Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 6
ce wanka na yi za ni unguwa a'a don Allah banda yawo kar in je a kwacemin ke waye zai kwace ni kuma? Na sani by the way yaya Hajara? Hajara na nan lafiya tana jiran ganinka insha Allahu zan zo next week don yau zan tafi bauhci sai karshen sati zan dawo kisa raina ranar 'talata, Allah ya kai mu yaya su Yaya? Suna nan kalau, sai kazo ke nan? Wahiddah don Allah ki rike min alkawari na ce kar ya ji komai ni tasa ce ba wani bayansa. Ya ce “Love you darling, kaima haka. Na ajiye wayar ina dariya na yi saurin shafe shafe na dama ni bana sa kwalli, balle jagira saboda gashin gira ta da na ido sun ishe ni illah dan nashafa janbaki, shi ma faful kasancewar yana mani kyau to in ba jan-baki faful kika ban ba ba zan karba ba. Bayan na gama sai na yi shigar fakistan mai haďe da rigar na dauki jakata da mayafi na fito, Inna na falo da na karasa da sauri na ce Inna ina kwana yaya gajiya? Ta dan yi murmushi ta ce wato sai yanzu ki ka shirya ko Wahiddahh, wanne irin bacci ne yanzu mutun ya yi ta zama da yunwa har sai ciwo ya shige ki eye? 13 Inna yi hakuri na gaji ne da yawa bara na je na gaida Abba na mike. Ta ce wanne Abba kuma ai ya tafi gun gininsa, sai daı in ya dawo sai agaisa ina za ki ne na gan ki da jaka? Inna gun Hajara mana, kin manta. To amma kyaci abinci ko? Inna me akayi ne yau a gidan? Waina ce da taushe sai koko in zakici sai ki je ga shi can kan tebir in kuma bakyaci ga shayi can a flaks sai dai Hanne ta soya maki wainar kwai. Sauri nake Inna wainar ma ta isa na nufi tebur in a gurguje na ci duk da wainar ta yi masifar dadi haka na hakura na ce Inna kar a cinye wannan nan Inna dawo zanci amma Inna ke kikayi miyar ko? Inna ta yi dariya ta ce me ki ka gani? Inna miyar nan ta yi dadi na san Hanne ba za ta iya kamar ta ba na tafi Inna sai na dawo, karfa ki dade to Inna bazan dade ba. Na fita da guduna na samu Manu ya gama wanke motar na ce muje Manu don Allah. Ina ne Hajiya? Na ce masa gidansu Hajara, banyi tsammanin Hajara na gida ba, saboda me kace haka? dazu na gamu da direrban gidansu ya ce Hajara na asibiti a kwance na da fa kirji, me ya faru da Hajaran? Ya dan rude ganain yadda na rude ya ce wal wallahi ban tambaye shi ba, illah na ce zan gaya maki kuma saina sha'afa, shiga don Allah muje nwallahi baka kyautamin ba. Yaja motar yana faman ban hakuri ni ko sauraransa banyiba hankalina na gun Hajara, muna isa asibiti na fito to Hajiya na jiraki? Manu tafi na taho ka gayama Inna kar ta ga na dade ga dalili, an gama Hajiya. Tani mai aikin gidansu ta ce Hajiya sun tafi mai duguri yau da safen nan, me ya faru da Hajara ne? Uhm wallahi Hajara na son kasha kanta saboda Yusuf, saboda wa? Yanzu saboda Yusuf ra yi ma kanta rauni haka? Wai a ina Yusuf din nan yake ne? na fada cikin alamun nuna tsanata gareshi, Tani ta ce mayaudari ne kawai 'yan mata na wane suka fada irin wannan halin waye bai san Yusuf ba, wallahi Allah Wahiddah duk mace da ra yi arba dashi to fa ta fada tarkonsa. 14 Yaudarsu yake da kyan da Allah ya bashı ua kuma iya lafazinsa ga uwa uba Naira. Oh ni Wahiddah to tunda ta san halinsa me ya kaita ma soyayya da dan iskak haka irnsa.? Well kina da Lambar wayarsa? Bara na duba Jakarta baza'a rasaba wallahi su Hajiya har gida sukak kira shi su ji yadda za'a yi cewa ya yi shi bai mata alkawarin aure ba in ta ga zata yi aurenta ta yi shi bai shirya yin aure yan zuba hasali ma bai ga macen da tiyi masa ba. Karki so kia yadda ransu Alhaji ya baci amma da akayi mata fada shi ne bayan tafiyarsu ta dauki gilashi ta yiwa kanta rauni Allah yasa na shiga dakin ta dauko kwanuka na ganta a sume jinni na ta tsartuwa bansan sanda na kwalawa Auwalu direba kiraba yazo ya taimakamin muka kawo ta nan. ta Na kar6I takardar lambar tarhonta na shiga duba ta mutumin da ta kira suna Yusuf na karba na kuwa ga lambar tasa ce biyu daga tawa sai tashi cikin kunan rai na zaro hand set di na a jaka na daddanna lambobin da na shiga saurare da allu'ar Allah yasa yana nan. Jin muryarsa naji kamar ya zuban ta fasheshshen ruwan zafi don tsanarsa da nayi Hello baby ya ce min? cikin tsawa na ce kai ni ba irin wulakantattun 'yan matan da kake yaudara bane ni na fi karfin Baby ka ji ko, wacece ke mai min magana haka gatsal? Kana so ka san ni ko wacece? To ka zo asibitin tunawa da bayajidda na kudi imajansi dfaki mai lamba 112 kazo kaga condition din da kasa Hajara daga nan kaga ko ni wacece Just I give you 10 minute na kife layin ina huci da zage zage, Hajara ta bube idonta cikin zafin nama na karasa gunta na ce Hajara me yasa ki kayi ma kanki haka so kike ki kasha kanki sabda mutumin da baya sonki. Ta runtse ido ta bude ta ce Wahiddah da zan iya cire ciwon son Yusuf a raina da nayi ko don maganganun da ya fada ma su Hajiya, to me yanzu ki ke nufi? Bazan iya rabuwa da shi ba, na mike to kuwa kina tare da wahala wallahi in baki rabu da shi ba ina ga zamu 6ata akan..... ban kado kofar da akayi ba ko sallama muka juya gaba dayan mu ya salam na fada a cikin raina saboda ganin mutumin dana tabbatar shi ne Yusuf Rashida gaskiya AHah ya ce duk dan Adam tara yake bai cika goma ba, hakika 15 haka yake Yusıf ya cika goma sha daya a dauke dayan na yaudarar 'yan mata gaskiya bazan iya wassafa maki kyan Yusuf ba, amma gashi can a Hoto kin kuma san shi ma a fili, na barwa kanki wannan amsar. Ban tari numfashin kiba Wahiddah mijin nan naki wanne irin yare ne? nayi dariya na ce mahaifinsa dan Nijar ne mahaifiyarsa indiya ce ta ta fakistan kinji inda Yusuf ya yi wo kyau bisa kyau ina gaya maki nan na dake duk kda razanar da nayi, na ganin kyawunsana turbune fuska ya kal lan sama da kasa ya jijjiga kai ya wuce daya 6angaren da Hajara take ya ce me yasa ki kayi haka? Muryar Yusif take is natural. Na doka masa harara, ya yi murmushi ya ce mu fan bashi guri don Allah zai yi magana da Hajara, na ce baka isa ba in zsakayi magana kayi in bada da abin cewa hanya a bude take ba inda zamu disiba. Ya yi murmushi ya ce wacece ne wannan mara kunyar? Kaine mara kunya munafikin buzu ni na rasa jarabar da kika gani gun wannan ra motar ki ka like masa har ki ke neman kasha kanki na bude kofar na fita a fusace. Ya bini da kallo cikin takaici ya kalli Hajara ya ce wacece wannan? Ya danyi murmushi ta ce kawata ce aminiyata ce waddata mai dani 'yar uwarta Yusuf don Allah kace kana sona? Ya danyi jim ya kuramata ido cikin alamar tausayi da kuma fargabar gaya mat ba zai iya ba. Ta dan dora masa hannu kana ta ce Yusuf me yasa baka sona ta fada cikin raunanniyar murya? Ya dan dora nasa hannun kan nata ya ce Hajara bance bana sonki ba amma tun farko na gaya maki ni bazan yi aure yanzuba kuma bana so na yaudare ki shi yasa na gayamaki gaskiya ta gashi kinh dau abin da mahimmanci kowa zata zaiyi ni na ce ina sonki kuma na zo na yaudare ki kin jifa abin da iyayanki suka ce da kawarki don Allah karki kuma yiwa kanki illah a kaina ina labe a bayan kofa ina jinsu take na kuma tsanar Yusuf na koma kan tebier na zauna jiki na har tsuma yake saboda masifar da na shirya masa in ya fito. Bai jima ba ya fito ya kalle mu ya ce kwa iya komawa naga ya fada a gadarance na kalli Tani na ce shiga ina zuwa ta16 Kayya Inna a koshe nake ina Abban ya dawo ne? tun yaushe yana daki amma ina ga bacci yake nima bara naje na kwanta na huta kafin ta gama. Inna ta ce in an gama na tasheki, na wuce dakina ina rangaji ko kayan jikina ban cireba na fada gado na sai me fuskar Yusuf da maganganunsa ke min zarya a kunne na na runtsa idona na muskuta wanne mataki zan dauak akan wannan takadarin saurayin mai cin fuskar 'yan mata. Bara ta fito tukunna mu ga hukuncin da ya ce zai yanke da ya ke shi ne autan maza naja tsaki ni sam baya burgeni na lumshe idona bacci mai karfi ya daukeni. To Rashida mu je mu yi sallah sai kuma gobe in Allah ya kaimu maci gaba lokacin aikina ya zo. Rashida ta doki cinyar Wahiida ta ce me yasa ki ke garani ne surukar indiyawa.? Muka kwashe da dariya abin ma ba'a ne ko Rashida to na bar gayamaki labarin kuma sai na gayama Yusuf. Dan Allah yi hakuri Wahidda mu dai yi sallar muci gaba na yadda ana sallar La'asar sai mu tashi Please. To Rashida na saba baccin rana fa amma dalilinki kinga har daya da rabi ra yi muna hira. Sorry mam wallahi ian son jin labarin nan naku mai kama da Film ko almara. Ke ki ka sani kij i komai ba ta mike ta nufi shashinta ta ce tun da ke liman ya roka maki ni bai kosheni ba Inna da ka ta taki Rashida sai kisa na yi sabo gun Ubangiji na. Baki jiba Wahdda? Wai mana muyi hirar da daddare mana kafin mu kwanta, in kai Yusuf din ina? Um shi kuwa goshi ya ganni bakuwa ba zai barki mu sake ba? Koma sokoto in kinyi fushi Auwal na jiranki ba matsi in shi ya yadda nii ban yarda ba. Iye lallai yau nasan matsayina Wahiddah ta shige bandaki tana ma Rashida dariya, Rashida ta shiga kallon Hotunan Wahiddah da Yusuf duk da suka dauka ba marabar Wahiddah da mutanen Yausuf don sun saje tunda Allah ya tarfa ma garinta nono itama tana da gashin kamar nasu. Wahiddah ta fito ta ce oh Rashidda kya gaji da kallon hotunan mu wallahi, eh kumyi bala'in burgeni to mu ci gaba 19 Wahiddab sha mur, ta ce na gaya maki bana son sunan nan fa, to vi hakutn matar buzu. An kuma bara na ci abinci ko? Oh Wahiddah wanne abınci kuma bayan wanda mukaci to kari za'ayi ki ka sani ko na harbu, to Allah dai yaban hakuri danasa kaina wahala ta ce kin shirya, Wahiddah ta zame daga kan kujerar ta kishin gida akan kafet ta ce kin shirya ko naje nayi bacci na.? Na shirya yaya za'ayi da halinki na miskilanci kinga kuwa da sai na ci yusuf da yaki ba, ai naga alama bismilla. Wahiddah ta ce haka muka ci gaba har da jinyar Hajara iyayenta suka dawo amma muka shirya musu kan faduwa ra yi kan gilashi sati biyu suna cika aka salami Hajara batare da Yusuf ya kuma ziyartattaba. Hajara ta shiga halin damuwa wai duk yadda aka yi baya gari shi ya sa bai zo ba saboda haka don Allah in rakata taje gidan su ta dubo ko lafiya na ce ba da ni ba gada a ka bari ta je ita kadai ina jiranta a gida. Hajara ta ci uban ado abinka da farar fata sai ta dauki haske ta karbl mukullin motar gidansu ta fara ajiyeni sannan ta wuce ina ta faman tausaya mata. Nan na cimma Mustafa yazo da murna ya tareni har naji kunyar Inna shi duk ya manta na ce yaushe kazo ne? Ya ce "banjima da zuwaba." Inna ta shige shashin Abba ta barmu don ta kula da wata tsakaninmu da Mustafa. Ganin Inna at tashi Mustafa ya rioni nayi saurin kwace kaina na ce meye hakak Mustafa? Ya shafa hannuna ya ce wallahi kin gama rudani kinga yadda ki ka hade gaskiya bazan iya jiran har ki gama Jami'a ba, na ce ba muyi haka da kai ba fa. Ya ce to yava kike so na yi da sonki badama fa na tabaki sai ki fara kawomin wasu hadisan da ayoyi. Na ce to kayi hakuri kaban sati biyu na yanke shawara, ya yi dan tsalle ya ce are you seriouse? Na ce sure. 20 7 Ya fakaici idona ya sumbaci kuncına, nasha mur na ce bana so in dai kana so mu shirya, to yi hakuri dama nazo ne muyi sallama zan kos na sati uku a Abijan. Na ce Allah sa Aslheri a dai rike alkawari kar aga 'yan mata a manta damu. Ya ce haba Wahiddah, don dai ba ki san yadda nake son ki bane ace san samuna ne da aurenmu zan tafi can dakin da na huta. Na ce kar kaji komai ina jiranka ya bani tsarabar da ya kawo min na kayan sawa ran tsatstsu da kayan adon mata na silba nayi masa godiya. Ya sa na kira Umma sukayi sallama ya bata Dubu goma da kyar Inna ta karba nan yake gaya mata da shifa da Najir daya suke dole Inna ta karba ra yi masa fatan Alheri, ta koma dakinta. Na raka shi har gindin motarsa nan ya ka mo hannuna ya sanyamin zoben gwal mai shegen kyau ya ce na alkawari ne. Nan na ji son Mustafa ya kuma sarkafe min zuciya har naji ya kwalla ta tahomin ya shiga rarrashina da haka muka yi sallama cike da begwen juna har motarsa ta bace. Wato Rashida abin da ya faru da fHajara babu dadin ji haka ta shigo min wujiga - wujiga tana ta faman dure duren ashar ban tankamata ba har ra yi mai isharta sannan na ce "What up this time?" ta ce "Wallahi sai yau nasan Yusuf baida mutunci" na ce dafa mutunci ne dashi? Ta ce kinsan abin da ya faru again? Na ce banason ji. Ta fashe da kuka wato da najwe da wata rantsatstsiyar yarinya tana ta faman gurza kuka.... Akan me? na tambayeta cikin rashin kulawa na ci gaba da ninninke kayana Wahiddahhn na yarda wannan wata baiwa ce da Allah ya bama Yusuf, tana ta faman rokon sa wai ya aure ta, shi kuma shegen sai ma ya ce mata ba zai yi aure yanzu ba, matarsa har gobe bata zo ba. Na kwashe da dariya na ce “Sai kuka yi yaya?" tuninma dana dauki jakata na zazzaga masa masifa na fito kin san abin da ya yi mana? Ina zan sani. Dariya kawai ya yi, ya rako ni da ita har gindin mota ya ce min in gaida tsagalgalalliyar kawata da ta koyan hankali har na iya yi masa masifa, shi ya gode maki don ya san yanzu na san 21 matsayina a gunsa. Sai 'yan'uwantaka inda hah Hajara ta sa kuka mai tsanani, share ta na yi don na san yanzu muddin na tamka mata zan kuma lugwigwita mata zuciya, na kyale ta ta yi mai isarta, sannan na ce sai hakuri amma ni zan yi maganinsa na rantse da Allah. Nan na gaya mata zuwan Mustafa da alherin da ya yi min, ta shiga cizon yatsa rashin ganinsa. Da yamma bayan mun ci abinci ta tafi kan za mu hadu ranar Lahadi da yamma, zuwa fatin bikin auren kawarmu Jamila Salisu. Wallahi har na manta, gwara da kika gayan zan dai ba ki Gift ki kai mata, saboda ba zan samu damar zuwa ba, ranar za mu tafi Yola bikin Yaya Fiddausi. Wacece haka? Na tambayeta, baki santa ba, 'yar kanwar Hajiya ce To Allah kiyaye hanya, don Allah a rage son maso wani. Wai, ai wallahi ni da Yusuf kuma har abada, Na yi murmushi na ce ko da kin burge ni. Bayan tafiyar Hajara na kuma fakin Hajiya muka cigaba da hira, nan take gayan yaya Salima za ta zo jibi don tahowa haihuwa, don tun da ta yi aure shekara shidda kenan ba ta taba haihuwa ba, sai yanzu. Kuma ya zama dole ta taho goyon ciki, murna ta kama ni na hau tsalle. Inna na dariya ta ce "Kai Wahiddahh ba ki da dama, mai sunanki dai ba ta da kiriniya haka, salihar mace ce wallahi." al Nayi dariya na ce Inna yaya sunana ne? Inna ta ce babbar magana aikin san ba zan fada ba, saboda sunan surikata ne, amma kin san sunan baban nan ko? Wacce Babannan? Ta gidan mai Koko. Oh Hindatu? To haka sunanki yake, muna cewa Wahiddah ne don sakaya sunan, na ce dama sunana Hindatu? Ba kya so ne? Inna ta tanbaye ni Na fada jikinta na ce Inna ina son mana suna mai dadi haka wazai ce bai dace dani ba? Haka nan muka cigaba da hirarmu da Inna har magariba muka tashi muka yi Sallah, Abba ya sauko falo shi ma ya zauna muna kallon labarai. Bayan mun yi sallar Ishai muka ci abinci, ko kallon ban koma ba na ce masu sai da safe **** **** * *** 22 Ranar lahadi da yamma na ci uban kwalliya, hakika ni kaina nasan ban taba kwalliya irin ta yauba. Duk da ba wata wai sabuwar kwalliya bace a garin katsina amma ni a guna kwalliya ce ta cinyewa. Na gaya miki bana sa kwalli illa na shafa hoda da janbaki na Fafaul. Doguwar riga nasa hadaddiya ruwan madara mai ribi biyu da dan kwalinta, sam ban yafa mayafi ba, illah wani takalmi da na sa, shi ma fari flat mara dunduniya da farar jaka. Na feshe jikina da turaren Diamond, nan fa kamshi ya ziyarci ko ina da ina a gidanmu. Na dauko jakar Gift dina da ta Hajara na fito na samu Inna a kicin. Ta kalle ni ta ce da kyau 'yar Baba, amma don Allah ki kula da kanki, duk da na san halinki ki kuma ja motar a hankali kar ki wuce takwas. Na ce "To Inna na gode ni ma zan kiyaye" ta ce a dawo lafiya ice ko da kudi a hannunki? Da akwai Inna sun ishe ni. Manu ya riga ya wanken motata, karamar Choroki. Haka na zuba kyautar a bayan motata na bude na shiga na yi addu'a ta kare kai daga sharrin hadari da kuma gudun faruwar wani abu. Na dauko cingam din Hubba-Bubba na jefa a bakina na manna tabarauna hi-hi na ja mota. Na hau titi a hankali, na kunna Casset din Brandy cikin wakar CARE FOR ME ina tafe ina bin wakar sannu a hankali, har na zo babban Hotel din garin Katsina inda za'ayi liyafar. Motoci na gani na fada kala - kala,gun ya cika. Nan na tabbatar taro ya cika, na koma waje kusa da wani mai nama na yi fakin na ba shi ajiyar motar tawa. Ya ce ba komai Hajiya, insha Allahu lafiya za ki samu motarki. Na yi masa godiya na karasa da kafa. Tun daga barandar idanuwa suka yi min yawa, daga matan har mazan, nan na fara dabarbarcewa, don wallahi Rashida na tsani kallo a rayuwata, haka na dake na shige. To fa ai har gwara wajen da ciki, wallahi kasa motsawa na yi duk fitsarata, Allah ya taimakan Jamila da Ummi Abubakar ta hango ni suka nufo ni da murna. Sannan na saki dariya gaba daya hakorina na maka guda daya mai kyalkyali ya bayyana. Suna zuwa muka rungume juna, Ummi ta ce ya na ganki ke kadai, ba Hajara? Na ce Hajara tafiya ta same ta, amma gani madadinta. 23 Jamila ta ce lallai kam zo ki gayan sirrin leyan nan naki Wahiddahh ban yardaba. Na yi dariya na ce wallahi ba za ki daina halin ki ba, ina Mukhtar din naki? Ga shi can gun..... ta yanke maganar ganin tahowarsa da babban abokin Ango. Muna ta faman hira da Ummi, sam ba mu ga zuwan su Mukhtar ba, sai maganarsu na ji. To uwar yanga gani gabanki sai yanzu akaga damar zuwa bayan ke yakamata ki zama ta dayan. zuwa. Na dago kaina da dariyata, na ce kaina bisa wuyana, tuba nake na Jamila ba zan kuma ba. Π Muka kyalkyale da dariya muka shiga gaishe- gaishe, wallahi sam ban kula wanne suke tare ba sai da Mukhtar ya ce Wahiddahh "Meet my best friend Yusuf Saheed, babban abokina ne" kai kuma Yusuf "Meet my wife's best and only friend Wahiddahh Maddo Annurın tuskata ya gushe lokaci guda, na yi bala'in daure fuska wanda na firgita angon kansa da amaryarśa. Shi ko sai faman kallona yake yana murmushi ya ce "Barka da zuwa miss Wahiddahh, nice name. Na kalle shi sama da kasa na buga masa uban harara, na ja bayan Ummi da Jamila muka wuce. Mukhtar ya rasa bakin magana, sai kawai ya bi mu da kallo har muka 6ace. Ya kalli Yusuf ya ce "Kai yaya me ya hada ka da Wahiddah?" Yusuf ya soka hannayensa cikin aljihun wandonsa ya се "Ba komai, hasali ma ban santa ba in banda yau.""A'a Yusuf, ko dai ka yi mata halin naka?" "Allah ban santa ba, sai yau. Mu je kawai amma fa Mukhtar ina sonta wallahi, ta burge ni. Don ni ina son mace mai jan aji, da ganin wannan sarauniyar 'yan matan za ta yi jan aji. Mukhtar ya ce "Kayya, halinka nake tsoro. Wahiddahh ba irin 'yan matan da kake latsawa bane, gaskiya muskilacе. " Na sani wallahi ina sonta ba da wasa ba, Just na ji ta shiga raina" "Kai ai da ma kullum 'yan mata shiga ranka suke, ba za ka lalata mana zumuncin mu ba, tana da jan aji da ji da kai, don Family dinsu babban gida ne, kuma ana sonta kamar yadda ake sonka. 7 24 "I know kawai zan iya sadaukar da kaina gareta" "Amma ka ban mamaki, ashe akwai ranar da za'a samu macen da za ta canza maka ra'ayi haka? " Yusuf ya yi murmushi ya ce gaskiya da wata tsakaninmu, boye maka kawai na y, ko dayake ba da ita muka haura ba, kawai dai tarar fadan ta yi. Ni na san ruwa ba ya tsami banza, me ya hada ku? Wato akwai wata kawarta da take so na, ni kuma gaskiya ban taba jin na so yarinyar ba, har ta so hallaka kanta a kaina. To shi ne farkon haduwarmu da Wahiddahh, ta caccaba min magana. Da na ga tsaurin idon nata ya yi yawa na rama, to ka ji hadin mu da ita. Wacece kawar tata? Hajara sunan ta. Mukhtar ya dafe kai ya ce lallai ba za ka samu yin soyayya da Wahiddah ba sam ba zai yiwu ba. Yusuf ya rude ya ce "Why me'ya sa?" Yusuf, Hajara babbar aminiyar Wahiddahh ce, kamar Hassana da Usaina suke, "Iam sorry count me out, zo mu tafi" Yusuf ya bi Mukhtar, ba waní abu da za ka iya. Wallahi har ga Allah ina son ta. Mukhtar ya ce to gwarama ka cire son Wahiddahh ba za ta yarda ba, ka kulal da kallon da ta yi maka mana. No kar kace haka wannan ba wani abu bane Just ka gayan yadda zan yi. "Iam sorry ba zan iya ba, na san halin Wahiddahh. Allah ya bata riko, muddin ta ga na yi Supporting dinka na kaďe. May be ma ta yanke hurda da matata, ni kuma ba zan so haka ba sai dai ka je da kanka, in ta sauko to, zan iya yi maka kamfen. Dole Yusuf ya hakura, amma ya rasa yadda zai yi. Ni da Ummi muna zaune kan wani tebir muna hirarmu muna kallon yadda fuskar Yusuf ta shiga cikin damuwa, duk budurwar da tazo gunsa sai ya kore ta: Ummi ta ce wallahi kin burge ni, kin ga yadda Yusuf ke gara mata, na yi tsaki na ce su matan ne marasa aikin yi. Me ye abin so a gunsa. A'a Wahiddahh don dai bakwa shiri ne gaskiya guy din Classic ne..... a gunku ba. Ke fa? Allah ya kiyaye. wallahi Ummi sai na yi maganinsa. Uhum Wahiddah ki bi shi a hankali, yaron ya san kammu fa, wait and so once naki ina tsoronsa. 25 Ashe haka ya yi ma Hajara, ita ma ba ta jin magana, wallahi ta wani fannin ba shi da laifi, tunda ya gaya mata gaskiyarsa. Don Allah Ummi mu canza Topic please. To to uwar fushi bara na kawo mana Snacks. Ta barni ni kadai ina shan lemo. Ganina ni kadai ya baYusuf halin zuwa guna. Hannayensa cikin aljihun wandonsa Jeans, fuskarsa kunshe da murmushin yaudara ya ce "Mallama Wahida sarkin fushi na zauna?" Ban kalle shi ba balle na yi masa magana, hasalima sai na ci gaba da bin wakar da ake a rediyo. Ya tura kujerar Umma baya ya zauna ya zuban ido ya ce "Wahiddahh don Allah ki saurare ni.... meye haka ne?" na kalle shi a yatsine, na ce "meye tsakanin mu da kai har da zan kula ka." Wahiddahh Allah tun ranar da na dora idona a kanki a Asibiti, ke hasalima tun da na ji muryarki a waya na ji ina mutuwar son ki. Wahiddahh (ME TUMSE PYAR KARTIHA) wato ya fada da yaren babansa ma'ana yana sonaa. Ba kalleshi sama da kasa na sheke da dariya na ce, "Hhaba ba indiye, ba ka isa ka yaudaran ba ko kai ne Shashikafur, nafi karfin ka ka ja can ka karata da dabbobin 'yan matanká. Yaw lumshe ido cikin kunan rai ya ce "Na san ba za ki yadda da abin da na ce ba, wallahi ke nake so da raina da jinina." Wahiddahh ta ce "ni kuma ba na sonka da raina da jinina, ka san fa kai

Chapter 2 of 6