Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 3
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels HAUSABOOK.COM HNL BILKISU ADo BAYERO 2 HANIFA BILKISU ADО BAYERO Harafi Publlshers KaAure Ni BILKISUHAMUHD BABI NA UKU Washegari sai ga Umar da abokinsa Usman. Usman shi ne wanda sukaje gidan sa Jiya ba yanan. bayan sun gaisa sai suka shiga hirar su. Umar ya ce da Hanifa da Usman: "Hanifa gaskiya na dauko abokin nan nawa ne don ya zo mu yi magana dani,da ke a gaban shi". Ya dan kalle su a lokaci daya sannan ya kara da cewa: "Kamar yanda kika riga kika sani ne, ina sonki sosai da sosai,kuma ina muradin ki zama matata, saboda haka nake ganin ya kamata ki tsayar min da magana daya, wallahi sam bana kaunar ganin wani ko wasu, suna zuwa wajenki. Bana son kina kula wani bayan ni. Gaskiya Hanifa ki gaya min gaskiyar ki a kaina, domin ni aure nake so mu yi. idan kin amince dani zan turo manya na gidanku da neman iri". "Hanifa ta amsa masa da cewa: "to kamar yanda ka tambaye ni, to dole na gaya maka gaskiya ta. Ka san dai ni budurwa ce ba bazawara ba saboda haka ban 1. 1 yi tsammanin masu neman aure na zan rabu da su ba. Kai ma layi kawai ya kamata' ka bi kamar kowa amma ba ruwanka da zancen na daina kula kowa. Wa ya san gobe ai sai Allah "Usman ya kalleta ya ce: "Ni madai na goyi bayan ki Hanifa.ka ci gaba kawai da gwada sa'ar ka, idan Allah yayi matar kace duk iya yawan masu zuwa wajentá dolesu hakura ka dauka. Saboda haka mun barki lafiya". "Umar ya dan ja numfashinsa tukunna sannan ya ce da su gaba daya. "To, sai mu tafi din. Sai da safe". Hanifa da ta shiga gida sai ta dauro alwala tazo ta ta da sallah, ta yi salla raka'a biyu, bayan sallama sai ta kara da ALLAHU ALLAHU RABBIY LAA 'USHRIKU BIHI SHAI'AN sau bakwai. Sannan ta yi fatiha kafa daya da salatin Annabi goma. {Wannan addu'ar ana yin ta ne ayayin da wani abu na bakin ciki ya faru ga musulmi, ko kuma mutum yana cikin damuwa. To sai ya dinga karanta ita wanan addu'ar kafa bakwai. To Allah zai yaye masa duk abin da ya dameshi. Saboda an samu Hadisi daga ASMA'U BINT UMAIS (RTA) cewa: Annabi mai tsaira da aminci ya ce da ni "Bari in sanar da ke wata 2. addua'a da za ki dinga karanta wa sau bakwai a duk lokacin d'a wani abu na bakin ciki da bacin rai ya sameki". Abu Dauood, Ibn Majah ne suka rawaito. Hanifa ta koma gidansu, bayan kwana uku aka koma makaranta. Yanzu basu da isasshen lokaci nasu na kansu sai na karatu {Final exam} din da za su rubuta an kafe musu {time table}. Ya kasance kullum su Hanifa ana class area, sannan ga practical dinsu da aka fara. Kullum Hanifa tana karanta Bismillah kafa (786) da asuba dab da bullowar alfijir tasha a ruwa {ta tofa}. Duk wanda ya jure yin wannan addu'ar hakika zai haddace duk abin da aka koya masa a kansa. Ana karanta wa yaro ko yara a ba su har tsahon kwana bakwai mujarrabi ne. Lokacin jarrabawa ya kawo kai Hanifa har rama ta yi, saboda ko abincin kirki ba ta iya ci sosai. Aka dauki wata guda ana rubuta jarrabawa sannan ranar {final paper} dinsu aka yi send off party da yamma bayan send off kowa ya bi iyayensa ko 'yan uwansa suka tafi motar Ya Aslam suka shiga bakinsu kowa har kunne an kammala secondary school. 3. Ranar speech & prize giving day ta zo duk 'yan candy suka taro, an dinka masu wata riga irin ta graduation koriya da ash (ruwan toka) a gaban rigar. Ranar kowa yana cike da farin ciki da annashuwa har sauran 'yan makarantar ma saboda a ranar aka yi visiting. Hanifa ta samu kyaututtuka sai ka zata don ita aka gina makarantar saboda takarbi lambar yabo ta kowanne bangare. Kyautar ta kuwa an bata sama da goma. Hanifa ta ga gata sosai kowa ya nuna mata kauna, yayyanta maza da mata kowa ya bayyana. Mazan sun zo da matansu da 'ya'yansu hakana matan duk da 'ya'yansu da mijinsu suka zo mata, kowa da tasa kyautar zuwa gareta. Bayan an watse aka kuma ware gangar bature a rediyo aka saki kidan Celinedion da Janifer Lopez. Hanifa na zuwa gida bayan ta yi Sallah sai ta dauko carbinta ta yi addu'a kamar yadda ta saba, sannan ta fara addu'a ga mahaliccin kowa da komai. Hanifa ta yi godiya ga Allah, ta yi kirari ta yabi Annabin rahma ta kuma roki alherin duniya da lahira. 4. Hanifa ta yi sujjada bayan ta yi salatin Annabi goma sai ta fara da: "Rabbana laa tu'akhidhnaa' in nasiina au akhta'naa. Rabbana wa laa tahmil alainaa isran kamaa hamaltahu alal ladhiinamin qablinaa. Rabana wa laa tuhammilnaa maa laa taaqata lana bihi, wa afu-anna waghfir lanaaa war hamnaa, Anta maulaa naa fansurnaa alal qaumil kaafiriin". Sau uku sannan ta kara da salatin Annabi goma ta dago ta shafa fatiha. Tun da ta kwanta ba ta tashi ba sai da aka kira sallar Asuba. Tana tashi ta shiga ta yi wanka ta zo ta yi sallah, ta riga ta saba duk lokacin da ta tashi daga barci sai ta yi wanka tun a makarantarsu. Ta kan hada da wankan janaba a yayin wankan ta, kasancewar bata iya tuna mafarki idan ta yi sai ta yanke wa kanta wanka kafin salla, saboda gudun kada ta kamu da janaba yayin baccin ta bata sani ba ta yi şallah. Bayan tabi masallacin unguwarsu aka idar da sallah, sai ta dauki kur'aninta ta fara bitar karatu. Bayan an kwana biyu sai Hanifa tashirya domin ta tafi Zaria tare da yayarta Hamida, suka shirya, Zaria ta diba. 5. Dasuka isa Zari'a sai suka tarar da mijin Hamida ya tafi'Yola sai bayan sati daya zai dawo Sannan Hadiza wata makociyarsu take gaya mata zancen auren kanwarta Hafsisy wanda ranar laraba za a yi kamu. Tare da aiko mata da goron bikin. Sun shirya zuwa bikin ita da Hanifa sannan suka shiga cikin gari da yamma. Ranar kunshi suka je gidan da ake kunshin amarya suka tarar da gidan a cike. kamar hadin baki sai Hanifa ta fita kofar gidan don ta dan tattaka, tana fita sai ga motar Umar a kofar gidan Hamida, ta yi matukar mamakin hakan sosai. Hanifa ta karasa wajen Umar da fara'arta. ta ce da shi: "Yallabai ka ban tsoro fa" ta dan rike habar ta tare da girgiza kai sannan ta sake cewa da shi: "Don Allah daga ina kake, kuma yaya aka yi kasan ina nan? Umar ya dan kauda kai ya gyara muryar sa sannan ya ce da ita: "Daga Kano nake, kuma wajenki na taho. ba ko sallama aka taho shi ne ni kuma na je gidan Sakina ta gaya min kin taho nan ta kuma bani address din nan". 6. Hanifa ta yi dariya sannan ta cе: "Wallahi ba haka ba ne Umar, kawai dai tafiyar ce ta zo amma ai ranar Juma'a zan dawo. Umar ya dada gyara tsaiwarsa sannan ya ce tare da sanyayar da muryarsa "Hanifa kin dauke mini tunani na gaba daya, kin gama tafiya da ruhina ina tabbatar miki da cewa akalar rayuwa ta a hannunki take, ki yarda da ni don girman manzon Allah na zo na dauke ki na mai da ke gidana a matsayin mata ta ke ce kadai burina a rayuwa". Hanifa duk abin nan tana sauraronsa yayin datake kallon kasa, sam hankalinta yabar jikinta, tana dai jin maganar da yake yi samasama. Ta dago kanta daga kallon kasa sannan ta ce da Umar. "Ina son. ka bari sai ranar litinin da yamma kaje gidan mu,ka same ni, sai mu karasa magana". Umar ya kawo wani (envelop) ya bata sannansukayi sallama da junansu. Ko da Hanifa ta koma bata tsaya a gidan bikin ba kawai sai ta tafi gida ta shiga daki ta zauna ta hau tunani. 7. A gaskiya akwai abin da Hanifa take hangowa a rayuwarta, duk data san ba ta da wani 'yancin yin abin da ta ga dama, tun da tana da iyaye da na gaba da ita A kan kanta da ita take da iko da kanta, wannan yana cikin abin da ta ke bukata a wajen irin mijin da y kamata ta yi rayuwarta da shi Na farko dai ya kamata ta samu wanda yake sonta saboda ita, wato don wacece ita: ya iya kasancewa tana da kudi, amma ba kudin nata kake so ba. Ka sota idan sunanta Zainab, ka sota saboda ita Zainab ce, mummuna ko kyakkyawa. Sannan kuma ta sami namijin da zai kasance mai sa ta farin ciki a ko da yaushe. Tabbas ko wacce mace tana da burin mijin ta ya kasance mai kyautata mata da faranta mata. Ba wacce za ta so ta bata lokacinta da namijin da zai sa ta bakinciki a ko wanne lokaci, duk tsahon lokaci. Farin ciki yana sahun farko a rayuwar mu ta 'yan Adam, masu 'yanci Tabbas kuma akwai bukatar yarda a tsakani. yarda da juna ya taka rawar gani a neman nagari. Ko wanne mutum. mace ko namiji, yaro ko babba yana neman wanda zai yarda da shi. Tana matukar bukatar kasancewa da namijin da za ta kasance ya zamar mata madogara a duk lokacin da ta bukaci wani a kusa daita ko wanda za su yi magana da. 8. Surar datafi bukata a wajen maza kuwa ya kasance ba wai mai kiba ba,' ko ramme ko muna kasusuwa. A'a wanda yakeda nama a jiki. Mata suna bukatar maza masu murdadden jiki. Ya kansa mace ta ji ta zama cikin sanin cewa atsaretake a kowanne lokaci kuma a ko inakuke tare. Hakannan wanda zai kasance ya sa ta ta dogara da kanta ta tsaya a kan kafarta.mata sun kasance masu kosawa da mazan da duk wani motsin mace sai sun saido a kai. Namiji ya kasance mai yawan kawo sabon salo na rayuwa,ko wasanni da sauransu. Akwai kuma abin da ya fi tayar mata da jijiyoyin hankali yanda ta lura da mazan yanzu da basu dauki hulda a koda yaushe, tana mai neman namijin dazai kasance mai hulda da ita a ko da yaushe, wala'Allah a waya ko a wasika, ko da ba ku yi magana ba idanun ku za su fidda muku maganar a tsakaninku. Mata suna saurin gajiyawa da mazan da suka kasance ga sunan ne dai. Sannan kuma Namijin da zai kasance mai yarda da kansa. Namijin da ya kasance ko da yaushe yana jin kunyar jikinsa, (musamman can kasa) yana zubar da kansa a wajen mata. Rashin yarda da kanka yana nufin, yana kuma nuna cewa ba ka cika isasshen namijin ba. 9. Kuma yana nufin ba za ka iya daukar nauyinta ba Ya kuma kasance wanda zai karbi jikin ta a yanda yake, ramammiya, mai kiba, a'a katon mazaunai. manyan mama. Abin da yafi sauki a zaman takewa shine kai namiji ka koyi yabon matarka da jikınta. yanda ta zama ta yı kyau.kayan sunyi mata kyau ko da yaushe don a zaman tare ba'a girma kuma ba'a gajiya. Kamar yanda ka dauke ta a matsayin wacece ita. * * * Ranar da Hanifa ta koma gida da yake sunje kano da wuri, saboda a gida suka yi sallar la'asar. Wanka kawai ta yi sai ta shirya ta dauki mota suka tafi gidan su Halwa ita da Zahra. Da isar su gidan su Halwa sai ta tarar da ita tare da mamansu a falo suna kallo. Halwa ta tashi ta tari Hanifa tana nuna matukar farin cikinta da dawowar Hanifa ta riko.hannun Zahra suka dawo wajen mamansu Halwa. Hanifa ta durkusa ta gaishe da mamansu Halwa. Suka tashi suka nufi bangaren su Halwa suka zauna a falo, Halwa ta tafi kicin ta hado musu abinci da abin sha kala-kala. Ta dawo. 10. Bayan sun kammala sun yı sallar magriba sai ga Aslam ya shigo yana shigowa kofar gida ya ga motar gidansu Hanifa ya san cewar ta zo. Ya shigo tare da sallama. sannan ya ce da Hanifa yayinda ya ke neman zama: "Ranki ya dade. Gimbiyata. saukar yaushe?" yana fada yana dariya irin ta hadaddun 'yan maza. Hanifa bata amsa masa ba sai dai tayi kasa da muryarta sannan ta ce da Aslam: "Barka da dare an dawo lafiya?" ba ta ko jira ya amsa ba ta fara kade mayafinta tana niyyar yafawa tare da dauko jakarta da take a gefe. Halwa tana kallonsu bata ce komai ba don ta san kanun zance, ai ba su yi aune ba sai Aslam suka gani a gaban ita Hanifar gwiwa biyu a kasa yana faman daga hannunsa duk biyun,. wato yana neman afuwa sannan ya samu ya.ce da muryar tausayi: "Don girman Allah Hanifa kada ki yi mini haka, wallahi bani da lafiya ne shi yasa ban zo ba. Don girman soyayyar ki da manzon Allah ki koma ki zauna". 11- Hanifa duk tausayinsa ya kama ta tabbas Aslam yana kauna ta. don Hälwa ma ta gaya mata cewar baı da lafiya Ita kuma ta yi masa hakan ne kawar don ta nuna masa bata ji dadın saba alkawarın da ya y mata ba Ya ce zai je Zari'a amma ko mai kama da shi ba ta gani ba Aslam ya zauna a kasa a kusa da Hanifa sannan ya ce da Halwa dan bamu waje sahibata". Halwa ya ja hannun Zahra suka shiga cikın dakinta. yayin da Hanifa da Aslam suka kasance a falon Aslam ya ce da ita yana mai sanyayar da muryarsa: "Hanifa ki yi Hakuri ina kwance Ulcer ta kayar da ni. shi yasa ban cika miki alkawarin da na yi ba Hanifa ta saki fuskarta sosai sannan tace da shi: "Wallahi Aslam na hakura komai ya wuce. ya ya jikin naka?" ya ce da ita: "Na samu sauki sai dan abin da ba'a rasa ba" "Allah ya kara sauki ya kuma kare ka da karewarsa". 12. Aslam da Hanifa suka ware ana ta diban hira, har'sai wajen tara saura kwata sannan su Hanifa suka kama hanyar gida ita da Zahra. yayin da Aslam da Halwa suka yi musu rakiya har waje, wajen motarta. Ranar laraba ne.har Hanifa tayi shirin kwanciya sai ga Salim ya shigo, yake ce mata ga Zubair ya zo yana waje a falon baki. Hanifa ta dauki irin hijab dinnan mai ribi biyu baki da yalo ta saka mayafin ma mai kala biyun ne amma rabi da rabi ne ko wanne zaka iya sawa. Ta dauki lemo da kofi guda biyu ta sa a kan faranti, sannan ta tafi dakin da aka ce mata. Ta shiga ta sami Zubair a zaune a tsakiyar 3 seater. Ta ajiye lemon a gabansa sannan ta koma gefe ta zauna tana murmushi. Bayan sun gaisa ne, ta zuba lemon a kofin ta sha kadan sannan ta zuba masa. Suka samu lokaci suna hira sannan sai Zubair ya ce da Hanifa: "To Hanny ni zan gudu don dare ya fara yi kada su mama su ga kin dade. Hanifa ta yi dariya sanan ta ce da Zubair: "To mai sanyina Allah ya kaika gida lafiya 13. suka yi sallama cikın kauna da begen juna suka rabu da alkawarin dawowa jibi Ya bata wasu kaya a cikin kwali guda biyu ya ja motarsa ya fita daga gate din. yayin da ita kuma Hanifa ta kama hanyar cikin gida yayin da kayan suka riga ta shiga. Ranar da Abdul ya zo ya ga kamannin Hanifa na tsoro wanda bai taba gani ba a rayuwarsa. Sai da suka dau awa biyu yana bata hakuri a kan abin da ya faru. Hanifa dai dama da biyu ga sonsa da ya fita a gabanta ga kuma haushin yanda suka yi ranar party. Dole suka rabu a sanyaye. Ranar da ya zama wata daya dai dai da kammala makarantar su Hanifa yaya salisu ya zo suka tafi zaga gari da salim da Hanifa sannan auta Zahra aka je well-care da see sweet & bakery aka kwaso kayan zaki da Ice cream. Suna dawowa gida aka yi bajet na kayan kwalama wasu kuma aka saka a freezer don karsu narke. Aka sha hira aka yi kallo har dai sai da dare ya tsala sannan aka kwanta. 14. Hanifa abin duniya ya sha mata kai sosai, domin yanzu duk kullum sai ánzo ance ana sallama da ita. Idan dare ya yi kuwa ta kwanta ko bacci bata iya yi don tsabar tunanin halin da take ciki. Har bata sanin lokacin da bacci ya ke saceta. Hanifa babban abin da yafi damunta a rayuwa bai wuce yanda aurenta zai kasance ba, ta san yanzu lokaci ne kawai iyayenta suka bata, kuma tana da yakinin ranar duk da Abbansu ya yunkuro bata da katabus. A ranta da jikinta ta riga ta san cewa dole dai miji daya za ta kawo a aura mata. To amma a gaskiya Aslam daZubair duk kansu sun cancanci zu sama abokan rayuwarta. Duka wasu samari da manyan mutane da suke zuwa wajenta ita basa gabanta sai su biyun nan ne kawai suka ciri tuta. A can wani garin kuma a cikin zuciyarta, banda tunanin halin da za ta shiga idan bata auri Aslam ba ba bu wani tunani. "Gaskiya ina son Aslam ina muradin na zauna tare da shi, kamar yanda na san haka ne a nasa zuciyar". Ranar ta kasance Juma'a mai taken ta na babbar rana. Bayan an sakko daga masallaci sai ga Aslam da Sani. Wato babban abokinsa, da kuma Halwa. 15. 1 Halwa ta shiga suka gaisa da mamansu Hanifa sannan 'aka kaiwa su Aslam ruwa da lemo mai sanyi. Halwa ke sanar da ita cewar suna so ta raka su gidan yayarsu wato Ilham. Hanifa ta ce: "To Allah ya sa mama ta barni". Hanifa ta fita, ta sami mamansu ta gaya mata. Sai maman nasu ta ce: "A'a Hanifa, ki zauna a gida sai dai wata rana kya je ku gaisa" Hanifa ta fara shagwaba tana cewa: "Haba mama, ga Halwan nan fa tana daki, yanzu sai na koma nace kin hanani zuwa? Ai baza ta ji dadi ba tun da ita tana ganin duk mun zama daya a wajenki". Mama dai ta ce ta amince a je amma a dawo da wuri: Bayan sun fita sai suka shiga bayan mota suka nausa. Daman sai da suka kara yin kwalliya a dakin Hanifa kafin su fito. Tun da Hanifa ta shigo motar Aslam ya kasa dauke kansa daga kallon ta, har kara saita madubin motar yake yi a gaskiya shigar ta Hanifa 16. ta tafi da ruhin Aslam ba Aslam ba ma duk mai rai zai so ya kalli wannan tauraruwa ya kara. A haka dai suka karasa gidan Ilham suka tarar da ita tana kallon film din Hausa na kamfanin Maishunku Movies, wato film din sa na Tangarda. Ilham ta yi murna sosai da zuwan su, ta karbe su cikin farin ciki tare da nuna musu kauna. Gidan ya hadu sosai kamar ba a Nigeria ba, hatta da kicin dinsu na girki sai da aka sa (AC air condition) guda biyu. Sannan ga wani inji a kusa da (cooker gas) wanda ake saka shi daga sama, in dai ana girki aka bude shi to duk hayakin da turirin girkin zai bi ta ciki, ba zai wanzar da shi a kicin dinba. Gidan ya yi masifar yi wa Hanifa kyau. Ilham ta ringa nunawa Hanifa kauna, tareda haba-haba da ita. Nan da nan aka kawo musu kayan snack da lemo da soyayyun kaji. Aka dauko musu album suka kalla, da lokacin sallar la'asar ya yi suka je suka yi salla a dakin Ilham, sannan Ilham ta hadawa Hanifa sha-tara ta arziki. Cikin kayan da Ilham ta bawa Hanifa har da Less da super holland sannan ga takalmi da 17. jaka da daı kayan kwalliya irin na mata har da turare Bayan an yi sallar'magrihba sai suka fito domin a kai Hanifa gida. Aslam ya ji dadi sosai shima don yana ganın duk wanda ya yı wa Hanifa hidima kamar shi ya yi wa Suka kaita gida sannan aka sauke Sani a gidansu shima. Ya Aslam da Halwa suka dau hanyar gida suma. Bayan Hanifa ta shiga gida sai ta zarce dakin Haj. Amarya kamar yanda suke gaya mata, ta kai mata kayan da llham ta bata ta kuma gaya mata yanda aka yi ta na ciki da bata labarin irin haduwar da gidan ya yi da kuma irin mutumcin da ta nuna mata.. Washegari da daddare sai ga Abdul ya bayyana, bayan ya aika ta fito sai suka koma falon gidan suka zauna. Ba su dade da zama ba sai mai gadi ya zo ya sanar da Hanifa cewar ta yi bako. Cikin sauri tace da Abdul tana zuwa ta fito don taga mai neman ta. Tana fitowa sai suka yi ido hudu da Aslam. Aslam yana jingine da jikin motar sa, yana kallon ta cikin sakin fuska sai ya ce da Hanifa: "Ya malama ina gajiya? Ya ya kuma mutan gida?" 18. Ta kalleshi yayın da ta lumshe idanun ta ta ta ce da shi: "Ina nan kalau da ni, kazalika mutan gida duk lafiya. Ya naku 'yan gidan ina ka baro min Halwa?" ya kalleta ya ce ita tare da murmushi a fuskarsa: "Nabar miki Halwa a gida, don har ta shirya zamu taho na ce kuma na fasa zuwa da ita. Ko a dawo lafiya ba ta ce mini ba ta koma gida, na san sai na koma zan tarar ana yi min fushin nata" ta bude baki za ta yi magana kenan sai ga Abdul ya fito daga falon, don ya gaji da jiran gawon shanu. Aslam yana ganin Abdul ya fito daga falon sai ransa ya yi masifar baci, nan da nan ya canza fuska kishi ya bayyana a tsakiyar kwayar idonsa. Sannan ya kalli Hanifa tare da cewa "Wannan kuma fa" muryarsa da alamun damuwa a cikinta. Abdul kuwa can gefe ya tsaya kusa da motarsa, alamun cewar zai tafi, don ba zai iya kwasar kwandon bakinciki ba. 19. Hanifa ta ce da Aslam: "Ban gane abin 'da kake nufi ba" don ta lura da yanda fuskar sa ta canza don ganin Abdul, kuma ta lura da yanda yake magana a wani gadarance, shi yasa ita ta dan canza fuska amma ba wai nuna wani abu ba. Aslam ya се: nufi ba" "Oh! Ai dama ba zaki gane abin da nake Hanifa ta yi 'yar dariyar mugnta fa ce: "To daman ya ya za'a yi na gane abin da kake nufi" Aslam ya gama lura da cewar ta mayar da abin na wasa sai ya ce da ita yana mai kau da kai daga kallonta. "To shikenan tun da ba ki gani ba, to yanzu dai ya za'a yi?" sai ta ce da shi: "Ka. dan jira ni, naje na sallame shi na dawo!" ko amsa bai bata ba sai ya koma mota ya zauna. Ta juya ta nufi wajen Abdul wanda ya riga ya gama sarewa da al'amarin Hanifa har zuciyarsa 20. ta yanke masa shawarar ya saurara haka nan tun bai zo yana da na sani bа. Ta karasa wajen Abdul, ta bashi hakuri sannan ta ce da shi: "Abdul ba dai tafiya ba na ga ka dawo wajen mota" ya yi dan murmushin yake ya ce da ita: "To Hanifa! Ai gwanda na tafi tun da mai wuri ya zo sai mai tabarma ya nade ai. Da alama da wancan za'a dai-daita?". Ta yi kamar bata san mai yake nufi ba ta kau da kai sannan tace: "To Abdul na gode ka gai da mutan gida, sai da safe". Daga haka sai Abdul ya shiga motarsa ya ja. Hanifa kuwa ta juya zuwa wajen Aslam. Wanda a lokacin da Hnaifa take wajen Abdul zuciyar Aslam har neman fadowa kasa take ga wani kululu da ya zo masa wuya Ta yi kamar minti biyu da tsayawa a wajen Aslam amma sam bai nuna alamun ya san ta karaso ba ma, sai da ta ga bai da niyyar amsa mata sallamar da ta gabatar tun zuwan nata sannan ta dan buga motar tare da kara 21. wata sallamar. ya dago a hankali ya amsa tare da cewar "Har ya tafi ne?" ya dan saki fuskarsa ba kamar farkon ganin Abdul bа. Ta amsa masa da cewar "Ya tafi" Suka dan taba hira sannan Aslam ya ce "To rabin ran! Zan gudu sai yaushe kenan zan ganki?" "Sai wata rana" in ji Hanifa. "Yaushe ne kuma wata rana?" cewar Aslam yana dariya "To ai ni ban san mezan ce maka ba, ai ni ko da yaushe ina nan kawai dai sai ka zo" Hanifa ke fada a cikin farin ciki. Aslam ya ce da ita: "To okey!

Chapter 1 of 3