Reading Bad Boys by Oum-Aphnan Chapter 3 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

barshi zan
biya duka ,amma Plz naji point of error a maganar ka , fada mun gaskiya baka ƙuntata ma Saleemart?

Naji kana cewa ka koya mata tattali ,anya baka lalata fine cutie pie ba kuwa? Kasan dai yanda mu
abokanka muka dinga santin Saleemart ,bro bari in Fada maka gaskiya da ace na kyalla ido akan salimart
Kafin auren ku ,wlh sai na ƙwace maka ita”
Wani malolon kishi ne ya taso ma Sheikh abinda bai taɓa ji akan Salima ba tun bayan auren su sai
yau ,nan take idonsa suka kada zuwa jaaaa.



“To Rashid ko zan saketa ne ko aureta kawai?”



“Hehehhee ,Meye yayi zafi miqdad,? Gsky nike fada maka,ynz ga tambaya yaushe rabon da ka fita da
salimart outing irin yanda zakaga maza na fita da kyawawan matansu a gaban mota matsayin ƙawar su?”



“To ko shekaranjiya mun fita”



“Zuwa ina?”



“Munje kasuwa mana ,mun siyo kayan cefanen gida”



“Hmm just imagine,bafa cewa chilling kuka fita ba,irin kace babes Shirya muje musha ice cream din
na ,come on ,kana fa da wayewan nan kudi kuma akwaisu ,kaji dalilin da yasa nace in baka so ka sallama
abarmu mu shigo filin mu ririta Rose🌹”



Sheikh yanda kasan ƙaramin yaro haka ya zama ,abunka da bai taɓa samun wanda ya nuna masa zalama
ido biyu ba ,kuma yasan halin Rashid ba karamin ɗan duniya bane ba ,ya kwallafa rai akan mace ko ba
aure sai ya nemeta .

Jikinsa na bari ya daga waya ya fara kiran Salimart .



Dammm! Ƙirjin Salima ya buga ganin kiran ya Sheikh daidai ta rufo ƙofar falon ta dawo ,gode ma Allah ta
shigayi a ranta da ta sallami Dr kafin nan.



“Assalamu Alaika ya zaujiy”(Mijina)
“Waalaikis Salam ya ustaziya ,kina jina”



“Eh ya sheikh”



“Yau Inason kici ado nan da sa'o'i biyu ina dawowa zamu fita shaƙatawa”



Ras gaban Sayyada ya ɓaci ,out of joy ta daka tsalle tace da gaske kake Habibiy?”



“Kwarai kuwa ustaziya zamuje musha Ice cream muci ɗan pizza ko ya kikace,ɗan flexing din nan dai
kema ki fita gari ayi dake”



“Umuuuuh😘 Ina sonka mijina ” ta manna ma wayar kiss ta kashe da sauri ta yi cilli da wayar akan kujera
ta haura sama da gudu zuwa sashen ta.



Ya Sheikh waigawa yayi ya kalli Rashid cikin Murmushi

“Mata wato sudai mata'ul hayat ne(Ƙyale_ƙyalen rayuwa) sudai a kashe kudi a ji daɗi,yanzu zo kaga
farinciki da murna”



Rashid lumshe ido yayi yana kora drinks din hannunsa yana sanyaya maƙoshi

“I can perceive bros”




***

“Salima

Salimaaaaa

Wai kina Ina ne?”
Ya shigo gidan hannunsa rike da Car key .



A ruɗe tace “Na'am ya Sheikh Ahlan wa sahlan”(welcome)



Sannan ta fito daga ɗakin tana biyo stairs din da takalminta mai tsini yana ƙara cakas! Cakas! Cakas!



Ya Sheikh Binta da kallo yayi ,kawai sai yayi zumbur ya mike



Ta saka wani dandatsatsen less an mata ɗinkin bubu ya fita sosai ya zauna ɗas a jikinta ta murza daurin
turban gingiringin ta sagalo mayafi a kafada hannunta daure da wrist watch da zobentana gwal daya
hannun na azurfa sai ƙamshi take zubawa.



“Salima meye hakan kenan?” cak taja ta tsaya ba tare da ta gangaro ba ,sai bin jikinta da ya nuna da
yatsa take da kallo,tana neman abinda yayi aibu a jikinta



“Salima wannan ba shine leshin da Anty uwani ta kawo maki tsaraba daga cotonou ba?”



“Eh shine mana ya sheikh” tafa hannu ya shigayi yana salati



“Hazbinallahu waniimal wakil ,yanzu Ke Salima ɗingurugum leshin nan kika bada aka tsiyata da wannan
ɗinkin? Ji leɓatu kotaina suna reto a iska ,meye amfanin dinkin nan kenan? Kinsan tsadan leshin nan
kuwa? Da aka tsiyata leshin da gown kwara ɗaya jal!!!”



Marairaice murya tayi a shagwaɓe tace

“Ni Ina son style din ne”
Dafe goshi yayi



“Ohwuuuuu,Salima meyasa bazaki zama irina ba, Leshin da za ayi kaya uku dashi anyi daya.....ya salam

Ya kamatane kisa tela ya maki dinkin yadi hudu doguwar riga,sai kuma ki siya wani yadin ko satin ne dai
ayi maki combination dinki a maki ko riga da siket ,ba sun zama dinki biyu ba kenan?”



Langaɓe kai tayi ta ɗaura hannu a ƙarfen benen ta masa shiru



“Yanzu dai nawa aka maki ɗinkin nan?”



“kyauta kawata tayi mun”




“Ehennn kinji maganar nan,ta cuce ki! Ni dama nasan ɗan jikinki bazakici 6yards ba ,ta maki wayo kamar
anci ƙyalle a ɗinkin ta kwashe sauran yadin....kiyi amfani da hankali salima ” ya nuna gefen kansa
kamar wani super professor



Caɓe fuska tayi duk ya sattar mata da gwuiwa



“Shikenan bari inje in sauya kayan ”



“Ke😳Tare nike da Ambassador ,sai kuma ki sake ɓata wani lokacin,kiyi amfani da hankali salima ” ya
sake nuna mata gefen kansa 😄



“To shknn muje ,za'a kiyaye gaba”
Oum Aphnan

09065990265

*_🐹BAD BOYS🐹_*

By...

Oum Aphnan



007

___________________

“Knock knock knock”



Daga can upstairs taji ana knocking a entrance door ɗin parlourn ta ,wannan ya sata fitowa da sauri tana
faɗin “Ana zuwa”



Sanye take da bugujejen jallabiyar Ya Sheikh sai hulan wanka a kanta da falkata falkatan silipas ɗin da
take sakawa a ɗaki.



Murza key ɗin ƙofar tayi ta buɗe ƙofar ,cak ta ja ta tsaya ganin very tall handsome man a tsaye ,
kyakyawar gaske cikin ƙananun kaya ,fuskarsa kewaye da ƙasumba ya ɗan ajiye tumbin kuɗi cif cif a riga



Yana ganin ta buɗe ya saki fara'a har jajayen leɓensa da suka haskaka brown ɗin fatarsa suka sake
bayyana.
“Hajiya Barkanmu da rana” yanda yayi maganar a rarrabe ya bata dariya ta lura baida Hausa sosai



“Masa'al khair” Adnan Yana jin ta iya larabci yaji kamar ta taindimashi a Aljannah ,ji yayi kamar ya
kamata ya rungume



“Masha'allh A adkhul?”(In shigo)



Yanda ya ruɗe sai kawai Sayyada ta tsinci kanta cikin jin nishadi ,daga gani wannan ɗan comedy
ne ,kuma duk yanda akayi mutanen Sheikh ne na wasu ƙasashen



“Tafaddal”(Shigo) ta bashi hanya ya shiga ,itama ta rufo ƙofan ta biyo bayansa .

A tsakiyar falon yaja ya tsaya ,suka gaisa sosai



“....Ammm sunana Dr Adnan Ni Likitan ƙwaƙwalwa ne ina da Asibiti a ƙasar nan ,London Specialist ,nazo
ziyarar aikine So nasa a siya mun gidan da innazo zan ringa sauka Inshallah ,shine aka bani wancan gidan
da yike kallon nan Compound ɗin.”



A ɗan ɗarare Sayyidah tace “Sannu sir,Ashe maƙoci mukayi”




“Na'am,to shine fa tun safe na sauka da empty stomach ,bansan koina ba ,Inason inci abinci ,amma
gaba-daya water system ɗin da wutan gidan na kasa connecting ,bansani ba ko ƙauyanci ne😆Ko tsarin
naku na irin na ƙasar mu bane oho”



Dariya Salima ta fashe dashi

“Hummm ɗan gayu kamar ka ai saidai ace baku saba da ganin local one irin namu ba ,na en
Nigeria...Nikam yanzu me kake so inyi maka”
“Yawwa don Allah to ki ɗan haɗa mun wai cofee ne insha atleast kafin in samu a gyara mun komai
nawa”



Gaban sayyada fadi yayi dam ,a take idanuwarta suka zazzago

Ta fara sosa ƙeya “Ammm eh ,dama ehhhh ,wallahi bamu da kayan shayi ” ɗaga kai yayi yana ƙarewa
falon kallo ,gida har gida kudi gasunan basu magana wai ba kayan tea” bai nuna mamakinsa ba sai ma
wayancewa yayi irin na gogaggun maza da suka saba hulda da mutane .



“Nop karki damu ai ma taho da nawa kawai ruwan zafi nikeso ” ya mika mata ledan hannunsa ,Plz ki
hado mun a ɗan mug.



Amsa tayi a kunyace ,ta wuce Katar Katar ,ɗuwaiwuka da nonuwa suna ta rawa a Jallabiya ,bin bayanta
da kallo yayi ,inner side ɗin zuciyarsa tana harbawa da ƙarfi ,a zahiri yace “Wow Original kyau please”



Sai kuma yayi saurin minding business ɗinsa ta hanyar daukan remote Yana canja channel din TV.



Minti kaɗan sai gata ta dawo da ɗan mug din shayi a saman tray ɗinsa da ɗan cokale a gefen cup ɗin.

Ta saman kansa ta miƙo masa



“Gashi ” Hannu biyu yasa ya karɓa yana bin ƙirjinta da kallo

Haka yakai cup din baki ya kurɓa “Shukran”(Nagode) ...Amma ina naki?”



Zaro ido tayi ,a ranta tana cewa shi wanann ya faye shishigi Ni ya tashi ya fita kafin ya Sheikh ya dawo.



“Ya zanyi in Sha maka abunka ? Hazha haram,ga sauran kayanka nan” cikin mamaki ya ajiye cup din
shayin a saman table yana kallonta .



“Kar kice mun kina da rowa?” girgiza masa kai tayi da sauri
“To Ni kayana na kowane ,in inacin abu Naga wani bayaci gaba-daya abun gundura na ma yake yi,don
haka Matsawar bazaki hada naki ba to nima na fasa sha”



Sayyada da tun asali ƙamshin shayin yake damunta ,miƙewa tayi a sanyaye ta samo cup ta ɗiba Dan
kaɗan zata mike yace “Wai ku haka kuke shan tea so watery _Ba kauri?_”



“A tattala Mana in ya kare fa kaya na tsada a nan?”



Zaro ido yayi

“Topah ,Add things johhhhrrr”



Lafiyayyen Tea sayyida ta haɗa tazo falon can nesa dashi ta zauna tana sha a ɗarare duk ta ƙosa ya tafi



“Kayi hakuri ba bread ”



“Nop banashan tea da bread ,akwai kaza? Ko soyayyene?”



Zaro ido tayi harda dafe ƙirji

“Kaza? A nan?(kawai sai ma ta fashe da dariya)



“Aah baƙo babu”



“Halan su mama da baba basa nan ne wai?”



“Nan fa gida na ne”
“Oh dama ƴan mata suna iya zama a gidansu su kadai ba aure?”



“Sir I'm married” tsuriii ya kafeta da ido yanason gano asalin gaskiyar



“Hummm Saboda kin ganni baƙo shine zaki mun kora da hali?”



“Aah wlh da gske”



“Wow amma fa mijinki ya iya zaɓe,wlh kin cika duk wasu quality da nike neman mace dasu ,da na sami
irinki da tuni nayi aure"



Sai yanzu ta masa kallon ƙurilla ,tabbas ya haɗo kuma tana kallonsa ba abunda ya faɗo mata a rai sai
aure. Ji take tamkar ta rungumesa ko zata samu sassauci,lokaci daya bugun nunfashinta ya daɗa
hauhawa



“Ƙatotonka dakai ba mata abun kunya”



A shagwaɓe yayi magana gamida langaɓe kai kamar zaiyi kuka



“Hum ban samu taste Dina bane ,nikuma gaskiya bazan iya auren macen da take not active a gado
ba,saboda gaskiya Ni maciyi ne,I'm sorry kuma kinsan duk foodie dole yana buƙatar ɗumin active woman
a Koda yaushe...”



Sunkuyar da kai tayi cikin jin kunya.



“Sorry na baki kunya ko? Ni namijine ke namiji... magana ake na gender equality ,kinsan komai na sani
daga halittan mu aka halicceku ,dole muna da sha'awar jinsin da bamu dashi ko ba haka ba ?”
Shiru ta sake yi Tana jin wasu feelings da ta manta when last ta jishi yana taso mata,Zuciyarta tayi
rauni ,hawaye a take ya fara kwanciya a idonta ,babu abunda takeso sai taji ɗumin namiji a kan
gadonta,amma ina abun ba da sauki bane ba ,kullum ya Sheikh yana cikin Alwala baya son ko da wasa
hannun mace ya shafi jikinsa bare ta karya masa Alwala.



Zumbur tayi ta mike tasa bayan hannunta tana goge ƙwalla

,tana tuna hadisin Manzon Allah da yike cewa duk inda mace da namiji suka kasance na ukunsu shaidan
ne.



“Mijina ya kusa dawowa zanje in masa girki”



Dariyar yake yayi “Ok Nagode da karamci,meye sunan ki to”



“Salimat” ta bashi amsa tana nufar ƙofa da sauri ta buɗe masa , Murmushi yayi amma shidai
psychologist ne ,ya fahimci akwai abinda ke damun Salima ,kuma ya kudiri aniyar zai bibiyeta a hankali.



A sanyaye ya sakai ya fice saida ya kai saman varendar ɗin ta sanann ya ɗago mata hannu “Bye Nagode
fa,kyakyawa"



Dammm! Ta rufo ƙofa ta koma ta maƙale bayanta a ƙofar kawai ta kurma ihu da ƙarfin tsiya kamar
zararriya.




_Plz next update na masu Aurene ,kar a karanta mun in ke budurwace_
Oum Aphnan

09065990265

*_🐹BAD BOYS🐹_*

By...

Oum Aphnan



009

___________________

_Emirate_

Yau fa fada An tashi da baƙar labarin rashin Lafiyar mai martaba ,saidai a kwantar saidai a tayar ,an
kwana dashi lafiya an tashi ba baki ,ba shiri Mai babbar ɗaki ta bada umurnin saita tafiya zuwa Cairo don
binciken lafiyar mijinta don ga dukkan Alamu ya shiga _*Coma* and if care is not taking will definitely
loose the king....what is the way out?_



A lokacin da ake kuciniyar fitar da sarki ƙasan kuma a lokacin duk wasu king makers suka kutso ɗakin da
me martaba ke kwance rai ga hannun Allah ,don a cewarsu ciwonsa ta iya yiwuwa sharrin
magautane.....But it will shock you ,all this drama Yarima baya gida baisan ana yi ba ,ya shiga cikin gari
ran gadi.....wani wainar ake toyawa ?

Gadai Waziri,Fagaci,Ciroma da sauran manyan fada kewaye da gadon sarki a daidai Lokacin da Babban
Malamin fada ke durƙushe a gaban Sarkin yaja carbi mai dubu da Alluna cike da ƙasa ,sai dukan ƙasa
yake yana shafewa yana sake zanawa duk don gano me ke faruwa da Sarkin a wannan safiyar?



Mai babbar ɗaki da Autar sarki a furgice suma suka shigo ɗakin suka yi carko carko a tsaye .



An kwashe sa'oi biyu cikin wannan halin gidan yayi tsit bakajin ko tarin bil'adam
Babu zato sukaji Malamin fada ya doki ƙasa cikin tashin hankali ,wani zufa nan take ya shiga karyo masa
kamar an watsa masa ruwan famfo.



Cak ya kakkaɓe rigarsa yana haɗa kayan wuridinsa cikin jakar fatansa ,zuruuuu kowa ya bisa da ido ,haka
ya taƙarƙara ya mike yana dogara sandarsa yaje gaban kan sarki ya tsaya kana a sanyaye cikin mutuwar
jiki yace “Sauya sabon Sarki shine samun lafiyar mai martaba !!!!”



Dararass gaban kowa na ɗakin ya fadi ,saboda indai malamin fada ya fadi magana to yanki takene haka
zai faru ,kenan Lafiyar sarki ne zataci gadon mulkinsa



Kowa yayi jungum jungum cikin tunani ,kafin su ankara har malamin fada yakai bakin ƙofa zai fice daga
ɗakin ,taran gabansa auta tayi cikin kuka ta kange bakin ƙofa



“Ya malamin fada to mu ya makoman abban mu? Yanzu zamu wuce dashi Cairo ganin likita”



“Cutar mai martaba ba na asibiti bane ba,idan har kuka bar dashi dakin nan tamkar kun fita da gawarsa
ne,Kuma fitintinu su zasu biyo bayan hakan”



Ƙara auta ta saki gamida rugawa da gudu gadon da babanta ke kwance tayi ta daura kanta a ƙirjinsa ta
kece da kuka .



Mai babban ɗaki kam ƙeƙam tayi cikin wani irin jarumta ,fuskarta nuetral ba yabo ba fallasa.



A dake ta kalli malamin fada sannan ta magantu “Sai a shirya gagarumin bikin naɗa yarona yarima sarkin
faƙat!”



Ɗagowa yayi ya mata wani irin kallo mai kama da tausayawa ko tsorataswa .
“Bamu da damar ɗaura wani mahaluki akan kujerar mulki har sai masu tsaron kujerar sun bada umurnin
wanda zai hau ,don haka ba naɗin sabon Sarki sai nan da sati guda .....daganan ne yarima zai tabbata
magajin kujeran nan ko akasin hakan....”



Yana gama magana ya fice daga ɗakin yana dogara sandarsa dakyar ƙafafuwansa ba takalmi



****

Wani irin gudu motocin Yarima suke shararawa akan kwaltan garin duk inda talakawa suka hango layin
motocinsa sauka da ababen hawansu suke ɗingurgum akan kwaltan har sai ya wuce.



Baba kadarko ,dattijo ne dan shekara 58 ya hudo ta ƙararramar hanya yina gungura tsohuwar kekensa
da ya ɗebo kara daga Gona ,cikin gaggawa yake tafiya sakamakon yarinyarsa Ummulsulaim ta dawo daga
makarantar kwana tun safe ba abinci a gidan ,shine ya fita yayo masu karare a samu ko taliya ƴar muji ne
a ɗan silala mata.



Yina dab da karya kwana shiga layin gidansa da ake hange tun daga farkon layi ginin jar yanɓu an ma
ƙofar Gidan labulen tsumma,ko arzikin kofa basu da shi.



sukuma daidai motocin su yarima suka keto fiyauuun fiyauuuun a tsiyace ,Raɓewa ya yi ta gefen hanya
zai cusa kekensa a hankali .

Saidai Wani ƙara ne ya ziyarci kunnensa na bazata, yaji kuuuuuuu ! wanda ya sashi firgita ya ɗago a
tsorace.




Kafin kace meye wannan motocin Yarima sunyi dafifi a kan baba ɗan tsoho ,firgita kam iya firgita
yayi ,amma haka ya aro mazantaka ya saka a ransa .



“Bayin Allah lafiya?”
Basu tamkasa ba suka fara kiciniyar ɗaukar kekensa su saka a Boot ɗin motarsu .



Baba sa azama ya damƙi hannun Yakubu



“Ɗan nan tsahirta...karka karya mun wuyan keke ,meye hadinka da keke na?”



Banza yayi da shi sai ma yana ƙoƙarin fincikarsa haɗe da keken ,don haka baba yayi tagal tagal zai
kifa ,wannan abu ba ƙaramar ƙona ransa yayi ba ,don haka cikin zafin nama yabi bayansa daidai zai saka
keken a mota ya daddage ya tsinke guard ɗin yariman da mari .



Ji kake faffassss!



Kafin ya sauke hannu a kuncin Yakubu yaji wani lallausan hannu ya kece fuskarsa da mari Wanda yasa
baba sakin fitsari a wanda ,idanuwarsa ɗif suka daina gani na wucin gadi ,kafin yana farfadowa yaga anyi
gefen hanya dashi an yasar ,sannan kuma an dauke kekensa an cusa a mota.



Ɗaga ido yayi yana kallon mutanen da suke ƙoƙarin yi masa fin ƙarfi haka ,yana kuma son ganin wanda
ya shafe fuskarsa da mari.

Bakowa bane face Yarima



“Allah ya ɗaiɗaita aniyarku ,yanda kuka tozarta Ni fanni ya tozarta kuruciyarki ,da duk abunda kuke
takama dashi”



Cakkkk yarima yaja ya tsaya yana kallonsa

Tsirrr cikin bana ya tsirga ya mike da sauri ya taka zuwa hanyar ƙofar gidansa



“ku dakatar dashi ” he ordered
Bai wahalar da Shari'a ba yaja ya tsaya



“WAYE YA BAKA IZININ RAYUWA A MASARAUTA TA?”



Kallon mamaki Baba ya bishi dashi ,kawai sai ya sunkuyar dakai yana kallon kasa yana mamakin wannan
Al'amari ,an wani banƙareshi kamar yayi sata.



“Ina takardan ka na shedan zama ɗan garin nan” waro ido yayi

“Topah ,jidali sabo!



Bai tamkasa ba ya yi masa shiru



Tsawa ya daka masa

“Kai talaka! Ka bani amsa ”

Girgiza masa kai yayi ma'ana baida shi .



“Kuma baka da takardan shedan zama ɗan garin nan har kake da gut ɗin zagina? Har kake da encin
noma a ƙasa ta! Wannan kana zagin masarautana ne ”



“Ni ban taba noma a gonar kowa ba sai gonar da na gada iyaye da kakanni



Subhanahi yarima ya hassala iya hassala Don haka ya daka masa wani mugun tsawa



“Rufe mun baki ina magana kana magana.....Yaƙubbb” ya ƙwalla ma yaronsa kira da yafi ji dashi a kaf
cikin yaranshi



“Ɗauko mun littafin ɗaukan rai!”
Da gudu yaƙub ya nufa wajen mota sai gashi ya dawo hannunsa ɗauke da wani rafkeken littafi Kamar
album an saka farin ƙyalle a tsakiya .



Yana zuwa gaban yarima ya wangale masa tsakiyar littafin ,bindiga ce kwance akan farin ƙyallen cike taf
da bullet .



Sa hannu yayi ya ɗauketa ya gyara mata zama tayi ɗan ƙara alamar alburushi ya shiga cikin mazauninsa
kana ya saita goshin baba kadarko.




Ummusulaim da mamanta suna daga cikin gida suke juyo Hayaniya sama sama daga waje wannan yasa
ummuh leƙowa , subhanahi wa zata gani ? Babanta ne an rirrikeshi an saitashi da bindiga za'a kashe
banza .



Wani irin ƙara ta saki mai tada tsikar jiki ta fyalla da gudu ta rumfashe uban tana kururuwa.



Baba hansai da gudu ta nufi gaban yarima ta tumu akan ƙafafunsa tana majinjinu tana gyara leɓen
zani ,tana roƙonsa yayi masu rai kar ya kashe mata miji shikenan gatansu



Yanda baba ke tima take burgima a kasa yasa ya sauke bindigar ƙasa yana kafe ummuh da ta sha gaban
babanta ta masa rumfa tana faman tutturo ƙirji kenan harbin ya sameta kar ya sami abbanta.



Murmushin ƙeta yarima ya saki ,gamida taune leɓe.



“Na yafe ma mijinki” wani ihun murna baba hansai ta saki



“Ehoo mun gode Yarima mun gode....”
“...Amma har zuwa lokacin da zai mallaki takardar shedar zama ɗan garin nan ,zata kasance Tawa...” ya
Kare magana yana nuna Ummulsulaim dake jikin babanta



Wani ƙara maman ta saki “Innalillahi ka taimake Ni kar ka rabani da ƴata ita kenan mana wallahi ƴar
makaranta ce yau ɗin nan ta dawo....” bai saurare su ba ya juya zuwa motarsa aikuwa guards dinsa hudu
sukayi ƙawanya suka cicciɓeta wannan ya rike hannu wannan ya rike kafa ,tana zille zille iyayenta na
binsu da gudu ummusulaim tana kurma ihun kiran iyayenta tana ɗaga masu hannu amma haka suka je
motan da yarima yake ciki suka bude ɗayan side ɗin suka wullata ciki.....




Ƙura ta tashi da karfi cikin minti kadan duk motocin suka watse aka bar su baba a yashe suna kurma ihu.




***

Ihu Ummulsulaim ta cigaba da kurmawa shikam gogan ya harɗe ƙafa ɗaya kan ɗaya yana karanta jarida
tamkar ba kuka take ba waƙa take masa.



Zuwa wannan lokacin ba abunda ya ƙosa illah ya isa gida yayi wanka ya miƙe a ruwan cikinta ,don kallon
farko ya hararo baiwan niima a ƙwarmin idonta .




“Ina fasa budurcin da kike taƙama dashi kuka ya ƙare ,as you know now you're belongs to me,ko ki
lallaɓani ko in maki shigar fata fata ,in maki cin wulakanci....




Ɗif Sulaimiy ta ɗauke wuta ko tari ta kasayi ,ta fara tunanin yankata yake nufi zaiyi ya cinyeta ɗanye ko
ƙaƙa?
Oum Aphnan

09065990265




Wannan shine zai kasance page na kusa da ƙarshe na pages ɗin kyauta ,daga page 10 na kyauta ya kare

Ki hanzarta biyan kudinki don ayi tafiyar dake ,BAD BOYS Ba Littafin Yara bane muje zuwa💃



Wacce ta shirya biya

Regular 500#

VIP 1000#

Special 2000#



Katin MTN ko ta nan bank din

7782217014

Mohammed Hassana

Fcmb bank

*_🐹BAD BOYS🐹_*

By...

Oum Aphnan



010

_LAST FREE PAGE_
Daga wannan page din na kyauta ya ƙare ki biya kuɗinki don karanta littafinki cikin salama🤗

Regular 500#

VIP 1000#

Special 2000#

Zaki biya ta katin MTN ta wannan Number

09065990265

ko kuma ta wannan Account Number

7782217014

Mohammed Hassana

Fcmb

Sai ki tura shaidar biyanki ta wannan Number

09065990265

___________________

Sayyada

It's late Evening gari ya fara duhu magriba ta ɗan gota ,Sayyida fitowa wajen compound dinta tayi da
sauri ta saka shirmemen jilbab yasha squeezing hannunta rike da ledan bin na zubar da shara ,zata zuba
a ƙatoton sanitary bin din da yake wajen gets din gidajen layin nasu .



Bismillah tayi a hankali a ranta kana ta buɗe bin din ta jefa discardable linning din ,ba zato taji ance “Hi”



Da sauri ta waiga bayanta ,Dr ne tsaye cikin shigar suit sai bulbula ƙamshi yake ,fuskarsa maƙale da eye
glasses



Washe baki tayi “Aah ya ɗabib ,a'anta Huwa?” (Aah likita kaine haka?)



Murmushi yayi ya lanƙwashe hannayensa akan ƙirjinta ya ɗan yi tsayuwar samarin nan masu son janye
zuciyar mace garesu
“Me kikeyi anan?”

“As You can see shara na zubar”

“Shara? Da Daren nan?” Murmushi tayi gamida gyada masa kai ,ita bata ma ji wani abu ba

“Ai nayi Bismillah kafin in zubar babu abunda zai sameni”

“Amma kamar naga mijinki ya dawo ai ko ,me yasa bazaki bashi ya zubar ba tunda bakida house help”



“Humm😁Ashema ka ganshi,to zan bashi next time ,ok?” ta ɗan yi magana in hurry tana son juyawa ciki



“Sissss ji mana” cak ta tsaya saidai wannan karon dukar da kai tayi saboda bata jin dadin kallon da yake
mata ,infact kadaicinsu ma ya na sa mata jin wani yanayi na dabam ,wacce bata san ko menene ba



“I observed something...” A tsorace ta ɗago tana kallonsa ,cikin mugun tsarguwa



“Menene?”

“Salimart ,anya kinajin daɗin auren nan?,anya mijinki baya azaba maki?You look so unorganized ,ji
hijabinki a yamutse kullum baki gayu despite the fact that ke ƴar gayu ce and well educated but why...”

Ɗaure fuska tayi ,lokaci ɗaya ta nema walwalarta ta rasa ,a duniyar ta ta tsani a zagi zaman auren ta



“Uhum hakane ,you're not far away from the truth ,Saidai abinda nake so ka gane shine duk wani family
akwai yanda tsarin gidansu yake don haka nawa gidan haka tsarinsa yake ,Nagode sosai da saka Ido ,zaka
iya ci gaba da aikin sa idonka ƙofa a buɗe take” ta juya idonta na dab da zubo da ƙwalla .



Ɗaga mata hannu yayi a tsorace kana ya fara magana cikin in_ina.



“Aah ahmmm aaahh Salima ,kiyi hakry ba ina nufin ɓata maki rai bane ba”
Juyowa tayi ta kalleshi eye ball in to eye ball kana ta saki murmushin yaƙe wanda yafi kuka ciwo



“Baka ɓata mun ba ,ko kaga na sauya maka ne🤨”



Girgiza kai yayi cikin saccewar gwuiwa

“Ko ɗaya,shikenan Sai da safe I'm heading to work now ,Ina da emergency operation”



“Allah ya tsare ya bada Sa'a”



“Amin...amin wife material ” juyowa tayi ta kalle shi



“Me kace last?”

“Uhm uhm kawai cewa nayi Amin mace ta gari” kyaɓe fuska tayi ta tura gate din gidanta a hankali ta
shige ,tsam ya tsaya yana kallonta ta saƙon ƙarafunan gates ɗin har ta buɗe main door ɗin da zai shigar
dakai falon ƙasa na gidan ,kamar ance waigo? Taga yana tsaye yana kallonta tun daga wajen gate
din ,Suna haɗa ido ya ɗan girgiza kai ya ɗaga mata hannu.



Wani abu ne ya ɗan tsikareta a zuciya a sanyaye ta masa waving good bye ,ta rufo ƙofar falon ta manna
bayanta akan ƙofar .



Wani yarrrr taji ƙwalwarta wasu abu na mata yawo kamar kiyashi ,ta rasa tunanin me ma ya dace
tayi ,kawai da ta rasa mafita batasan sanda ta buɗe baki ta kurma ihu ba “Ahhhhhhhhhhhhh”



Da gudu ya Sheikh ya sakko daga benen yana haɗe stairs bibbiyu



“Lafiya?...Lafiya??”
Dukan kanta ta somayi cikin borin kunya ,da sauri yazo ya kamo haɓarta ,ya tsira mata ido kyarrrr.



“Salima sa idonki cikin nawa,me menene?” kwantar da kanta akan kafaɗunsa tayi nufin yi amma yayi
masa ya ɗan ture kanta



“Salima meye wai? You're changed person”



Cikin shesheƙan kuka tace “Ya Sheikh i need se*x Ya Sheikh ina so ka cini ,I felt so so urge to se*x...”
hangame baki yayi yana kallonta ,amma maimakon ya dauki wani mataki kawai sai ya kamo ta ya saka
bakinsa a saman kunnenta ya fara mata ƙira'a a kunne.



Ɓarkewa da kuka tayi tana ƙoƙarin turje kanta yana sake damƙota .



“Salima nasha fada maki gidan nan da aljannu ki daina yawo tsirara_tsirara ko ki ringa zama ba ɗankwali
amma kinƙi ji .....Walaya'uduhu hibzuhuma wahuwal aliyyul azeeem" tuf ! tuf ! tuf!!



Ya cigaba da mata feshin miyau a fuska



“Uhm Ni banda Aljannu saboda nace ka kwanta dani shikenan Aljannu? Ni ka ƙyaleni” sakinta yayi yaje
ƙofa da gudu ya mirza key

Wai saboda kar ta gudu.



Ya wuce ɗakinsa ya ɗebo maul khal ya ajiye ya koma ya ɗauko Black seeds ya zuba a burner Yana ƙoƙarin
connecting da wutar nepa.

Ai da Salima ta

Book Chapters
Chapter 1Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4

Please Login or Register in order to submit comment