Reading Ƙanwar Maza Book 3 & 4 By Aisha Adam Chapter 10 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

masifar Samha ba, an shakkarta sosai da sosai, saboda a tsaye take ba ta da kunya, yaya rumaisa za ta yi da ita, ita da take yarinya ?an?anuwa?.

Rasa abun yi ta yi, ta saSule ta zauna a kan gadonta, ?irjinta na cigaba da dukan uku-uku saboda tsananin fargaba.

Mintuna kusan sha biyar da fitar Samha, amma iman ta kasa kataSus, ?irjinta sai cigaba da bugawa yake yi.

Nusaiba ce ta shigo da sallama ta ce "Ashe kun dawo, bamu zaci zaku rigamu dawowa ba, mun je sai wa Sabir kaya, kin san ya kusa 6months, Ammi sai nuna mini irin kayan da za a zubawa amaryar takawa a lefe take, ya kuka baro ta?" Sai da Nusaiba ta kai aya, sannan ta lura kamar Iman a tsorace take.

"Lafiya kuwa?"

Iman ta jinjina mata kai ta ce "Lafiya lau"

Nusaiba ta ce "Kin ga idonki kuwa kamar mara gaskiya, ko wani abun ya faru a gidan da ku ka je ne?" Iman ta girgiza kai alamar a'a.

"Tsaya, ko jikinki ne ya motsa?"

Iman ta yi ajiyar zuciya ta ce "Babu ko Waya, cikina ne ya Saci zuciyata ce take tashi"

Nusaiba ta sauke numfashi ta ce "Har kin tsorata ni, bari na kawo miki anti acid, ina da shi a Wakina" iman ta jinjina mata kai.

Da Nusaiba ta fita ta sanarwa da Ammi iman ba ta jin daWi, ulcer ya tayar mata, a rikice ammin ta nufi Wakin Iman, ta je ta tutsiyeta tana tambayar ko jikinta ne ya motsa.

Kamar yadda ta yi wa Nusaiba ?arya, haka ta dake, ta Soye damuwarta, ta tabattarwa da ammi, ulcer ne kawai ya tasar mata.

***
Kwanciya ce ta isheshi, musamman da kwana biyun nan, a gida yake wuni saboda ?afarsa, amma yanzu ta yi sa?i sosai, kawai dai fita ce bai yi ba, gashi ya kusa komawa makaranta.

Kamar wanda aka tsikara, ya tashi ya fita falo, ya Wau lemon kwali mai sanyin gaske, ya koma Wakinsa, corridor ya nufa, ya buWe tagar a hankali, wata sassanyar iska ta dake shi, ya zu?e lemon tare da lumshe idanunsa.

Dare ne sosai, manyan security lights, sun haske ko ina na gidan, kukan tsuntsye na ta tashi, da ?anan ?wari, ga ?amshim furannin harabar gidan sun gauraye da sassanyar iskar da ke kaWawa.
Yanayin yayi masa daWi sosai, sai dai babu tsammani ya ga wani abu yana duddu?e, yana motsi ta jikin fulawoyin da zai sadaka da sashinsu.

Tsayawa yayi ya ?ura ido sosai, yanayin inuwar abun, kamar mace ce, dan har da lulluSinta.

Mamaki ne ya kama Mahmud, ganin maimakon ta shigo direct ?ofa, ta kutsa can ?arshen ginin da kai tsaye Wakin Mummy zai kai ka.

Bai yi wata-wata ba ya sauka, ya nufi sashin Mummy a hankali, sai dai bai buWe ya shiga ba.

"Kin shanya ni, tun Wazu nake zaman jiranki, amma baki zo ba"

Baba uwani ta risuna ta ce "Tuba nake Allah ya baki yawan rai, sawu ne bai gama Waukewa ba"

Mummy ta hura hanci ta ce "Ina jinki, bani labari, meke wakana da ki ke son ganina?"

"Allah ya baki yawan rai, labari ne nake tafe da shi, idan yayi miki daWi haka nake fata, idan bai yi ba ayi mini aikin gafara"

Cikin ?osawa Mummy ta ce "Hanzarta, ina jin ki"

"Takawa zai yi aure, sai dai alamu sun nuna kamar Iman zai aura, kuma zancen ya iske Samha ?ar wurin turaki, dan Wazu ta zo har wurin Iman Win ta yi mata kashedi da zafafan kalmomi, dan na laSe na ji komai"

"What? Aure kuma? A wannan karon kuma ita za a li?awa, ita ma ya cinyeta, lallai giwa ba ta tsoron Allah, amma na yi mamakin yadda aka yi Samha ta zo ba ta ?araso nan ba, kuma ba ta yi mini wannan bayanin ba, ko da yake ni kujera ce, ko dan zama za a neme ni, jeki na gode na ga yadda wannan lamarin zai yiwu"

Baba uwani ta ce "Godiya nake, na barki lafiya".

Mahmud ya so shiga Wakin Mummy, dan ganin wacece wannan, take zuwa a tsohon daren nan, amma ya fasa, ya lallaSa ya buWe ?ofa ya fita harabar gidan ya laSe.

Can baba uwani ta fito tana duddu?enta cikin duhuwar fulawoyi, ta nufi sashinsu ammi, tana buWe ?ofar, fitila ta hasketa, dan haka ya ganeta da kayan jikinta.
Hakan ya fallasa ma wacece ita, domin kuwa baba uwani kayanta ba Soyayyu bane ba, duk da tarin alkhairai da suturar da ammi ke bata, amma kullum cikin kaya Waya zuwa uku take.
Kan sa ya Waure da mamakin me take zuwa yi sashinsu, a wannan daren cikin siga ta rashin gaskiya

A hankali ya koma sashinsa, gaba Waya baya son wannan halin na Mummy, na bin diddigi da shiga abun da babu ruwanta, ya san ?arshe ba zai wuce rahoton wani abun ake kawo mata ba. Amma ya sha mamaki, idan har ace hadimar ammi ta kusa da ita, za ta aikata mata haka, to duniya kowa ma ba abun yarda bane ba.

***
Kwanci tashi asarar mai rai, mai girma turaki ya dawo daga aikin umara da ya tafi, duk da an riga an saba zuwa, amma ba a rasa ?an sannu da zuwa da su kan zo, domin yi masa barka da dawowa.
Ammi ba ta son takura masa, dan haka ta bashi lokaci, tare da sauraron abun da zai ce mata.

Duk da a nata Sangaren ta tsananta addu'a a kan lamarin sosai da sosai, tare da fatan tabattuwar alkhairin da yake cikin al'amarin.

?angaren Samha kuwa, da fari a iya tunaninta, za ta iya ji da lamarin, amma abun ya shallake tunaninta, kuma gaba Waya hankalinta ya karkata a kan Iman ce ake ?o?arin aurawa takawa, dan haka ta fara tunanin yadda za ta yi da ita, a ?arshe dai ta koma wurin Khalifa, domin samun mafita sannan ta je ta samu Mummy da zancen.

Mummy ta yi dariya ta ce "Yaro man kaz???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?a, ai na yi zaton ba zaki gaya mini ba, shi ya sanya na zuba miki ido na ga iya gudun ruwanki, ba shakka giwa wata irin murWaWWiyar mace ce, mara al?ibla, dan haka dole ki zage ki san abun yi"

Cikin damuwa ta ce "To ni yanzu Mummy ya zan yi?"

"Duk abun da ya kama ki yi, ko dai a kan Iman Win, ko kuma a kan giwa ko ma adam Win. A baya babu abun da ba mu yi ba a kan yarinyar nan, wanda hakan ya sanya duk ta rasa manemanta manyan mutane da suke zuwa wurinta, dan haka yanzu shine giwa ta yanke shawarar ?arshe na aura mata adam, shawara ta rage gareki, ko dai ki bari ayi auren daga baya ki san abun yi, ko kuma dai ki Wau wani matakin"

"TaS, ai wallahi da na bari ya aureta, gara uban kowa ma ya rasa, ni Mummy a cikin malamanki nake son ki haWani da wani, a watsa komai ko da kuwa yana nufin in rasa ta rasa kowa ma ya huta ne"

Mummy ta jinjina kai tana murmushi ta ce "To shikenan, zan yi tunani a kai kar ki damu"

"Mummy ba ni da dogon lokacin da zaki yi dogon tunani, dan Allah ki taimaka".

"Na ji zamu yi waya, ko zuwa sunday ne, akwia wani ?auye da nake zuwa, sai mu tafi tare"

Samha ta ce "To shikenan, na gode sosai Mummy".

Kusan sati guda da dawowar mai girma turaki, giwa har ta fara ?osawa, tana tunanin ko magana za ta yi masa, babu tsammanni ya kirata a waya ya ce zai zo.
Hakan yayi mata daWi, sai dai ta shiga fargabar da wacce zai zo, da nasara ko kuma babu?"

Kasancewar baba uwani na wurin, ammi ta yi waya da turaki, baba uwani ta saci hanya, ta je ta kira mummy a waya, ta kai mata rahoton cewar turaki zai zo, kuma da alama magana mai muhimmanci zasu tattauna, dan haka Mummy tace lallai ta sanya mata ido, ta naWo mata duk wani rahoto na abun da zai wakana.

Bayan sallar azahar, mai girma turaki ya iso gidan, kai tsaye ya sauka a sashin giwar da.

Hadimai suka shiga hidimar kawo kayan ciye-ciye, sai dai turaki ya?i magana a kan ha?i?anin abun da ya kawo shi, a lokacin da hadiman ke kaiwa suna komowa.
Dama tuni ammi ta hana Adam fita, ta ce lallai koma menene ya zauna ayi a gabansa, dan haka shima yana nan.

Ammi ta sallami hadimanta, Sannan ta nutsu ta fuskanci turaki.

Hakan ba ?aramin Satawa baba uwani rai yayi ba, dan babu damar samun rahoton da take son samu.

Ammi ta dubi turaki ta ce "Ranka ya daWe an dawo lafiya ya hanya? Ban samu shigowa ba, saboda ba na son zuwan nawa ya zama takura ko matsi a gareka, shiyasa ban yi maka sannu da dawowa ba"

Turaki ya ce "Kar ko damu, da ke da abun ya shafi zuriyar marigayi, dolenmu ne, kuma babu yadda za ayi ku zama takura a garemu.
Toh! Na zo da sa?onki, a can saudiyya ma na je gidan Wan uwanki mahadi, mun tattauna da shi sosai, kuma ya bayar da amanna sosai. Sai dai da muka dawo gida da kwanaki uku, mun sami wambai, in da ya nuna rashin amincewarsa da nuna za a sake zubar da darajar masarauta, ta hanyar auro wadda ba jinin sarauta ko tushen arziki ba, sai dai na yi iya yina na nuna masa ?ar gidan daraja ce da kuma gudunmawar da ta bayar.
Har ila yau ya gaya mana zancen da bamu ji daWinsa ba, ya kawo ?orafi sosai a kan ka takawa, ciki har da yin?urin taka Wan uwanka da mota, wannan lamari bai yi mana daWi ba, ya ce ya bayar da sa?o ka je, nan ma ka yi burus. Abun bai yi mana daWi ba, har yayi i?irarin babu shi babu kai, sai dai mun yi ?o?arin kwantar masa da hankali, in da har mai Wakinsa ta sanya baki, ta hanyar nuna masa tsaurinsa a gareka yayi yawa, shiyasa ba kwa shiri, amma dai duk da haka yakamata a din ga lura ana kiyaye wasu abubuwan, yanzu idon duniya a kan ka yake".

Ammi ta ce "Wallahi ranka ya daWe, abun da nake yawan gaya masa kenan, amma dai a cigaba da jaddada masa"

Turaki ya ce "Haka ne, akwai bu?atar a din ga kai zuciya nesa, akwai abun da yarinyar nan ta faWa mini a kan ka, wanda kuma tabbas haka ne ba ta yi ?arya ba, yana daga dalilan da ya sanya na yi amanna da auren nan sosai, nake yi muku fatan alkhairi".

Ammi ta ce "Allah sarki, Adam kuma ya sunkuyar da kai, yana murza zoben hannunsa.

"To, mun dai yi ?o?arin shawo kan wambai da ?yar, duk da yana nuna ba da yawunsa ba, amma ba wani abun damuwa bane ba zai sakko, illa iyaka kai takawa ka je ka same shi ka bashi ha?uri.
Magana ta gaba kuma, a sanar da iyayen Yarinyar nan, ranar juma'a zamu kai kuWin aure, kuma wata biyu zamu sanya rak, Allah ya tabbatar mana da alkhairi dan ba ma fatan a jinkirta wani abun ya zo ya gilma".

Ammi ta faWaWa murmushin ta tana faWin "Alhamdilillah, Allah ya sanya alkhairi ya nuna mana da rai da lafiya"

Yayin da adam wata irin mummunar faWuwar gaba ta same shi, kansa ya sara da ?arfin gaske, ya ji tamkar Wakin yana juya masa!


Ayshercool
08081012143
*MAMAN MEENAT COLLECTION, MAMAN MEENAT SUPPLEMENT/SKIN CARE*

*SHIN YAR UWA KINADA LABARIN* *SHAHARARRIYAR MAI SAYAR DA SUPPLEMENT DIN NAN KUWA?*
*TO IDAN BA KI SANI BA KIYI MAZA KI GARZAYA DOMIN KEMA KI SAMU RABONKI DOMIN ZATA GYARAKI TSAF KI FITO KAMAR SABUWAR AMARYA, KEMA KI SHAGA CIKIN MATAN DA SUKE HASKAKAWA KAMAR TAURARO. SHIN ?URAJE NE SUKE DAMUNKI, KO KUMA MATSALOLIN JIKINE KAMARSU RAMA BUSHEWAR FATA KARANCIN NI'IMA NE KO BUDEWA NE, KO KUMA INFECTION? KO KUMA SO KI KEYI FATARKI TAYI LAUSHI KIDIN GA SHE?I KINA HASKAWA? TO MAZA KI GARZAYO WURIN MAMAN MEENAT DOMIN KI SAMUN MAFITA CIKIN SAUKI, ACIKIN FARASHI ME SAUKI*
*SANNAN YAN UWA KUSANI DUK* *SUPPLEMENT DIN DAZAMU KAWO MUKU SAI MUNYI BUNCIKE AKANSHI DAN TABBATAR DA INGANCINSHI MUN TABBATAR DA CEWA BASHI DA WATA* *MATSALA GA LFY, AKWAI MASU CEWA SUNSHA SUPPLEMENT AMMA HAR YANZU SU BASUGA WANI CANJI BA, TO YAR UWA KODAI AN BAKI FAKE KO KUMA BA'A BAKI WANDA YA DACE DAKE BA, KO KUMA BAKISHA YADDA YA KAMATA BA, DOMIN KISANI YAR UWA KAFIN KI FARA SHAN* *SUPPLEMENT AKWAI WASU KA'IDOJI DAYA KAMATA ACE KIN KULA DASU KUMA KIN KIYAYE, MATUKAR KINASO SUYI MIKI AIKIN DA KIKESO CIKIN SAURI, WANNAN KA'IDODIN SAI KIN NEMENI ZAN SANAR MIKI, DOMIN BAZAN IYA KAWOSU ANAN BA SBD SUNA DA YAWA*

*Yar uwa muna da duk wani supplement da kuke bukata masu kyau da inganci tested and trusted, sayen na gari mai da kudi gida, gaskiya da Amana shine takenmu 08039437158.*

=?I? *Supplements suna da yawa amma ga kadan daga cikin su.*

*1. Supplements na gyaran jiki ciki da waje*

*2. Supplements na gyaran gashi da farce, dasa haske mekyau ba irin na bleaching ba*

*3. Supplements mai da tsohuwa yarinya anti aging wanda zaisa ki kullum ki koma kamar yarinya matashiya*

*4. Supplements na karawa fata kyau da sheki glowing skin*

*5. Supplements na masu fama da ciwon jiki da stress da rashin samun isashshen bacci*

*6. Supplements na masu ciki, da masu shayarwa wanda zai kara miki lfy keda babynki*

*7. Supplements na gyaran jiki da gashi, kara hasken ido da sauransu*

*8. Supplements me kara lfy da karawa garkuwar jiki karfi.*

*9. Supplements na karin ni'ima da dandano da tightening ciki da waje*

*10. Supplements na magance cututtuka, kamar matsalar ido ulcer, infection, karawa garkuwar jiki karfi, etc*

*11. Supplements na gyaran nono da mazaunai breast/hips Enlargement*

*12. Supplements na gyaran HQ ciki da waje*

*13. Supplements na rage tumbi slimming capsule/flat tummy Lipton*
*14. Supplement na whitening/glowing skin*

*15. Supplement for Acne, dark spots remover*

*Sannan ga wadanda sokeso jikinsu yayi kyau sosai amma basa son susha supplement to albishirinku muna da kowanne irin mai na gyaran jiki da kuke bukata irinsu lotion, cream, soap, scrubs, face Cream,sun screen, serums concentrate, hair oil, hair cream face mask etc, sannan ga masu fama da matsalar ciwon jiki wadanda kullum sai sunsha magani suke jin dadi ko iyaye ko kakanni, to albishirinku kuma mun kawo muku cream, soap na ciwon jiki masu kyau da inganci wadanda indai kana amfani dasu ka huta shan maganin ciwon jiki da yardar Allah*

*Muna saida duk wasu nau'in supplement Lotion da kuke bukata, sannan Maman Meenat collection ba anan kadai ta tsaya ba muna saida turaruka kowanne irin na wuta dana jiki, da Airfreshners, sayen daya ko sari ke dai kawai neme ni a wannan number call or chat 08039437158*




*PAID BOOK NE, ? 500 ME VIA 0009450228, AISHA ADAM JAIZ BANK, SAI SHAIDAR BIYA TA 08081012143*





Gaba Waya Adam bai san yadda aka ?are zaman ba, da ?yar ya tashi ya nufi Wakinsa, yana neman yayi karo da bango, dan ko gabansa ba ya gani sosai, saboda matsanancin ciwo da kansa yake yi, ga juya masa da duniyar take yi, ga wata irin kururuwa da yake ji a kunnensa.

Innalillahi wa Innalillahi raji'un, yake ta maimaitawa.

Gadonsa ya laluba ya kwanta, yana ta sauke numfashi, yana addu'a, sai dai kamar a hayaniyar yake jin muryar rumaisa, duk da baya gane me take faWa, daga haka bai kuma sanin in da kansa yake ba.

Bai san iya adadin lokacin da ya shafe a haka ba, ya ji ?amshin turaren ammi, tana taSa shi ta ce "Adam wai lafiya kuwa?" Ya buWe idonsa a hankali yana kallon ammi.

"Wa meyafaru da kai ne? Tun da turaki ya zo aka yi maganar nan, daga yi masa rakiya, na dawo na tarar baka nan, tun Wazu kake bacci sallar magariba fa ake yi yanzu"

Haryanzu kansa bai daina ciwo ba, ya dubi ammi ya ce "Bacci ne yayi mini nauyi, bari na tashi"

"Ka hanzarta ka rama sallolinka, kar ka sake bari lokaci ya ?ure maka ba ka yi salla ba, sonake mu je gidansu rumaisa, mu sanar musu, yau asabar ka ga nan da kwanaki shida kenan za a kai kuWin"

Magana yake son yi, amma ammi ta ce "Bana son musu, ka hanzarta bana son Sata lokaci"

Kawai ya jinjina mata kai, dan shikaWai ya san abun da yake ji, cikin dakiya ya tashi ya shiga yayi alwala, ammi kuma ta koma falo.

Iman kuwa tausayin rumaisa take ji sosai da sosai, ji take kamar ta sanar musu da abun da yake faruwa, da irin furucin da Samha ta yi.

Sai dai tana tsoron abun da ka iya biyo baya, mussaman yadda Samhan ta ?ware a iya fuska biyu da masifa, dan ita ba ta tausayawa kanta, yadda Samha ta yi zaton ita adam zai aura, kamar yadda take tausayawa rumaisa.

Adam saboda yanayin jikinsa, ya ce wa yaronsa sidi ya kaisu gidansu rumaisa, yayi iya ?o?arinsa da jarumta ya danne yanayin da yake ciki, sai dai jirin ya kasa barinsa.

Rumaisa kuwa, tana gida jikin mama tana ?un?uni, ta yi wa Huzaifa da Yasir rashin kunya, sun ce wannan satin ba za su wanke mata kaya su goge ba sai dai ta yi abun ta. Mama ta goya musu baya, ta ce "Kar ku wanke mata, tun da ba ta da ta ido, ai yakamata ta fara wanke kayanta da kanta yanzu, ke zaki wanke abunki yau"

Cikin shagwaSa ta ce "Dan Allah mama ki ce su wanke mini, idan na yi wanki rashin lafiya zan yi"

Mama ta kalleta baki buWe ta ce "Sangarta mai sanya kifi kukan wanka, samun wuri ne ya sanya ki ke wannan maganganun ma, ke ba dan Allah ya sa da su Win ba, ai shekara tara kin fara wankin ki, ko yaushe su suke yi miki, ba kuma dan baki iya ba, dole ki karSi abunki"

Rumaisa ta sake langaSe kai ta ce "Dan Allah mama ki ce su wanke mini, ni fa yarinya ce"

"Eh nono ma ki ke sha" ta kwanta a jikin mama tana cewa "Mama dan Allah" mama na shirin ture rumaisa, ruman ta tashi zaune da sauri, ta Wan tsuke fuska.

Mama ta ce "Lafiya kuwa?"

"Kamar baban Sabir zai zo gidan nan, yana hanya"

"Baban Sabir kuma?" Ruma ta jinjina kai ta ce "Haka nake ji a jikina"

Huzaifa ya ce "Iyeee soyayya da ?auna, bari zamu gani ai"

Rumaisa ba ta iya yi wa Huzaifa martani ba, saboda ji ta yi ?irjinta ya yi nauyi, jikinta kuma yayi sanyi ?alau.

A hankali ta zame ta kwanta a jikin mama, ta lumshe idonta.

"Ki tashi bana son barcin la'asar, ki yi shi ki tashi da fushi ki hanamu sukuni da koke-koke da Sacin rai"
Maimakon ta tashi, sai ta sake langaSewa, ta ri?e hannun mama.

Mama ta kalli rumaisa ta ce "Ke! Lafiya kuwa?"

Ruma ta jinjinawa mama kai alamar eh.

Mintuna ashirin, sai ga sallamar ammi, mamaki ne ya kama mama, dan ba su yi waya ammi za ta zo ba.

Ta Soye mamakinta, ta amsa mata cikin mutuntawa.

Suka gaisa da mama, ammi ta ce "Maman sabir bacci take yi ne?"

Mama ta ce "Rigima dai take ji, wai sai an yi mata wanki, na ce ma ta tashi kar ta yi mini barcin la'asar, ta tashi ta ishi mutane da kukan banza"
Ammi ta yi murmushi ta ce "Haba maman rumaisa, kamar rumaisa idan ba ayi mata wanki ba, ai ba zata iya ba, kar a ramar mini da ita kan ta zo fa"

Suka yi dariya, ruma daga kwancen ta ce "Ammi ina wuni"

"Lafiya ?alau rumaisa, kina lafiya?"

"Lafiya ?alau"

Ammi ta ce "To masha Allah, tare muke da takawa fa"

Mama ta ce "Ahh kuma ki ka bar shi a waje, Yasir ka ce ya shigo mana"

?oye mamakinsu suka yi, dan rumaisa ta ce ta ji a jikinta yana hanya.

Tun da yayi sallama jikinta ya kuma sanyi, ta rasa menene yake yi mata daWi.

Ya shigo Wakin mama, suka gaisa, mama ta ce wa rumaisa "Ba zaki tashi ki gaishe shi ba?" A hankali ta tashi zaune, ta kalli Adam sau Waya, ta kawar da kai ta sake kallonsa na biyu amma ta kasa magana.

Mama ta ce "Ba magana nake yi miki ba rumaisa?"

Ammi ta ce "Wannan ?ar tsamar ta su, idan da sabo sun saba".

Mama ta ce "wannan rashin Wa'a ne, ya girmeta, kuma mutumin da zaka aura ka din ga yi masa haka, iskanci ne kawai, ai ba haka take yi wa sauran mutane ba"

Rirri?e mama ta yi cikin kuka ta Soye fuskarta ta ce "Mama baki san me nake gani ba ne"

A rikice ammi ta ce "Me ki ke gani rumaisa, yi mini bayani?"

"Hararata yake yi, idan ya harareni ni tsoro yake bani" haka kawai mama ta ji rumaisa ?arya take yi, dan ta sha faWa ita fa ban da fuskar mai sunan baba, babu wata fuska da take bata tsoro.

A zahiri kuwa, a karo na biyu yau ta ga abun da ta gani a tare da adam, kamar yadda ta taSa gani, lokacin suna asibiti.

Idonsa gaba Waya ya koma ba?i ?irin, babu wannan farin, sai haya?i da yake fita, kamar ana kunna itace, a wannan karon har da kamar harshen wuta daga idanun nasa.

Shi kansa adam, cikin jikinsa wata irin rawa yake yi, amma a zahiri yana zaune normal, jikinsa ji yake tamkar ana sassra shi, ba bu wani abu da yake muradi, banda ya sha?e ruma ko ya ri?e ta, ya samu sassauci.

Ya sunkuyar da kai, mama kuma ?uluwa ta fara yi, da lamarin rumaisa, dan a ganinta rashin mutunci ne kawai.

Ammi ta ce "Haba rumaisa, shi ne har da kuka, ba hararki yake yi ba, haka yake dai bai fiye fara'a ba, ku da kun kusa zama abu guda ma. Maman rumaisa dama zuwa na yi na gaya muku, a sanar da dangin mahaifinta, ranar Juma'a za a kawo kuWin aure"

Mama jikinta yayi sanyi ta ce "Da wuri haka?"

"Kar ki ce haka maman rumaisa, jinkirin ba shi da wani amfani, kin san mu masaurata ba sa son jira, ayi musu addu'a dan Allah, in sha Allah za a kawo kuWin aure"

Har mama da ammi da suka gama tattaunawar su, babu wani ?warin gwiwar cewa wani abu, a tsakanin adam da rumaisa, kowannensu shi ya san halin da suke ciki.

Bayan sun gama magana, suna fita rumaisa ta tubure da kuka ta ce ita fa ba ta so, ba zata aure shi ba, da fari mama ta fara rarrashin ta, ta zaci abun na ta na hankali ne, amma ta ga ba ta da niyyar nutsuwa, ita dai ba ta gaya wa mama, me take gani ba, amma ta ce ba zata aure shi ba.

Shihowar mai sunan baba ce, ta sanya ta Wan nutsu, Aikuwa tambayar da ya fara yi, shi ne meya sameta take kuka.
Mama ta sanar masa da duk abun da ya faru, rumaisa ta zaci yanzu ma zai turje, sai ji ta yi ya ce "Allah ya tabattar mana da alkhairi, nan kano zasu kai, ko can katsina?"

Mama ta ce "Wai da su kai wa kawunku na mandawari, ba sai an wahalr da su ba"

Mai sunan baba ya ce "Babu laifi, Allah ya kaimu"

Cikin kuka rumaisa ta ce "Mai sunan baba ni fa na fasa bana son shi".

Wani mugun kallo ya yi mata ya ce "Suwa zaki mayar ?an iska, ko yau suka ce a Waura, sai an Waura, ki bari na fita na dawo na tarar kina wannan kukan, ki ga yadda zan yi ?asa-?asa da ke".

Haka nan rumaisa ta tsinci kanta da kasa gaya musu abun da take gani a tare da adam, da alamu suka nuna mata su basa gani, ita kaWai kawai take gani.

Usman kuwa cewa yake "Wallahi ba zaki yi mana ba?in ciki ba dan ubanki, haka kurum ke fa ki ke son auren mai kuWi, kuma Allah ya kawo, ki ce ke ba kya so, kin yi kaWan yarinya, dole ayi auren nan, ko ba komai ma hau doki, kina kallo albarkacinsa aka fito da Aliyu, yanzu malam shamsu har gaisheni yake, saboda yadda ya kankaro mana mutunci, sai kin je".

Cikin kuka ta ce "To ni bana son shi"

"Uban da ya sanya, ki ka amince tun da fari, shi zai sa ki ha?ura ma a yanzu" gaba Waya aka ?i goya mata baya, ta din ga surutai da koke-koke suka ?i kulata.

Ammi da suka tafi

Please Login or Register in order to submit comment