An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
*🌹RAYUWAR SAMHAD🌹*
DAGA ALƘALAMIN MARYAM STAR✍🏻
⭐⭐⭐
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/K8VBORyiBdJCR61hLJ9Hq9
*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mi id=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
𝑷𝑨𝑮𝑬1️⃣
_________________________________
بسم الله الرحمن الرحيم.
Tsaye suke a kanta suna ta sheƙa dariya, ɗayar budurwar wadda take kusa da ita ta fara magana cikin dariya. "Ke yanzu baki da sauran amfani, a haka za ki ka ƙare rayuwarki a auren dan daba wanda ya addabi kowa, waya sani ma ko can wajen yawon iskancin da kika saba kuka hadu har ya biyo ki gida, mu de wallahi an cucemu ambata wa gidan mu suna, Allah kaɗai ya san in da abun kunyar da kika aikata yaje"
" Nifa ba ma wannan ba Zee waifa Abba har wani fankama da tunkaho yake ya aurar da wannan borar. " Haka su ka saka ta a gaba suna ta ci mata mutunci, Duƙar da kanta ta yi ta na zubda hawaye masu zafi, A zuciyarta take cewa wannan wace kalar rayuwa ce? bata jin daɗi a wajen kowa ba ta da me sonta, babu wanda ya damu da ita, mai yasa Mahaifinta ze zama cikin masu yiwa rayuwarta illa, ta gaji da wannan rayuwar wadda babu komai acikinta sai bakin ciki da mutane masu son zuciya.
Ɗago da kanta tayi jin abin da zee ke faɗa. "Samhad ke da jin daɗin duniya har abada, sai dai ki gani awajen wasu ki dauki wannan aure a matsayin 'kaddarar da za ta sadaki da mutuwa, gidan da za ki shiga ki 'dauƙe shi kamar kabari, don wallahi ina tabbatar miki daga yau ko in ce daga yanzu Kin yi bankwana da farin ciki sai dai kiga wasu nayi ba dai ke ba."
Ta 'karashe maganar tana jefawa Samhad kallon tsana. Girgiza kai Samhad tayi cikin sheshshekar kuka tace "Nayi imani da ubangijina babu me kashewa ko rayawa sai shi, kuma dukan wani abu da zai sameni nayi imani daga shi ne, Anty Zee na riga na miƙa al,amarina a wajen Allah na san Allah yana sona tun da har yayoni mace kuma musulma, bari in tuna miki wani abu shi aure nufin Allah ne idan Allah ya nufeka da yin shi babu makawa sai kayi, wannan misali ne da ke, batun yanzu na san kina son kiyi aure ba na san ki na da buk'atar aure tun shekarun baya amma Allah be nufa kin yi ba, kin sha gorantamin cewa babu wanda ze aureni ahaka zan k'are rayuwata, kimmanta Allah shine ya ke tsara al,amurransa. Alhamdulillahi ko a haka aka tsaya naci riba dan na san na riga nayi gaba na barki a baya 'yar gata diyar so" ta karashe maganar tana sakarwa Zee murmurshi wanda ya sanya zuciyar Zee bugawa da k'arfin gaske.
Kallon Zee Haneefa tayi tare da jan hanninta su kai waje, fitarsu babu jimawa Samhad ta fashe da matsanancin kuka wanda jikinta har girgiza yake tsabar kukan, A hankali takai hannunta wajen wani photo tana shafa kuskar wacce ke cikin photon tana murmurshi kamar za,a kirata ta amsa.
"Ummanah farin cikina Ina kaunarki dan Allah ki dawo gareni ba zan iya jure rashin ki ba, rayuwar ta isheni haka nan wai kin san mai Abbu ya yi min? Auren dole Tatum in kuma auren cuta, Abbu ya cutar da rayuwata ba zan iya jure wannan zaluncinba, Ummana kin san mai yayi d'an daba ya auramin kuma bada amincewata ba, na san ke ma ki na jin kwatan kwacin Abin da na ke ji, Ummana zuciyata ciwo take kaina tarwatsewa zai yi in mutu ko na samu salama, Ummanah Ina son in zo lahira in zauna tare da ke, Ina son in yi rayuwa kamar ko wace 'ya a gaban mahaifiyarta."
Kukane me matsanancin karfi ya kwace mata nan take ta fadi awajen kamar matatta bata Numfashi, saurin shigowa Abbu dake bakin kofa yayi saurin shigowa jimfaduwarta, jijjigata ya shiga yi yana zubar hawaye yace "Kar kiyi mani haka diyar Albarka, karki mutu kibarni wallahi Ina sonki wannan shine kadai gatan da zanyi miki ba zan cutar da keba, dan Allah ki tashi shalele "
Jin sauti muryar Abbu yasa mutanen gidan fitowa suna ganewa idansu abin da ke faruwa,
Hajiya Adama ce ta shigo tare da tsayawa akan Abbu dake kuka tace "kai kuma lafiya ka zauna kana uban kuka sai kace karamin yaro? "
Bai tsaya saurarenta ba ya saɓi Samhad tare da fice wa yana zubda hawaye.
𝑨𝑩𝑼𝑱𝑨 𝑵𝑰𝑮𝑬𝑹𝑰𝑨
𝑴𝑨𝑰𝑻𝑨𝑴𝑨.
Wata arniyar farar motace ta fito daga wani arnen hadadden gida, taka motar yake damatsiyacin gudu kamar wanda zai tashi sama. Gudu yake bana wasaba harseda ya isa in da yake son zuwa.
A firgice ya bude motar ya fito daga motar doguwar sumar kanshi me kama da ta larabawa dukta hargitse, manyan idanuwanshi duk sunyi jah kamar gauta, hannu ya sanya a Cikin aljihunshi ya fiddo dalleliyar wayarsa yashiga laluben wata number.
"Saniga please gani na zo har in da kake dan Allah ka zo ka bani sak'on wallahi ba zan iya nutsuwa ba idan ban sha ba kaina tarwatsewa ze yi" daga can cikin wayar akayi magana wanda ni dai ban san me,a ka ce ba se jinayi yace, "No SaNIGA ba zan iyaba wallahi dole kasamomin abunnan ko kuma ka kaini in da zan samo" Dafe kanshi yayi tare da jefar da wayar ya bude motar yaja yabaɗe wajen da k'ura yayi gaba da mugun gudu.
𝑫𝑨𝑮𝑨 𝑨𝑳𝑲𝑨𝑳𝑨𝑴𝑰𝑵 𝑴𝑨𝑹𝒀𝑨𝑴 𝑺𝑻𝑨𝑹✍️⭐⭐⭐
🌹RAYUWAR SAMHAD 🌹( 𝑨𝒃𝒂𝒓 𝒕𝒂𝒖𝒔𝒂𝒚𝒊𝒄𝒆) 🥹
DAGA ALKALAMIN MARYAM UMAR STER⭐⭐⭐🌹
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/K8VBORyiBdJCR61hLJ9Hq9
*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
PAGE 2️⃣
_________________________________
بسم الله الرحمن الرحيم.
Tun bayan barin shi wajen ya samu gefen hanya yayi parking tare da dora kanshi a sitiyari, zafi zuciyarsa ke masa baya jin dadin komai, cikin matsananciyar damuwa ya runtse jajayen idanuwansa da k'arfi ya na tuna yanda rayuwa ta juya masa baya, har yanzu yana mamakin yanda farin ciki yayi k'aura a cikin rayuwarsa, idan dukiyace farin ciki yana da ita wacce har nanda shekaru masu tarin yawa ahalinsa zasu amfana da ita, amma miyasa yakasa samun cikakken farin ciki arayuwarsa? Kode yayi wani babban zunubi wanda be sani ba Allah yake hukunta shi ta wannan hanyar??? Ya rasa waze raba yaji dadi komai ya kwance masa. Daga hannu yayi sama yana addu,a cikin zubar hawaye da karayar zuciya.
"Ya Allah idan wani laifi nayi maka abisa kuskure ka yafemin na tuba, Allah na tuba ka gafartamin, ya Allah idan mutuwa hutu ce a gareni Allah kadauki raina kozan huta, Allah nayi iymani da kaddara me kyau da marar kyau Allah ka saukakamin wahalar rayuwa. "
Yadade yana zubda hawaye kamin daga bisani ya tada motar ya cigaba da tafiya cikin matsanancin gudu, mutane da basu gani su kyale duk inda ya gifta se anyi maganar gudun da yake shararawa, wasu suce "Allah ya shirya wasu kuma su zageshi suna me Allah wadai, wadanda sukasan mahaifiyarsa suce yaron Alhaji Muhammad k'arfe ne yafito yana wulakanci saboda ya nuna shidin wani ne, Kasancewar Mahaifinsa sanannen mutum ne kuma duk motocin gidan nasu suna da tambarin M k'arfe a jiki.
Kuka sosai Abbu keyi sadda suka isa asibitin dake kusa dasu. Allah yaso sanda ya fito da Samhad ma'kocinshi Mamman driver ya ganshi, dawowarshi kenan daga aiki ya hango Abbu yana kuka yana tsaida motocin dake wucewa wajen, saurin karasawa Mamman yayi inda Abbu yake, be jira komai ba ya bude mishi motar yana kama mashi Samhad da zuwa lokacin numfashinta ya fara dawowa amma sama-sma, suna isa asibitin dake kusa dasu aka amshi Samhad tareda bata temakon gaggawa.
Bayan an samu andidaita numfashinta aka saka mata ruwa tare da allurai.
Likitanne ya fito tare da kallon Abbu dake ta safa da marwa cikin tsananin damuwa yace "Baba muje office se muyi magana".
Saurin binshi Abbu yayi yana zullumin jin abinda likitan zace yana faruwa da Samhad.
Bayan sunshiga ya nunawa Abbu kujera yace ya zauna, Bayan ya zauna suka gaisa sama-sama Abbu yace "likita ya jikin Samha? Tade tashi ko? " yayi maganar yana zubawa Dr idanuwa yana jiran jin abinda ze ce. Saita nutsuwarshi yayi tareda kallon Abbu cikin sanin makamar aiki yace.
"Alhmdllh tana cikin koshin lafiya a yanzu haka, Allah yasa kunyi gaugawar kawota asibiti da wuri, a halin da ake ciki yanzu tana barci sede jininta ya hau sosai Amma yanzu Alhmdllh munyi mata duk abinda ya dace sede inaso inyi maka wasu 'yan tambayoyi"
Gwauron numfashi Abbu ya sauke yanajin kaso ashirin cikin Dari na zullumin da yake ciki ya kau. Saide haryanzu hankalinshi be kwanta ba tunda be ga halinda Samhad take ciki ba.
"Ina jinka doctor kayi tambayoyinka".
"Baba duba da yanda naga kammaninka da marar lafiyar nasan cewa dole cikin biyo seya zama gaskiya
A yanda naganka kuna kama sosai ga dukan Alamu kaine Mahaifinta ko kuma wani makusancinta na jini".
"Tabbas 'yata ce, ni na haife ta."
Masha Allah, Amma baba miyasa kukayi sake da lafiyarta?
A gwaje-gwajen da mukayi mata mun gane tana dauke da hawan jini kuma da alama bata samun kulawa akan hakan?
Numfashi Abbu ya sauke yace wallahi doctor ni kaina bansan yanda akayi nakeyin sake da al,amarin yarinyarba gata yarinya me hankali da nutsuwa, ga biyayya da kawaici. Amma duda haka nakasa tsayawa akan lamuranta. Insha Allah A wannan karon nasan nakaita hanya me billewa don kuwa nayi mata garkuwa wacce zata kareta daga ko wane irin farmaki, Samhad baiwar Allah Insha Allah daga yau ta gama zubar da hawayen damuwa, maraici, da bakin ciki sede na alfahari da farin ciki.
Shiru Dr yayi yana kallon Abbu dake magana yana zubda hawaye kuma yana murmushi duk a lokaci daya.
Bayan sun karashe tattaunawa Dr yabada shawarwari yanda za,a kula da ita.
Wai nikam baza,a iya sallamarta yanzu ba doctor? Cewar Abbu yana duba agogon hannunsa.
Muna jiran ta farka ne muga yanayinta sannan idan da yuyuwar a sallameta zamu sallameta insha Allah.
Shiru Abbu yayi yana addu,ar Allah yasa ta farka cikin koshin lafiya a basu sallama don yasan lokacin da aka bashi bazasu sauyaba tunda su ba kanannan mutane bane dake canza magana, a wani gefe na zuciyarsa yana tantama akan tafiya da ita yau kamar yanda sukace, wata zuciyar kuma na bashi kwarin gwuiwa akan hakan shine gatan da zaiyi mata, agefe daya kuma yana zullumin rabuwa da ita.......
Daga alkalamin maryam star⭐✍✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
Follow this
link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/K8VBORyiBdJCR61hLJ9Hq9
🌹RAYUWAR SAMHAD 🌹( 𝑨𝒃𝒂𝒓 𝒕𝒂𝒖𝒔𝒂𝒚𝒊 𝒄𝒆😭)
𝑾𝑹𝑰𝑻𝑬 𝑩𝒀 𝑴𝑨𝑹𝒀𝑨𝑴 𝑺𝑻𝑬𝑹.⭐⭐⭐✨🌹
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.co/
K8VBORyiBdJCR61hLJ9Hq9 *htps://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
𝑷𝑨𝑮𝑬 3️⃣
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
بسم الله الرحمن الرحيم.
Zaman shiru sukayi a wajen kafin daga bisani Mamman driver yayiwa Abbu sallama ya wuce gida zuciyarsa cike da tausayin halin da Samhad ke ciki.
Samhad ba ita ta farka ba sai da tayi awanni ukku tana barci. Abbu yaje ya fad'awa doctor farkawata zuwa yayi ya sake dubata tare da yimata 'yan tambayoyi, dayaga babu wata matsala ya sallameta kawai.
Sosai Abbu yaji dadin sallamar don ya riga ya yanke hukunci a yau zai mi'kata gidan mijinta don zuciyarta ta samu salama.
A daidaita sahu ya tare musu suka shiga. Suna tafe Abbu yana bawa Samhad hakuri tare da nasiha me ratsa jiki.
'Dago manyan idanunta da suka fad'a saboda kuka da damuwa tayi ta kalli Abba cikin karayar zuciya tace. "Abbu dan Allah da gaske kayimin aure? Anty zee tace d'an daba ka auramin hakane? "
Tayi maganar harshenta na sark'ewa.
Numfashi Abbu ya sauke tare da kallon layin nasu wanda ha wasu motoci suka jera tun daga farko har zuwa gidan shi dake karshen layin.
Samhad ma kallon motocin take zuciyarta na tsinkewa.
Abbu be sake magana har suka isa k'ofar gidan nashi. Me a daidita yasaukesu ya Abbu ya biyashi hak'inshi yayi tafiyarsa, kama hannun Abbu Samhad tayi tana rarraba idanuwa ganin ambud'e wata jibgegiyar hamshak'iyar mota, wani babban mutum ne ya fito fuskarsa da fara,a ya tunkarosu, yana zuwa ya mik'awa Abbu hannu suka gaisa cikin mutuntawa.
Gaidashi Samhad tayi ciki sanyayyar muryarta.
Kallonta yayi cikin fara,a ya amsa mata a ranshi yana yaba nutsuwarta, tabbas ya yaba da hankalinta kuma daga gani zatayi abinda ya dace saidai wani 'barin na zuciyarsa yana gaya mashi anya beyi son kaiba kuwa, wani gefen kuma yana bashi kwarin gwuiwa akan hakan shine dai-dai.
Maida hankalinsa yayi wajen Abbu suka ɗan tattauna,
Samhad bata fahimci komai ba seda Abbu ya kama hannunta yana mata kallon tausayi, gani tayi wannan mutumin ya buɗe wata wata rantsatsiyar farar mota yace wa Abbu bisimilla,
Janta Abbu yayi ya sakata cikin motar tare da yi mata magana cikin kwantar da murya.
"Kibisu Samha iyayen mijinki ne nasan zasu basu kulawar dana gagara baki tsawon rayuwar da mukayi atare, na yafe duniya da lahira kije ki riƙe mijinkin hannu biyu kiyi biyayya Allah yana tare da ke zan kasance me yimaki addu'a akoda yaushe Allah yayi maka Albarka ya karemin ke aduk inda kike." Yana gama maganar ya saki hannunta tare da ɗauke kwallar data zubo mishi.
Jikin Alhaji Muhammad yayi sanyi yanjin anya basu dauki alhakin yarinyar ba.
Gwauron numfashi ya sauke yana miƙawa Abbu hannu sukayi musabaha, sake jaddada mishi Abbu yake ya kula mishi da Samhad Ammana bata da kowa se Allah sekuma shi.
Tunda suka ɗauki hanya Samhad tayi shiru tanaji a jikinta wannan tafiyar itace mukulin bud'e sabbin ƙofofin da zasu saura RAYUWAR SAHMAD, tanaji akwai babban k'alubalen dake tunkaro rayuwarta.
Tanaji a jikinta akwai babban al'amarin daze faru da ita a yau ɗinan, hannu takai akan kyakkyawar doguwar fuskarta tana ɗauke hawayen da suka gangaro mata. A fili ta furta "ya Allah koma miyene ze faru dani ka sauk'ak'amin yanda zan iya ɗauka, Allah dakai kad'ai na dogara banida kowa se kai Allah ka ji'bnci lamurrana."
𝑫𝑨𝑮𝑨 𝑨𝑳𝑲𝑨𝑳𝑨𝑴𝑰𝑵 𝑴𝑨𝑹𝒀𝑨𝑴 𝑺𝑻𝑬𝑹⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐🌹
🌹RAYUWAR SAMHAD 🌹( 𝑨𝒃𝒂𝒓 𝒕𝒂𝒖𝒔𝒂𝒚𝒊 𝒄𝒆)
𝑫𝑨𝑮𝑨 𝑨𝑳𝑲𝑨𝑳𝑨𝑴𝑰𝑵 𝑴𝑨𝑹𝒀𝑨𝑴 𝑺𝑻𝑨𝑹⭐⭐⭐
: Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/K8VBORyiBdJCR61hLJ9Hq9
*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*
_
Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
________________________
🌹❤🌹❤🌹❤🌹❤🌹❤
PAGE 5️⃣
بسم الله الرحمن الرحيم.
Gaban Mammy yayi wata mummunar faɗuwa har tuntuɓen harshe take wajen Tambayar Samhad, "ke lafiya mike faruwa waya kawoki nan?".
Diriricewa Samhad tayi da kyar ta lalubo jarumta ta tace
"Babu komai dama wani abu ne ya fad'amin ido shiyasa kikaga ina kuka"
Ajiyar zuciya Mammy ta sauke duk da kamar akwai karya cikin maganar yarinyar.
Nannauyan numfashi Mammy taja tare da cewa Samhad, "yanzu ɗauko kayan kizo in kaiki masaukinki".
Ajiyar zuciya Samhad tayi tare da hamdala ga Allah da yasa Mammy bata fahimci komai ba, haba wannan abun kunyar har ina duk ta tsargu da kanta gani take kowama zai iya fahimtar abunda yafaru.
Ajiyar zuciya ta sauke bayan ta dawo daga tunanin abinda ya faru daga zuwanta gida.
A daddafe tashiga toilet dake dakin nata wanda ya ƙawatu da kayan zamani.
Ita yanzu gidan ya isheta batajin zata iya rayuwa cikin shi, gefe guda kuma tunanin yan gida da kewar Abbu sun isheta duk da ba wani sakin jiki yake da itaba amma kullum cikin yimaya nasiha da ban haƙari yake.
Ture tunanin komai tayi ta fara alwala cikin nutsuwa duk da jikinta da zuciyarta babu dadi.
A nutse ta gabatar da sallar isha'i tare da shafa'i da wutiri, bayan ta kammala ta fara kwararo addu'oi cikin zubar hawaye da karayar zuciya.
Ta dade tana addu'a kamin daga bisani ta tashi ta linke hijabin ta ajiye.
Abincin da Salma ta kawo mata lokacin da take sallah ta jawo ta bude fried rice ce tasha vegetables se ƙamshi spices take, se ruwan zafi cikin dan ƙamshin flask da lemon me sanyi.
Tanajin yunwa sosai shiyasa taci abincin amma kwata-kwata baya mata dadi hasalima wani ɗaci-ɗaci takeji bakinta nayi.
Bayan ta kammala ta yi brush ta kwanta kasan tyils tana tunanin rayuwa yanda take garata kamar kwallon kafa, batayi aune ba barci yayi awon gaba da ita.
A 'bangaren Hajiya Turai kuwa ajiyar zuciya ta sauke jin abinda Samhad ta faɗama Mammy, kwata-kwata ta manta da inda take ganin yarinyar ba ƙaramin rudar da ita yayiba, Wanka tayi tana tunanin irin mummunan hukuncin da Mammy zata yimata idan tasan tayi wannan gangancin.
Bayan ta kamala ta fito hakanan haihuwar uwarta ga uban tumbi gaba kamar me tsohon ciki,
Hajiya Turai irin matannane wanda basu da fasala, gata masha Allah doguwa amma babu gaba bare baya sede uban tumbi daya tasota gaba.
Rungume Mamy tayi suka hau aikata masha'ar su ko kunya babu basa tsoron mutuwa ta riskesu cikin wannan yanayin tunda babu wanda yasan ranar mutuwarshi bare ya shirya mata.
Allah kasa muyi kyakkyawan 'karshe Allah kadauki raimu cikin kyakkyawan yanayi🙏😭Allah ka sanyaya makwancinmu Ka haska kaburvuran mu ka jikan iyayenmu kayi musu rahama🙏🙏🙏
ƙanin
🌹RAYUWAR SAMHAD 🌹( 𝒂𝒃𝒂𝒓 𝒕𝒂𝒖𝒔𝒂𝒚𝒊 𝒄𝒆😭)
𝑫𝑨𝑮𝑨 𝑨𝑳𝑲𝑨𝑳𝑨𝑴𝑰𝑵 🌹𝑴𝑨𝑹𝒀𝑨𝑴 𝑺𝑻𝑨𝑹✍️⭐⭐⭐🌹
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/K8VBORyiBdJCR61hLJ9Hq9
*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
🔴🌹🔴🌹🔴🌹🔴🌹🔴🌹
__________________________
بسم الله الرحمن الرحيم.
𝑷𝑨𝑮𝑬 6️⃣.
Barci tayi sosai don bata tashi se bayan gama sallah shima Habiba me aiki ce tazo ta buga mata kofa.
Tunda ta gama sallah wani barcin ya sake daukar ta annan inda tayi sallar, bata sake tashi ba se da rana ta fito shima ba don barcin ya isheta ba kawaide dan ta saba tashi a irin lokacin tayi aikace aikacen gida.
Hajiya Adama tsaye ta tasa abu gaba akan lallai seya gaya mata inda yakai Samhad, Tunda ya dawo gida ya zauna sukusu dashi ranar ko fita be sake yiba sede lokaci bayan lokaci yana kiran waya.
Zuba mashi ido kawai tayi tana kallonta ikon Allah.
Numfashi Abbu ya sauke tare da kiran cikakken sunan Hajiya Adama.
"Adama wallahi zuciyata ta kasa nutsuwa akan hukuncin da na yanke akan aurar da yarinyarnan, inaji a jikina kamar ban kyauta ba Abun yana damuna wallahi.
Shewa Hajiya Adama tayi tare da tafa hannuwa tace "yau ni naga idi zindir yanzu kai saboda wannan shashashar yarinyar kake wannan damuwar tun jiya nake kallonka ko Abincin kirki baka ciba, Imbanda abinka kaida zakayi farin cikin rabuwa da ita lafiya ba tare da ta janyo maka abun kunya ba, duk da naji mutanen unguwa suna fadin wai ana ganinta a wani kango ita da malamisu suna zagawa yanzu haka....
Be bari ta ƙarasa ba ya yatshi fuuuuu ya fice ya bar mata gidan.
"Mtswwww yaja tsaki tace maganinka kenan ai wajen shegen son abin duniya ka dauki diya ka bawa masu shan jini, waya sani ko har sun halaka ta sunyi tsafi da ƙashinta, su Zee ne suka shigo suna tambayar wai lafiya take surutu ita kadai.
"Inafa lafiya ubnku ne ya zo yana ta damuwa akan waccan kodaddiyar yarinyar wai hankalinshi be kwanta ba tunda suka tafi wai ba tada lafiya gashi tafiyar ta kasance ta gaggawa.
Tsaki Fauzeey tayi tace wai ku bazaku daina zancen waccan yarinyar ba ni wallahi haushi kuke bani akanta kuyita abu wanda be dace ba kubarta manah tayi rayuwarta itama tunda ba shiga harkar ku take ba.
Gum sukayi babu wanda ya sake cewa komai saboda kamar shakkarta sukeji idan tayi magana dole subi kamar itace uwarsu.
Janyo ledojin da ta shigo dasu tayi ta mik'awa Hajiya Adama daya ta fice da dayar tana amsa kira.
Dirarwa ledar Hajiya Adama tayi tana faɗin, Allah sarki yarinyar kirki niko gaskiya na ƙagu wannan Alhajin ya fito ko ayi aren nan nadena ganinki haka a gabana.
Tsuke fuska Zee tayi tana faɗin waike hajiya se kiyita cewa kingaji da ganinmu mi muka tsare maki ne wai haka?
"Baku tsaremin komai ba Ammade idan kukayi aure ai na huta da ɗumim jama.a dake cewa kun tsofe kunki auruwa.
ABUJA NIGERIA
MAITAMA
Bayan kammala jera kayan breakfast kowa ya hallara duk iyalan gidan Alhaji Muhammad ƙarfe, Mamy ce ta lura da babu Samhad bata wajen, cikin iya duniyanci tace Salma wai ina kanwar taki naga ita har yanzu bata fito ba, Salma bata kawo komai a rantaba tace wallahi mamy bata futoba inajin kamar barci take amma bara induba.
Murmushi Daddy yayi yanajin farin cikin samun Mamy a cikin zuri'ar shi.
Cikin kulawa yace "Sannu Mamyn yara nasan kina ƙoƙari sosai wajen kulawa da gidannan Allah de ya biyaki Hajiyata"
Wani makirin murmushi ta saki wanda ba kowa ne ze gane da manufa daban tayishi ba se wanda yasan takan mugunta da makirci......
Daga Alkalamin Maryam star✍⭐⭐⭐✨✨✨✨✨✨✨✨
🌹RAYUWAR SAMHAD 🌹( abar tausayi ce 😭)
DAGA ALKALAMIN MARYAM STAR✍️⭐⭐⭐⭐
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/K8VBORyiBdJCR61hLJ9Hq9
*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*
_
Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
PAGE 7️⃣ TO8️⃣
_______________________________
بسم الله الرحمن الرحيم.
Tura ƙofar ɗakin da Samhad ke ciki Salma tayi tare da yin sallama ta shiga.
Zaune take akan gado idanunta a lumshe tana karatun Alkur'anin, jin sallamar