girmamawa,


Lokacin da aka iso wani bangare mai ɗauke da manyan falo guda uku haɗe da kewayen wanka, kayan more rayuwa sai


Waɗansu tsala-tsalan kuyangi na kai komo a cikin turakar,


Da sauri wata dattijuwar mata mai kimanin shekaru hamsin ta rugo izuwa inda sarauniyar lasmirat take ta zube ƙasa bisa gwiwoyin ta ta kwashi gaisuwa


Bakin ta na kyarma kuma kanta a sunkuye tace "me kike da buƙata ya shugaba ta?


Lasmirat ta dube ta tace" yake zarima kiyi sani cewa bakomai nake da bukata ba face ina so wannan baƙo dake tare da ni a basa kulawa da dukkanin wani abu da ya buƙata kiyi sani cewa yana da matukar muhimmanci agareni


Koda jin wannan batu sai zarima ta sake risina wa tace angama ya shugabata bin umarnin ki ai shi ne ibada ta,


Tana gama faɗin hakan ta mike tsaye tana Mai yiwa saurayi yaslir nuni da ya biyo bayan ta


Batare da bata lokaci ba yaslir ya kama linzamin dokin sa ya sauko sannan ya rufa mata baya


Amma koda ya waiga ya haɗa idanu da sarauniya lasmirat sai yaga tana yi masa wani mayataccen kallo mai ɗauke da alamar tambaya.


Cikin hanzari sarauniya lasmirat ta juya taɗa linzamin dokin ta ta nufi bangaren da turakar ta take,


Lokacin da isa sai ta shiga izuwa kewaye ta tsala wanka sannan ta shiga tsaɓa ado tana mai fuskantar wani madubi


Tana cikin wannan hali ne sai ta jiyo motsin tafiya a bayan ta


Koda ta waiga sai tayi arba da shi ba wani bane face wazirin ta mai suna ukashat


Waziri ukashat yakasance dattijo mai yawan shekaru amma duk da hakan babu gajiya a tare da jikin sa,


Yana da kaurin jiki, dogo ne tsaka-tsaki,yana da tarin gemu da ƙasumba fararen sol,


Fuskar sa tana da kwarjini


Ukashat yakasance ɗan uwa a wajen mahaifin lasmirat wato sarki kazmal kuma babban aminin sa, bisa wannan dalili ne yasanya duk abinda lasmirat zata zartar sai ta nemi shawarar waziri ukashat,


Bisa al'ada duk sa'adda waziri ukashat zai gana da sarauniya lasmirat yana sanya ayi masa iso,kuma zai shigo ne fuskar sa cike da annuri


Amma a wannan karon sai ga fuskar sa a murtke babu annuri tamkar an aiko masa da saƙon mutuwa,


Kawai sai ya zaune a bisa wata kujera dake fuskantar lasmirat ya dube ta cikin tsananin fushi yace" yake lasmirat shin menene yasanaya za ki karrama wanda ya wulakanta ki a gaban talakawa?.


Tabbas hakan zubar da darajar wannan masarauta ta mu ne da muka gada tun iyaye da kakanni,


Shin yanzu da wane irin idanu zamu kalli sauran sarakuna abokan gabar mu?


Wai shin ma bakya tunanin cewa wannan saurayi ɗaya daga cikin abokan gaba ne yayi ɓadda kama domin ya yaudare ki?


Koda jin wannan tambaya daga bakin waziri ukashat sai sarauniya lasmirat ta dube sa a nutse tace"yakai waziri kayi sani cewa ko kaɗan bana taɓa da nasanin karrama wannan saurayi kuma jiki na ya bani cewa tabbas bazai cutar da Ni ba, hakika zai zamo mai amfani a gare ni.


Ukashat ya katse ta ta hanyar ɗaga mata hannu yace " Haƙiƙa ke yarinya ce, tabbatas Abin da Babba ya hango yaro ko ya taka tsani bazai iya gani ba.


Ban yi mamakin maganar ki domin na fahimci cewa tsananin kauna da soyayyar wannan saurayi ce ta makantar da idanuwan ki, ta sanya har kika manta da burin zuri'armu na kare martabar wannan masarauta,


Koda wannan batu daga bakin ukashat sai sarauniya lasmirat ta fusata ainun ta dakawa matsawa ta dube sa tace" yakai ukashat kayi sani cewa ni nake da ikon bayar da umarni a wannan masarauta don haka abin da naga ya dace shi zan aiwatar,


Tana gama faɗin hakan sai ta miƙe tsaye ta fice daga cikin turkar ta bar waziri ukashat a zaune


Cikin alamun tsantsar damuwa waziri ya mike tsaye ya fice daga turakar zuciyar sa cike da takaici.


Da shigar saurayi yaslir izuwa cikin turakar, sai ya tarar turakar takasan ce ƙasaitacciya da aka ƙawata ta da nau'ikan kayan ƙawa da alatun jin jin daɗin rayuwar duniya.


Gaba ɗaya turakar shimfiɗe take da wani koren kilishi mai taushin gaske,


Bayan yaslir ya fito daga kewayen wanka wani wanzami yayi masa gyaran fuska da saje, sai wata kuyanga ta kawo masa waɗansu fararen tufafi masu taushi ya sanya a jikin sa,


Nan take tsakanin kyawun sa ya fito fili ƙarara, kawai sai ya nufi teburin da aka tanadar masa abinci da abin sha ya shiga kimtsa cikin sa,






Bayan ya kammala ne da yake a wannan lokaci duhun dare ya fara Kawo kai,


Sai ya kunna fitulun dake turakar ta kaure da haske,


Sannnan ya zauna a bisa kan gadon sa kuma ya zurfafa izuwa kogin tunani,


Yana cikin haka ne sai yaji an turo kofar shigowa turakar


Ai kuwa kofar na buɗewa sai ya yi arba da ita ba wata ba ce face sarauniya lasmirat ta caɓa ado wani irin daddaɗan ƙamshi na tashi daga jikin ta.


Cikin Wata irin tafiya mai ɗaukar hankalin duk wani ɗa namiji,ta nufi wata ƙasaitacciyar kujera dake fuskantar yaslir ta zauna a kan ta,


Cikin annurin fuska ta dubi yaslir tace"yakai yaslir kafin mu kai ga tattaunawa abinda ya taramu anan Yana da kyau ka sanar dani labarin rayuwar ka.


Koda jin wannan tambaya sai idanun yaslir su ka ciki da kwalla ya dubi lasmirat yace" ya sarauniyar kyawu shin ina dalilin son kiji labarin rayuwa ta?


Lasmirat ta numfasa tace"Domin sanin labarin ka ya na da matukar muhimmanci a gareni,


Yaslir ya yi gyaran murya a karo na biyu sannan yafara dacewa






***




































Kimanin shekaru arba'in baya anyi wani ƙauye da ake kira da suna Darul-Na'am.


Gari ne mai ɗauke da arzikin noma, kiwo, Sarkin dake mulkin kauyen yakasance adali mai tausayin talakawa


Ana kiransa da suna Abu-salimat, Abu-salimat yakasance GWARZON MAYAKI mai tarwatsa maza a filin daga,


Yana da ƴa guda ɗaya kyakkyawa tagaban kwatance ana kiran ta suna salimat ta gaji mahaifin ta a kyawawan halayen mahaifin ta.


Ƙauyen Darul-Na'am na karkashin mulkin wata babbar masarauta da wani kasaitaccen sarki ke mulki mai suna Husnalu ibn kailub,


Sarki Husnalu yakasance GWARZON MATSAFI, kuma mashahurin mayaki, daɗin daɗawa kuma yakasance AZZALUMI nagaban kwatance,


Ƙwace,kashe rayukan al'umma,tare da farauce dukiyoyin su ba a bakin komai yake a wajen sa ba,


A rayuwar sarki Husnalu babu abin da yake tsananin kauna fiye da ɗansa guda ɗaya mai suna Hatmal,


Yarima Hatmal yakasance ɗan lele a wajen sarki Husnalu baya son ɓacin ransa ko kaɗan,


Bisa al'adar Sarki Husnalu duk bayan shekara ɗaya sarakunan dake ƙarƙashin ikon sa kan biya sa haraji na dukiya da adadin ta yakai dinare dubu ɗari tara, gami da kayan amfanin gona da dabbobin ni'ima


Tsakani na da gimbiya salimat akwai soyayya mai karfi, kasancewar mahaifina shi ne wazirin mahaifin ta,tun muna yara ƙanana muke kaunar juna.






****


Wata rana daga cikin ranakun da sarakunan ke kaiwa sarki Husnalu haraji, kamar yadda aka saba duk shekara,


Sai yazamana cewa a wannan shekara anyi tafiyar tare da ni da masoyayi ta gimbiya salimat,


Bayan dukkanin sarakunan sun kammala hallara a fada,


Bayan shiru da ya mamaye fadar na ɗan wani lokaci sai aka hango sarki Husnalu da yarima Hatmal sun shigo fadar, suna sanye cikin suturu iri ɗaya hatta takalmin dake kafar su iri ɗaya ne,


Koda jama'a suka hango sarki sai suka miƙe tsaye domin girmama a gare su,


Kai tsaye sarki Husnalu da yarima Hatmal suka huce izuwa inda karagar mulki take suka zauna a tare,






Sannan sauran jama'a suka zauna, batare da bata lokaci ba sarakunan suka dunga tashi daga wajen zaman su suna zuwa gaban na Husnalu suka kwasar gaisuwa sannan su gabatar da harajin su da jama'ar da suka yi musu rakiya






Sarki na farko da ya gabatar da harajin da ana kiransa da suna zulaibu, yana mulkin wani ɗan ƙaramin gari mai suna madinatul-shaswal,






A gaba ɗaya sarakunan da suka hallara a fadar babu wanda yakai zulaibu yawan shekaru da kuma dadewa akan karagar mulki,






Sai da sarakuna biyar suka gabatar da harajin sannan aka iso kan sarki Abu-salimat,






Abu-salimat ya mike tsaye ni da gimbiya salimat muka mara masa baya, dakaru na biye da mu ɗauke da akwatin dinare gami da kayan amfanin gona, har mu ka isa inda karagar mulki take, muka zube ƙasa muka kwashi gaisuwa muna masu sunkuyar da kawunan mu.






Kawai sai waɗansu dakaru daban a fadar suka karɓi wadannan akwatin dinare suka lissafa kuma suka bincike kayan gonar suka tabbatar da ingancin su sannan suka ɗauke suka fice daga fadar,






Ana cikin wannan hali ne na ɗan saci kallon yarima Hatmal ai kuwa sai na ga ya ƙurawa gimbiya salimat idanu yana mai yi mata wani irin kallo daya sanya hantar ciki na ya kaɗa, Ku ma tsoro ya kamani.






Domin kallon da naga Yarima Hatmal na yi mita kallo ne ma nuna kamuwa da soyayya.






Jikina a ssnyaye na mayar da kai na kasa, sannan sarki Husnalu ya Umarce mu da mu fice daga fadar,






Cikin hanzar sarki sarki Abu-salimat ya miƙe tsaye muka rufa masa baya muka fice daga fadar


Fitowar mu keda wuya sai muka fara shirye-shiryen komawa izuwa ƙauyen Darul-Na'am






Bayan an kammala ne muka hau bisa dawakan mu muka fice daga kasar Baitul-sharhal muka nufi hanyar da zata sadamu da ƙauyen Darul-Na'am,






A wannan lokaci sarki Abu-salimat ne akan gaba tare da wani hadimin sa mai suna Haimar suna hirarrakin su cikin nishadi,






Ni da salimat muna hira irin ta masoya, ana cikin wannan hali ne gimbiya salimat ta dube ni tace"ya masoyi na kuma hasken rayuwa ta shin nayi maka wata tambaya mana






Cikin annurin fuska nace faɗi tambayar ki ya abar kauna ta






Salimat tayi ajiyar zuciya ta ce " shin a halin yanzu yaya matsayin soyayya ta yake a zuciyar ka?






Koda jin wannan tambaya sai na tuntsire da dariya na dubi lasmirat nace " shin kina kina tantama ne akan matsayin ki a rai na ko kuea.






A,a kawai ina so naji matsayi na ne






Salimat ta faɗa fuskar ta cike da annuri,.






Murmushi nayi a karo na biyu nace" Ai matsayin ki a waje na tamkar hanta da jini ne domin babu abin da zai raba tsakanin mu face mutuwa,






Salimat tayi murmushin jin daɗi tace " Ni kuwa ka zame mini tamkar numfashi a rayuwa ta,






Nan take mu duka biyun muka fashe da dariyar farin ciki






Ana cikin wannan hali ne muka jiyo alamun takun sawaye a bayan mu,






Cikin firgici muka ja linzamin dawakan mu muka tsaya koda muka wai ga sai muka yi arba da waɗansu ZARATAN DAKARU masu matukar yawa






Shirye cikin gagarumar shigar yaƙi mai matukar kwarjini daban tsoro,






Har mun yunkura zamu zare takubban mu sai sarki Abu-salimat yayi mana nuni da mu dakata






Bisa lura da yayi cewa basu bane dakarun face na sarki Husnalu






Sannu a hankali dakarun suka iso har izuwa inda muke suka yiwa dawakan su Turkiya,


Sarki Abu-salimat ya dubi wani garjejen kato mai kirar samudawan farko wanda da alama shine shugaban dakarun yace dasshi" yakai muraizu shin wane saƙo kuke tafe dashi izuwa gare mu ina fatan dai bamu saɓawa mai girma Husnalu ba,


Sadauki muraizu ya bushe da dariyar mugunta mai kama da kukan jaki daga bisani ya murtuke fuska tamkar an masa da saƙon mutuwa,


Cikin Wata irin kakkausar murya yace" ya kai Abu-salimat kayi sani cewa bakomai ne ke tafe da mu ba sai domin ka bamu yar ka salimat mu Kaita izuwa ga sarki saboda ɗan sa Yarima Hatmal ya kamu da soyayyar ta kuma yana so ne ya aure ta


Cikin matukar kaduwa Abu-salimat ya dubi muraizu a lokacin da idanun sa suka zazzaro yace" shin wace irin maganar banza kake yi yakai muraizu anya kuwa a cikin hankalin ka kake kuwa?


Muraizu ya bushe da dariyar mugunta har ya kusa faɗowa daga kan dokin sa daga bisani ya haɗe rai yace"Tabbas garau nake nasan Abin da nake faɗa ina cikin hayyacina,


A halin yanzu ba neman shawarar ka muke yi ba face zartar da umarnin mai girma Husnalu,


Koda jin wannan batu daga bakin muraizu sai na fusata ainun ya dakamasa tsawa cikin matukar fushi na dube nace " karyar ka tasha karya yakai wannan la'ananne kuma BAKIN AZZALUMI kayi sani cewa karyarka tasha karya baza mu taɓa lamunta da wannan magana taka ba,


Kafin na gama rufe bakina sadauki muraizu ya fusata ainun ya zaro kibbau guda biyar a gadon bayan sa ya ya saka a cikin bakan sa yaja ya ɗame cikin wani irin zafin nama ya harba kibban


Kafin ɗaya daga cikin mu yayi wani yunkuri kibiyoyin guda biyar sun sauka a kan waɗansu jama'ar mu mutum biyar sun faɗi kasa matattu






Mutum biyar ɗin sun kasance dattijawa kuma manyan yan majalisar sarki da muke matukar alfahari dasu a cikin ƙauyen Darul-Na'am


Koda sarki Abu-salimat yayi arba da gawarwakin yan majalisar tasa sai hawayen takaici da bakin ciki suka zubo masa,


**


Lokacin da saurayi yaslir yazo daidai nan a labarin sa sai hawaye suka zubo daga idanun sa,


Al'amarin da ya sanya sarauniya lasmirat ta kamu da matukar tausayin sa kenan.


Har ta buɗi baki da nufin tace wani abu sai kawai suka ga sararin samaniya yayi dubu dunɗim!


Cikin matukar firgici lasmirat da saurayi yaslir suka ruga mike tsaye zumbur suka ruga izuwa wajen turakar, suna fita suka ci karo da Sarkin yaƙi,


Sarkin yaki ya dubesu cikin tashin hankali yace " ya shugabata muna cikin gudanar da ayyukan mu na tsaron kofa kawai sai mu kayi arba da wata gibgegiyar halitta mai matukar muni daban tsoro tana ta hallaka mutane,


Ya shugabata na rantse da karfin mulkin ki babu wata halitta da zata tsira da ga sharrin halittar,


Kafin Sarkin yaki yagama rufe bakin sa sarauniya lasmirat ta tari numfashin sa tace" A yi maza aje a busa ƙahon yaƙi,


Batare da lasmirat ta jira Sarkin yaƙi ya furta wani abu ba ta shige gaba yaslir ya mara mata baya yana mai dogare da sandar sa,


A can cikin gari kuwa halittar ta wanzu tana ta hallaka mutane jama'a suna ta guje-guje da ifice-ifice domin tsira da rayukansu,


Duk inda halittar ta sanya a gaba sai dai kaga gawarwakin jama'a birjik kwance a ƙasa cikin jini,


A wasu lokutan ma sai kaga halittar ta sanya hannun ta ta yaye rufin ɗaki ta ɗauko mutum ya na ihu ta sanya a bakin ta ta laƙume tayi loma ɗaya dashi,


Ana cikin wannan hali ne sai aka hango sarauniya lasmirat da saurayi sun rugo wajen a bisa dawakai cikin gagarumar shigar yaƙi suka tsaya cak,


Kawai sai lasmirat ta dakawa halittar tsawa,


Koda halittar taji an dakama tsawa sai ta tsaya cak a waje guda ƙurawa su lasmirat idanu tana mai nazarin su,






Ita dai wannan halitta takasance,shirgegiyar aljani mai matukar tsawo,muni,gami da ban tsoro,






Babu wata halitta da zata yi arba da wannan aljanar face firgici, Saboda matukar munin ta






Duk irin dakewar zuciya irin ta lasmirat da saurayi yaslir sai da tsoro ya ɗarsu a zukatan su,






Dakarun dake bayan su kuwa sai jikin su yakama kyarma yana tsuma tamakar ace kyat su cika wandon su da iska saboda tsananin tsoro,






Sai da aka shafe tsawon dakika talatin a cikin wannan hali ana kallon kallo






Daga can sai aljanar ta bushe da dariyar wanda ta haddasa girgizar kasa,






Nan fa bishiyoyi suka dunga karairayewa suna zube ƙasa, gida je su ka dunga rushewa suna hallaka, ƙasa tana tsagewa dawakai da mahayan su suna rufta wa cikin ta,






Ihun mazaje,mata, tsofaffi gami da yara ya cika dodon kunne,






Sa,adda sarauniya lasmirat taga yadda jama'ar ta ke hallaka sai ta cika da tsananin baƙin ciki maral musaltuwa,






Cikin fushi ta sake dakwa aljanar tsawa a karo na biyu tana mai cewa "yake wannan shu'umar aljana yau duhun ta cika idan har kin isa ki fito muyi fito-na fito na rantse da karagar mulki na sai na ga bayan ki,






Koda jin wannan batu sai aljanar ta tsuke bakin ta komai ya samu dai dai tuwa bishiyoyi suka daina karyewa duwatsu suka daina fashewa kasa ta dai na tsagewa,






Aljanar ta buɗe bakin ta wanda yafi kama da kofar gari cikin murya mai ban tsoro tamkar saukar aradu tace"yake wannan sarauniya kayi sani cewa bakomai ne ya kawo wannan birni naki ba sai domin ya kashe mutanen birnin ki kuma na mallake ki saboda wata muhimmiyar buƙata ta,






Kafin aljanar ta gama rufe bakin ta saurayi yaslir ya tari numfashin ta yana mai daka mata tsawa cikin fushi yace"yake rafkananniyar aljana kuma yar tsakuwa a cikin jerin JARUMAN DUNIYA, kiyi sani cewa karyar ki tasha karya ina mai tabbatar miki dacewa bazaki tsira daga sharrin mu ba,






Sai ki shirya ka maza nan bisa kanki,






Yana gama faɗin hakan ya sakarwa dokin sa linzami yana mai gyara rikon sandar sa cikin hanzari lasmirat ta mara masa baya tana mai ɗaga takobin ta sama,






Sauran dakaru mutum dubu arba'in sukayi koyi dasu






Ana haɗuwa aka kacame da azababban yaƙi mai matukar tayar da hankali






Domin kafin a haɗu sai da aljanar ta sanya hannu ta ta ɗebi dakaru mutum hamsin har da dawakan su ta watsa a bakin ta ta taunesu tayi kalaci dasu,






Sannan ta afkawa su lasmirat.






Lokacin da aka kacame da azababban yaƙi tsakanin shu'umar aljana da su sarauniya lasmirat,






Sai lasmirat da yaslir suka wanzu suna kaiwa aljanar sara da suka cikin tsananin zafin nama JURIYA DA BAJINTA






Duk sa'adda makaman su suka sauka a jikin aljanar sai kaji sun bada kara ƙal ƙal !! Tamakar karfe suka sara






In banda lasmirat da yaslir suna cikin kariyar tsafi da tuni sun hallaka,






Idan aljanar ta kaiwa yaslir da lasmirat hari da hannayen ta, idan suka goce duk abin da hannun ta ya sauka akai sai dai kaga ya tarwatse,idan kuwa a ƙasa ne sai ya haddasa wani rami zurfin gaske,






Take dakaru da dawakan su zasu afka cikin sa suna ihu da kururuwar neman taimako,






Nan fa waje ya cika da ihun mazaje mata da yara da matasa,






Karafniyar ƙarafa ta cika dodon kunne, JINI DA KASA suka cakuɗu, ƙura ta turnuƙe sararin samaniya,






Lokacin da aka shafe dakika ɗari biyu da sittin ana wannan bakin gumurzu,






Sai ya zama na cewa aljanar ta samu nasarar hallaka dakaru Fiye da dubu shida,






Amma bata samu nasarar koda lakutar jikin su lasmirat ba sai ta cika da matukar mamaki kuma ta fusata ainun,






Abin da ya bata mamaki shi ne ya akayi sarauniya lasmirat da saurayi yaslir suka kasance masu tsananin zafin nama, tabbas yau ta haɗu da takadiran jarumai, hakika rashin wannan nasara ƙasanta darajar ta ne da kimar ta,






Koda tazo nan a tunanin ta sai kawai ta canza salon faɗan ta yazamana cewa tana haɗa kai bugu da naushin hannu da ƙafa,






Ai kuwa nan take labari yasha Bambam, domin a halin yanzu daƙyar su yaslir ke iya mayar da martani






Idan ta daki gini ya tarwatse sai kaga duwatsun sun yiwa su lasmirat lugudan duka,






Sai da aka shafe tsawon dakika dari da ɗoriya ana wannan fafatawa,






Ana cikin wannan yaƙi ne aljanar ta kaiwa sarauniya lasmirat da yaslir wawan naushi da nufin yi musu farat ɗaya,






Amma kafin hannun ta yakai gare su sai suka daka tsalle a sama tamkar an harbosu daga cikin baka suka bar kan dawakan su






Sai gashi hannun ya sauka akan dawakan sun tarwatse tamakar an talitse tumatir,






A daidai wannan lokaci ne yaslir da lasmirat suka sauka akan aljanar bisa tsakiyar kanta su shiga kafta mata sara babu sassauci,






Nan fa yazamana sun riki ta aljanar yazamana cewa ta daina kaiwa dakaru hari






Sai dai ƙoƙarin taga ta jefo su yaslir daga kan ta, ana cikin wannan hali ne aljanar ta samu nasarar damƙo su yaslir ta hannun ta ta matse su nan take suka sume sakamakon maƙurewar,






Ashe ta samu nasarar karya ɗan yatsan yaslir, lasmirat kuma ta samu gocewar ƙashi, a hannun ta,






Koda samun wannan gagarumar nasara sai aljanar ta bushe da shu'umar dariya






Sai da tayi dariyar ta ishe ta sannan ta tsuke bakin ta kawai sai ta juya ta nufi kofar fita daga birnin tana mai koɗa kanta gami da yiwa kanta kirari, tana mai cewa






" Saini GAWURTACCIYA uwar hatsabibai,






GUGUWAR YAƘI nake mai share MAYAKA,






ANNOBA ƊARI nake duk wanda ya Kusan ceni zai baƙun ci barzahu,






Ni ne gararriya uwar gagararru,














Haka ta cigaba da yiwa kanta kirarin tana lafiya a cikin birnin,






Duk sa'adda ta ajiye kafarta ɗaya sai dai kaga ƙasa tana girgiza tamkar zata tsage abin da ke saman ta ya faɗa cikin ta






Koda sauran dakarun suka ga abin da yafaru sai suka dunga ɗame kwari da bakan su suna Harbin aljanar






Duk tsananin yawan kibban sai yazamana a banza domin ko gezau batayi ba






Sai dai ma kaga ta sanya hannun ta ɗaya tana karkaɗe kibiyoyin kamar tana kaɗe ganyayyakin bishiya,






Kwatsam bazato babu tsammani sai aka ji aljanar ta kurma wawan ihu kuma ta faɗi ƙasa tim,






Ta saki su sarauniya lasmirat suka faɗo ƙasa babu alamun rai a tare dasu ,






Kuma akaga aljanar ta ɗaga hannayen ta sama tana mai roƙon gafara






Al'amarin da yayi matukar bawa dakarun mamaki kenan, suka rugo izuwa wajen domin su ga abin da ke wakana,






Su na isowa sai suka ja linzamin dawakan su suka yi turjiya,






Ai kuwa sai su kayi arba da wata kyakkyawar budurwa,






Budurwur takasance dogowa mai matsakaicin kaurin jiki, cikin ta ashafe yake tamkar bata cin komai ba,






Kuma a tsuke yake daga ƙasa, ƙugunta mai faɗi ne yayi tudu sosai, gashin kanta mai tsawo ne ya zuba har izuwa kan kafaɗun ta baƙi ne siɗik tamakar gilashi, a jikin ta tana sanye da tufafi irin na mutanen birnin sun, kanta daure da bakin rawani idanun ta kaɗai ake gani,






A sannanne dakarun suka fahimci cewa wannan bakuwar budurwa ce ta ceci rayuwar su sarauniya lasmirat,






Bakuwar budurwar ta nuna aljanar da ɗan yatsan ta na hagu take aljanar ta ƙame, tamakar gunki, komai na jikin ta ya daina motsi,






Faruwar hakan keda wuya sai budurwur ta taka da ƙafafuwan ta izuwa inda su yaslir ke kwance,






Kawai sai ta buɗe bakin ta ta karanto waɗansu kalamai da ita kaɗai tasan me take faɗa,






Tana gama rufe bakin ta sai aka ga sarauniya lasmirat da saurayi yaslir sun mike tsaye zumbur tamakar babu wani abu da ya same su.






Kafin wani daga cikin su yace uffan, budurwar ta sake nuna aljanar a karo na biyu da ɗan yatsan ta,take ruhin aljanar ya dawo jikin ta, komai nata yana yin motsi,






Budurwur ta buɗi baki cikin wata irin zazzakar murya tamkar ana busa sarewa tace" yake wannan AZZALUMA kiyi sani cewa na yarda zan barki Lafiya kici gaba da rayuwa amma bisa sharaɗin cewa za ki dai na zaluntar al'umma,






Cikin ladabi da ƙan-ƙan da kai aljanar tace Muryar ta na rawa saboda tsoro" Na amince ya shugabata na ɗaukar miki alkawarin cewa bazan kara cutar da wata halitta har abada,






Koda jin wannan batu sai budurwur tayi wa aljanar nuni da ta tafi,






Cikin hanzari aljanar ta miƙe tsaye ta buɗe manyan fuka-fukan ta tashi zuwa sararin samaniya tana mai keta gajimare cikin tsananin gudu keta Sa'a ta ɓace,






Nan fa gaba ɗaya jama'ar dake wajen suka cika da matukar mamaki maral musaltuwa,






Abu na farko da ya basu mamaki shi ne yadda ta ceto rayuwar su sarauniya lasmirat kuma suka warke sumul,






Abin da yafi basu mamaki kuma ya ɗaure musu kai shi ne yadda bakuwar budurwar take sarrafa aljanar tamakar tana juya waina (masa) a tanda,






A ɓangaren sarauniya lasmirat kuwa, mamaki ne ya cika zuciyar ta ta kasa cewa uffan,






Yaslir kuwa yafi kowa mamaki domin ko a mafarki bai taba ganin ya mace mai baiwar sarrafa irin wadannan aljanu ba,


Kawai sai ya ƙurawa budurwur idanu yana nazarin ta, duk da kasancewar fuskar budurwur na rufe da rawani amma idanun ta kaɗai yaslir ya kalla ya fahimci cewa ta nunka sarauniya lasmirat a kyawun sura,






Lasmirat da yaslir suka taka da ƙafafuwan su izuwa inda budurwur take tsaye, suka risina da kawunan su kasa domin girmama wa agare ta,






Sannan lasmirat ta ta dube ta cikin murmushi mai taushi tace"yake wannan basadaukiya mace mai kamar maza shin mene ne labarin ki?






Menene kuma dalilin da ya sanya kika ceci rayuwar mu ni da jama'ar birni na?.






Koda jin waɗannan tambayoyi sai budurwur tayi shiru tana mai nazari,






Daga can sai ta ɗago da kanta ta dubi yaslir, lasmirat tace cikin tattausar murya






" Da farko dai suna na Sunaila na fito daga cikin wata nahiya da ake yiwa da Haurul-zamras,






Abin da ya baro dani daga birnin mu shi ne domin na sadu da waɗansu irin mutane da ake yiwa laƙabi

Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6

Please Login or Register in order to submit comment