Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 3
Sai na zo din kenan, yanzu zan je gida, idan kin gama abin da kike yi ina jiran wayarki". Bayan Aslam ya tafi ita kuma Hanifa ta shiga gida, ta je dakinta tayi wanka sannan ta gyara gashinta bayan ta kammala duk abubuwan ta sai ta dauko waya ta buga gidan su Aslam. Aslam yana gaban waya yana jiran Hanifa tabugo.ai kuwa ringin daya sai ya dauka. Bayan sun gama gaisawa sannan sai ya cе: 22. Yanzu don Allah sai yanzu kika tuna dani? Kin san kuwa irin jiran da na yi miki? Tun bayan na dawo nazo na zauna jiranki. Har sai dana gaji naje nayi wanka na ci abinci amma shiru ba labari wai malam ya ci shirwa Ni da har na kwanta sai kuma na ji karar waya". ce: Hanifa ta kyalkyale da dariya sannan ta "Shi ya sa na ji tanata ringin sai da na dade sanan aka dauka. Ta kara da cewar: "To yanzu dai ka yi hakuri, zance ya wuce ba za'a kara ba". Hira ta yi dadi har basu san dayan dare ta yiba, sai da Hanifa ta kalli agogo tace da Aslam. "Wallahi Aslam dare ya yi fa. ga shi baccі nake ji". Aslam ya kalli nasa agogon sannan yace "Allah ni kuwa ba na jin bacci, kuma gaskiya kema ba za ki kwanta ba. Haka kurum ki yi bacci ki barni ni kuma ba na ji". "To kai ma ai sai ka kwanta, baccin zai zo sai ka yi kai ma". In ji Hanifa. "Lallai ma ai ni na san tun da ban jin baccin ba zan yi ba, ke ma sai ki hakura" cewar Aslam 23. "Dare fa ya yi gashi dare mahutar bawa kana kwanciya baccin zai zo" in ji Hanifa ta na magana kasa-kasa. "Gaskiya a'a ba za ki kwanta ba "Yana darıya ahankali ya fada. Hanifa tace "To shikenan" "Don Allah Hanifa hotonki nake so kamar guda goma masu kyau". Aslam kenan. Hanifà ta ce dashi cikin mamaki. "Haba dai guda goma, sai kace a film, ya ya za ka yi da hotona ni daya guda goma, ai sun yi maka yawa". "Wallahi ni da zaki bani film guda ma ina so". Cewar Aslam. "Gaskiya sai dai na baka guda daya ko biyu amma ai sun yi maka yawa". Hanifa ke fada. "Haba sun yi min kadan, ai ni guda talatin da shidan nan nake so". In ji Aslam "Guda talatin da........ fim guda fa kenan! Hanifa ta fada tare da nuna mamaki a muryarta. "Eh mana, to meye dan kin bani ko ban isa a ban ba?" In ji Aslam. "A'a ni na ce, ai ka isa har kayi yawa, sai kagansu". 24. Aslam ya dan dauke wuta kadan (Ya yi shiru ga barin zancé) sannan ya ce da Hanifa "Gaskiya ni ma na fara jin bacci, bari na barki mu kwanta haka". "Ka yi me? Ka kwanta lallai ma Aslam wasa ma kenan. haba haba nima fa yanzu ka hana ni na kwanta". Ta fada cikin nishadi ta kama shi a hannu "Ya nesa ya ce to shikenan ki je kema ki kwanta" inji Aslam ta ce da shi: "To ai ni yanzu bana jin baccin kuma gaskiya ba za ka kwanta ba kai ma". Aslam ya hakura da baccin suka cigaba da hira. Bayan wajen minti talatin sai Aslam ya ji suna cikin magana Hanifa ta yi dif, ya dan saurara shiru. Can sai ya ce a hankiali "Hanifa ya ji ba amsa sai ya dan bubbuga kan da dayan hannunsa ya kara kiranta "Hanifa. Hanifa da ya tabbatar Hanifa ta yi bacci sai ya hakura shima ya kwanta. Washegari da yamma sai ga Aslam. Ya zo gidan su Hanifa. Bayan sun gaisa sai ya ce da ita: "An tashi lafiya sleeping beauty?" 25. ta sha kunu sannan ta се: Wai don Allah jiya ya aka yi kayi bacci ka barni? Ya kalleta ya saka wata hadaddiyar dariya sannan ya ce: "Ni Hanifa? Yaushe ma muka hadu da kе bare na yi bacci na barki?". Ta dan yi masa kallon soyayya mai kwantar da hankali sannan ta ce: "Don Allah zancen gaskiya". Sannan sai Aslam yace tare da sassauta murya: "To Wallahi keki ka yi bacci kika barni akan line ina ta faman magana da fanfalakwai. "Ta dan rufe idonta tana dariya ta ce: "Wallahi ni bansan lokacin da ya dauke ni ba. Ni dai kawai natashi wajen shida da safe don ban samu sallar Asuba ba ma. Sai na ganni a kwance ni a can kan wayar a can". Suka kyalkyale da dariya sannan ta kara da. cewa: "Allah ya so nima na kulle kofata kafin na bugo wayar, da na san sai mama ta yi min fada ban yi sallar Asuba a jam'l ba, daman ai na gaya maka bacci nake ji, ka hana ni na kwanta". Haka dai suka sha hirarsu sai da aka kira sallar magriba suka yi sallama. Ya je masallacin 26. unguwar ya bi sallah, ita ma Hanifa tana shiga gida ta daura alwala ta yi sallah. Bayan an yi sallah ne sai suka ci abinci gaba dayansu har da Alh. Aminu. Da aka kare cin abinci sai Hanifa ta shiga dakinsu ta yi wanka.sannan tanufi dakin maminsu. Bayan ta zauna a kan kafet din falon mamansu sai mamansu ta fara da yi mata nasiha da bata shawarwari a harkar rayuwa Sannan sai ta kara da cewa: "Hanifa ina fatan kin fara tunanin mafita a harkar ki, domin kuwa na san Abbanku yana dab da gabatar da zancen aurenki, domin na ga ya fara damuwa da wadannan samarin da suke zuwa wajenki". Ta dan kalli indaHanifa take zaune à nutse sannan ta cigaba da cewa: "Hanifa ina kara jan.kunnenki da ki rabu da wadannan taron tsintsiya ba sharar, samarin yanzu karya ta cika musu ciki. Kuma yau inason ki gaya min duk cikin masoyan naki waye kika zaba ya zama mijinki? Don kin san dai ba sa miki ido za mu yi ki kawo mana lalatacce ba". 27. Hanifa tashiga kogin tunani yayin da mamansu tà bata lokaci domin ta yi tunanin ta a hankali. Tabbaş ina son Zubair, kuma ina matukar kaunar Aslam. Ni kuwa yanzu idan ban auri Aslam ba ya ya zan yi, gaskiya ina matukar kaunarsa ina kuma kaunar kasancewa tare da shi. Amma yanzu idan na ce zan auri Aslam, to ai shi yanzu ba aüre za'a yi mishi ba, yanżu ma masters dinsa ya ke yi level 100, kuma gashí, shima Aslam din yana kaunar ta sosai. Basu kara da komai ba sai ga babansu Hanifa ya shigo tare da Haj. Salamatu. bayan sun samu waje sun zauna sai Hanifa ta tashi za ta fita waje, sai Abbansu ya ceda ita "Ke Hanifa! Zo nan ki zauna ina da magana muhimmiya da ke" Bayan ta dawo sai ta koma inda ta tashi ta zauna. Sannan sai Abbansu Hanifa ya fara da salatin Annabi goma sannan suka yi addu'a aka shafa. Alh. Aminu ya dubi Hanifa ya ce: "Kin gama makaranta, gashi har sakamako ya fito, yanzu kuma sai abu na gaba 28 kin riga kin san babu zancen makaranta sai dai idan mijin da za ku aura yayarda. Ya dan gyara muryarsa sannan ya ce tare da kallon matayen nasa a lokaci daya: "Ina son ki gabatar min da wanda ki ka zaba a matsayin abokin rayuwar ki ba da bata lokaci ba idan kuma duk maneman naki ba su kwanta miki a rai ba, to kada ki kwari kanki ki fito ki gaya mini. Ina son ki gaya mini abin da yake ranki". Hanifa hankali duka tashe ta ce a cikin rawar murya: "Baba ina da shi" Baban nasu ya ce "To Alhamdulillah". Bayan dan dakikun da suka wanzar da shiru sai Alh. Aminu ya ce: "To kafin na kai ga nisa, ina son na san kin san wani yaro wai Zubair?" Hanifa ta kara. sunkuyar da kanta kasa sannan ta ce: "Eh Baba! Na san shi yana zuwa wajena, dan uwan su Salimat ne" sai mahaifin nasu ya sake cewa: "To shi ne ya aiko da magabatanshi wajen kawunki Sani, suna nemar wa dansu aurenki, ina so na ji kin amince da shi ko kuwa 29 akwai wani daban. sai a sanar da su tun kafin lokaci ya kure". Hanifa kwalla ta cika mata ido taf ai ba'a kara sakan ba sai da hawaye ya cika mata fuska Bata ce komai ba sai ma dada sunkuyar da kanta kasa da ta yi. Hanifa ba ta san yanda za ta yi ba, a ranta ta san tana son Zubair tana ganin kuma za ta iya zama da shi don ya cancanci a so shi. To amma Aslam ta san ba aure za ayi wa Aslam ba yanzu, kuma ita ta san ba barinta za a yi a zaune a gida ba, dole ta zabi Zubair. Haj. Salamatu ce da ta ga shirun ya yi yawa ta ce da ita: "Ya ya dai 'yar Hajja, ba ki yi magana ba". Hanifa ta daga kanta sannan ta ce: "Ina son shi, Baba" Haj. Amina ta ce da ita: "To Hanifa tunda kin.amsa kina son shi sai ki rabu da wadannan samarin da suke sallama da ke" Dukkansu suka watse aka bar Hanifa a zaune. Sai da ta gama nazarin ta sannan ta tashi ta nufi wajen Haj. Salamatu. 30. Haj. Salamatu ta ce da ita daman yanzu nake son na aiki'Zahra ta turo mini ke a falon Hajiya. Bayan sun dan taba hira sai Hanifa ta kara yin shiru tare da ajiyar zuciya. Haj. Salamatu ta rarrashe ta tare da yi mata dabarun manyan mata har sai da ta gaya mata abin da yafi tada mata da hankali. Haj. Salamatu ta yi nazaria kan matsalar Hanifa sannan ta ce da ita: "To, 'yar diyata ga wani taimako zan baki ki yi kokari ki aiwatar da shi" Ta tashi ta shiga cikin dakinta ta fito mata da takarda da biro sannan ta koma ta zauna a. kusa da ita kan kujera ta fara da cewar: "Hanifa ko da yaushe ki kasance mai mika lamarinki ga ubangiji" zaki ga biyan bukata a cikin lamarinki". Tadan saurara kadan ta ce: "Yanzu ga wata addu'a ina so ki yi ta cikin yardar Allah za ki ga biyan bukata. A game da biyan bukata an samo Hadisi daga SA'AD BIN ABI WAKKAS(R.A) cewa Annabi mai tsira da aminci ya ce (Addu'ar nan da Annabi Yunusa ya kira Ubangiji da ita lokacin 31. da yake cikin kifı, duk mutum musulmi wanda ya roki Allah da ita a kowace bukata, to Allah zai amsa masa). Turmizi, Nasai Hakeem ne suka ruwaito. "LAA'ILAHA ILLA ANTA SUBHANAKAINNI KUNTU MINAL ZAALIMIN" Ita dai wannan addu'a manyan malama na musulunci sun yi bayanin hanyoyi iri dabandaban wajen amfani da ita, to amma daga ciki ga wasu muhimmai guda uku. 1. Hanya ta daya mutum ya yawaita fadar wannan addu'a dare da rana. Safe da yamma a ko wanne lokaci da nufin Allah ya biya masa wata bukata da ta dame shi. 2. Hanya ta biyu, mutum ya dinga karanta addu'ar sau dubu daya da dari daya da goma sha daya (1,111) sau uku kullum wato safe, yamma da daddare, sannan ya nemi biyan bukatar da ta dame shi a duk lokacin da ya karanta adadin. 3. Hanya tą uku, ita ce mutum ya yi sallah raka'a biyu da fatiha da ko wacce sura ta sawwaka gareshi sannan a sujadar karshe wacce daga ita sai tahiyya sai ya karanta ita addu'ar sau arba'in da daya (41) kuma ya roki bukatar tasa, sannan sai ya dago ya yi tahiya ya yi sallama, kana ya yi istigfari da salatin Annabi (SAW) sannan kuma ya maimaita fadin bukatar tasa. In sha-Allah za ta biya kamar dai yadda hadisin ya nuna. Kuma wadan nan 32. hanyoyi da malamai suka bayyana wacсе đük mutum ya bi duk daya ne. Allah ya'sa mu dace amin. Haka kuma, dai game da ita dai wannan addu'ar an samu Hadisi daga ABDURRAHMAN BIN AUFIN (RA) cewa: ANNABI mai tsira da aminci ya ce: "Hakika addu'ar nan ta dan uwana Annabi Yunusa (AS) akwai mamaki acikinta, farkonta Hailala ce, tsakiyar ta tasbihi ne sannan kuma karshen ta furuci ne da zunubi. Kuma wani mai fama da tsanani, ko bacin rai.ko bakin ciki, ko bashi, bai roki Allah da ita sau uku a rana ba,sai Allah ya amsa masa. DAILAMI NE YARAWAITO. Hanifa ta gama rubuta duk wannan bayani da takardar da Haj. Salamatu ta kawo mata, sai ta kuma karanto abin da ta rubuta don tabbatar da bata samu bata ba. Bayan an gyara batan da kuma kara yi mata bayani sai Haj. Salamatu ta kara da cewar ga wata kuma, "Idan kin samu isasshen lokaci ki dinga yin ta itama." Idan mutum yana da wata bukata muhimmiya a game da sha'anin aiki ne, ko 33. aure, ko neman arzikı. ko kuma kashe wata magana. ko sarauta. ko tafıya ko kuma ko wacce irin babbar bukata, to sai ya yı wannan sallah tare da wanan addu a kamar daı yadda manzo (SAW) ya nuna mana. An samo Hadisi daga ABDULLAHI BIN MAS'UD (RA) cewa: daga ANNABI mai tsira da aminci ya ce: wanda ya yi wannan sallah raka'a 12 sallama 6 a dare ko rana, bayan ya gama sai ya yi yabo ga Allah madaukakin sarki, da kuma salati ga Annabi mai tsira da amincı. Sannan kuma sai ya yi sujjada. yana halin sujjadar sai ya karanta: 1 Fatiha kafa (bakwai 7) 2. Ayatul kursiyu (bakwai 7) 3 Wanan addu'a (10) goma: "LAA'ILAHA LAASHARIKA WALAHULHAMDU ILLALLAHUWAHDAHU LAHU,LAHUL MULKU YUHYI WAYUMITU WA HUWA ALA KULLI SHAI'IN QADIR".10 4.. Ita kuma wannan addu'ar sau (daya 1). "ALLAHUMMA INNIY AS'ALUKA 'BIMА AAQIDIL IZZI MIN ARSHIKA: WA MUNTAHAR RAHMATI MIN RITAABIKA, WA ISMIKAL A'AZAMI WAJADDIKAL A'ALA WAKALIMAATIKAT TAMMAT" 34. Sai kuma mutum ya fadi bukatarsa yana halin sujjadar. kana kuma sai'ya dago ya yi tahıya ya yi sallama dama da hagu. Annabi mai tsira da aminci ya ce: "Kada ku sanar wa da wawaye wannan addu'a domin kada su dinga amfani da ita barkatai. kuma za'a amsa musu IMAM HAKEEM ne ya rawaito (Wannan addu'a babu shakka babban makami ne wajen biyan bukatu, don haka ya rage mai bukatu ya dukufa. Bayan sun gama suka rufe da addu'ar biyan bukata, suka tashi. BABI NA HUDU Bayan kwana biyu Hanifa ta tambayi abbanta tana so, za taje gidan Aunty Sakina ta kwana biyu. Abbansu ya amince mata. Ta sanarwa da mamainsu ita ma ta ce: "Sai kin dawo, а се muna gai da su da kyau 35. Hanifa ta shirya ta tafrgıdan Sakina "Salim ne ya kai ta da shi da abokınsa Nazir. Hanifa na zaune a gidan baya Bayan sun isa gidan Sakina, sai suka shiga suka sha hira sannan da yamma ta yi Sakina da Hanifa suka shirya suka tafi well-care Suka sayi kayan dadi, su lemo da sauransu. Sannan Hanifa ta sayi fim na hoto. ta sa a camerar ta, da yake ta taho da ita. Bayan sun fito daga well-care sai Sakina tafara daukan Hanifa a hoto, har idan sun ga gidamai kyau a hanya sai an tsaya an dauka a wajen sannan su wuce, har sai da suka karasa Badawa Hanifa na kaunar ta ga ta faranta wa Aslam rai shi ya sa ta yanke shawarar ta dauki hoton fim guda ta ba shi. Sun sami kwana biyu ana daukan Hanifa a hoton sannan aka karar dashi. Hanifa ta je beirut road ta ba da a wanke mata a AGFA. Ranar Juma'a su Hanifa da aunty Sakına suka tashi da wuri don su yi 'yan girke-girken su Matar yayansu ta haihu wato. Ta haifi da namiji an sa masa sunan kakansa wato Amin. 36. Bayan sun gama hada kayan abincı sai kuma suka fada wanka. duk suka gama suka shirya cikin wani brown cotton lace. Anko za a yi duk yan uwa har da iyayensu da iyayen matan yayansu. Bayan an hadu a gidan suna aka yi shagali mai kayatarwa. Sai da aka yi sallar magriba sai Hanifa tace da Sakina tana so, za ta je gidan su Halwa. Sakina ta ba ta mukullin motarta ta ce mata ta dawo da wuri saboda su wuce gida. Da isarta gidan su Halwa sai ta ci sa'a ta tarar da su tare da Aslam da kannen Halwa a falonsu suga hira Halwa ta yi murna kwarai don ganin Hanifa bazata. Suka gaggaisa sannan ta shiga gai da mutanen gidansu Halwa Da ganin hotona sai Aslam ya ce lallai lallai shi kam bazai ba da hotuna ba, daman guda haka ya ce yana so. Halwa tana ta mitar ita ba'a kawo mata ba amma sam Aslam ya hana ta ko guda daya. 37. Da ta samu 'yan dakiku sai ta ce da su za ta koma, saboda auntyn ta tana jiranta a gidan suna Sukayi sallama ta ja motarta ta dau hanya. Yayın da Aslam ya kasa tsaye ya kasa zaune sai murnar daukan hotunan nan yake don ya tabbatar da Hanifa na son shi sosai. Bayan su Hanifa sun koma gıda sun kammala komai za su kwanta sai Sakina ta ce da Hanifa. "Hanifa zabinki na auren Zubair ya birge ni, Allah ya ba da zaman lafiya. Domin kin ga yanzu a gidan biki har an gayyato meeting ranar wata juma'ar saboda a fara shirin bikinku". Hanifa ta kalle ta a hankali sannan ta се da ita: "Amma kin san me aunty Sakina? Wallahi har yanzu ina jin son Aslam a raina. Kamar ma ba aure za'a yi mini ba. ga shi ko Halwa na kasa gaya wa zancen Zubair don ina ganin za ta gaya wa Aslam" Sakina ta ji tausayin kanwar tata sannan ta ce da ita cikin muryar ban baki: "Kada ki ji komai Hanifa Allah zai kawo komai cikin sauki, amma dai ya kamata cikin week din nan ki gayawa Halwa duk abin da kike 38. ciki ciwon ya mace na ya mace ne, sai ki ga ma ta Bà ki hadin kai kun samu hanyar nusar da Aslam yadda al'amarin ya ke Zancen auren Hanifa ya koma hannun manya sai shirye-shirye ake yi. An sa ranar daurın aure ya kasance wata biyu. Yanzu Hanifa da Zubair ko da yaushe ana tare don ko da a ofis ya ke yana bugo mata waya. su dau awa daya ko biyu kafin su ajiye. soyayyar su abar sha'awa ga kowa. Tabbas shawarar Aunty Sakina ta yi amfani, domin yanzu Aslam da Hanifa kamar wa da kanwa haka suka zama. Soyayyarsu tana nan lafiya kalau, sai dai ance fadan da ya fi karfinka ka mai da shi wasa. Haka ma 'yan gidan su Halwa, sun mai da kansu kamar 'yan dangin su Hanifa, da su ake shirye-shirye komai na bikin Hanifa. Biki ya rage sati biyu aka kawo kayan lefe da na sa lalle. Kaya sun hadu kamar ba da kudi aka sayo su ba. Komai dozin biyu aka zuba mata, a kalla akwatin sun kai ashirin sai kuma kanana guda biyu da kita shima guda biyu. Ashirin da hudu kenan haka aka kawo su a cike da kaya. ko wanne sai an danne kafin arufe. 39. Gwal ma set hudu aka zuba acikin da manya guda biyu sannah kirar white daimon guda daya da kuma half set shima guda daya. Awarwaro mai guda shidda-shidda quda uku. Agoguna guda goma sha-daya. .Da rotar ta sabuwa dal a cikin ledarta. A bayan motar ma wasu kaya ne akwati biyu inji ang Kayan ready made ne wasu kuma 'yan dubai ne sannan da wata dalleliyar sarka (fashion peart) da (wrapper) dallar America guda biyu kudio dinki. Katin biki ma daga Swizerland aka bugo shi mai kyau da tsari. Babu wani (events) da yawa. Kamu ranar Laraba, sai tea perty ranar Alhamis, ranar Juma'a a yi yini sannan a yi mothers night a Lebanon Club. Ranar Asabar za'a kai amarya sai ranar lahadi da daddare akwai Dinner party a Chinese restaurant. Zubairu Auwal, kyakkyawa ne amma ba fari ba ne chocolate colour za'a kira shi dona garin bakake shi fari ne kal. Alhaji Auwal Naira, sunan mahifinsa kenan, suna zaune a Mayu road. 40. Allah ya yi wa mahaifin Zubair arziki, mutumci. kyau da tausayi ga kuma uwa uba rikon amana da son mutane. Alh. Auwal haifaffen kasar sudan ne, yana da matarsa tun auren fari, ko yaji ba ta taba yi ba, Suna da va ya guda hudu Amal. Sadiya (Sunan mominsu). Abdulhamid sannan Zubairu. Amal ita ce babba a gidan tana aure acan Sudan din a dangin mahaifinta. Sadiya ita ma ta yi aure tana zaune a matan fada road tana auren dan shugaban kasar Niger. Abdulhamid kuwa yana Swizland da matarsa Basma, yana aiki a swiz Bank. Alh. Auwal ya dade da baro kasarsu Sudan, domin yanzu akalla sun doshi shekara bakwai a gidansu na Ibrahim Dabo road, kusa da Aliyu Ibn Abutalib. Zubair kuwa a can aka barshi har sai da ya gama kara tunshi ya kuma kama aiki yanzu ma ya zo ganin iyayen shi ne, to Hanifa ce ta tsai da shi domin tun ranar da ya ganta a asibitin nan ya san ya samu matar aure. Zubair ya kasance da mai biyayya da ganin girman na gaba da shi ga Addini, kamar dan Sudais haka za ka ji idan yana karatun Kur'ani. 41. Hanifa an zama amare, ko ina sai labarın auren' ta ake yi. kowa kuma yana musu fåfan alheri da samun 'ya'ya na gari. An gama gyara gidan da Zubair zai sa Hanifa a ciki.gida ne da ya amsa sunansa na gida, a Zoo road ya sayi gidan a hannun kwaran nan mai sunaTahir (mamallakin Tahir Guest palace). Gida ya tsaru kamar dai wani rantsatstsen fadar shugaban kasa. Surar dawisu shine ainihin abin da idonka zai dinga hango ma, kamar dai yanda yake baza gashin nan nasa kore. A farkon gidan garage dinsu ne mai kunshe da motoci na gani na fada da kuma katon fili. Akwai wata hanya wadda aka zuba kwalta ya nufi cikin gidan. Idan ka bi kan kwaltar ahankali sai ta kaika bayan gidan wanda babu komai a wajen sai wani tafkeken swimming pool da kuma garden a gefe. A cikin garden din babu abin daba'a shuka ba Apple, lemo na tsami da na zaki, gwanda, Ayaba, Abarba, Baure, Peach, Kankana da sai sauransu. Ko wanne dan itace ya sakata ya wala a bangarensa. 42. Akwai boys Quarters (BQ) a can gefen gidan an zagayeshi da 'gini. Dakuna uku ne da falo babba ko wanne daki akwai Air condition da kuma fankar sama. Bangaren matar gida da na maigida abin sai dại a yi shiru, don ba magana sai talking. Hanifa ta sami dakuna guda shida, da dakin yara guda biyu na maza da na mata. Akwai dakin baki (Guest room) guda daya da babban falo a ciki da bandaki. Akwai kicin dinta gudabiyu daya а samadaya akasa. Kowanne dauke da kaya fal, ba masakar tsinke. Bangaren maigida kuwa, wato katon falo ne, wanda idan da fili ne kawai za'a iya gina gida mai dakuna uku har a samu kicin da bandaki. Kujerun falon ko wanne set dinsa guda goma shabiyu ne da tebura a tsakiya da gefe. Fitilun, falon ma abin kallo ne. Akwai dakunan kwana. guda biyu da kuma sito a gefe. An kawo amarya bayan da aka gama hidimar biki da kuma bidi'o'l na malam Bahaushe. Bayan iyayenta sun dadayi mata nasiha da fadan zaman gidan miji sai kowa ya watse. Yan siyan baki su shida aka bari. Da Halwa 43. daRabi'at Aliyu Mohammed, Asma'u Abba Garko da Halima Murtala Gaya, Hafsát Ibrahim da Aisha (Indian girl). Angwaye suka shigo aka kammala sayen baki da kuma sai da fura da yakę ba su samu damar zuwa sai da furar ba, sai angwaye suka biya su kudinsu. sun samu dubu dari biyu da hamsin. Suka yi sallama da Amarya abokanen Zubair da kuma motar gidan su Hanifa ta kwashe su sai gida. Gida ya zama daga Ango sai Amarya. Ranar da Hanifa ta kwana bakwai sai ga Halwa da kanwarta Rahma, suka zauna suka yini suka sha hira. Hanifa ta yi mugun kokari don har sai da za su tafi sannan ta ce da su "don Ailah ku ce ina gai da mama da Aslam". Ranar da Hanifa za ta koma Zari'a suka zo sallama da Hamida. Bayan sun gama hirarsu za su tafi sai Hamida ta ce da ita: "Hanifa girma fa ya kama ki, sai hakuri sannan ki dage da addu'a da kuma bin mijinkı Ga wannan Addu'ar ki dinga yi ta zama a wuri ce" "SUBHANAKAL LAHUMMA WA BI HAMDIKA, ASH-HADU ANLA'ILAHA ILLA ANTA ASTAGFIRUKA WA ATUBU ILAIКА". 44. Kuma ko da yaushe ki kasance mai biyayya da ganin girmån mai gidanki". Hanifa ta ce da yayarta "To insha Allah zan yi biyayya gareshi, Allah ya kiyaye hanya. Hamida ta kara da cewa". "Ga wani sirri kuma da zan gaya miki, saboda ki samu jin dadin zaman aure. Kin ga Hanifa ki lura da kyau zaman aure sai da kwantar da hankali. Kuma kada ki kuskura ki kasance mai cewa mijinki "Daga ina kake?" ba ke ce mai iko da shi ba, shi yake iko da ke. Ki barshi ya yi abin da yake so, idan kika takurawa kanki saiya daina dawowa gidan, baki kuma da katabus. Abin da ya fi ki yi masa tarba ta musamman tare da nuna damuwarki ta rashin dawowar tasa da wuri, sannan idan ma tambayar ce sai ta biyo baya. "Dan jira ba'a gama abincin ba har yanzu". Ya dawo daga aiki a gajiye da kuma yunwa, wannan ba dai-dai ba ne, Allah ya taimaka. "Sulaiman ya sayo wa matarsa karima katuwar sarka da sabuwar mota mai kyau, wancan satin. Wayyo ina ma nima na samu kamar ta". Za ki sa shi ya zama kamar ba ya gabatar da aiyukan da ya kamata a kansa naki". Hamida ta gyara zamanta sannan ta ce daita: 45. "Abin da ya kamata ko da yaushe shi ne; ki kasance mài godiya a gareshi, mai yawan addu'a gareshi. Ko wannen ku yana da hakkı a kan dan'uwansa, ku kasance masu ba da hakin juna. Idan abu ya taso masa ki kasance mai kwantar masa da hankali maı yawan damuwa da bukatunsa Ko da yaushe ku kasance masu goyan bayan junanku a ko ina. Ku kasance tare da juna ko da yaushe. kuma ko da wane lokaci ku kasance masu samun abin da kuke so. ki gaya masa bukatarki cikin kwanciyar hankali. shi ma ki tabbatar ba shi da damuwa". Hamida ta kalli agogo ta ce da Hanifa tare da mikewa tsaye: "Kada dare ya yi mana a hanya Amarya, sai mun yi waya ma karasa abin da ya rage mana. Asha amarci lafiya". Hanifa ta koma cikin gidan su ta fara shirye-shiryen tarbar Angonta domin lokacin dawowarsa ta kusa. "BARKA DA SHANRUWA" 46. Tammat. Taku Siyama (mrs. Idris) 1 40h ANNIVERSARY !!! MUNA TAYA MAIMARTABA SARKI ALH. ADO BAYERO (CFR LLD. JP) (SARKIN KANO) MURNAR CIKA SHEKARA 40 A KAN GADON SARAUTA. RANAR 11. Ga watan OCTOVER 1963-2003 ALLAH YA JA ZAMANIN SARKI a t DAGA: lyalan maimartaba Sarkin kano (maza da Mata) "A YI SALLAH LAFIYA!!" 47. An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya

Chapter 2 of 3