Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 3
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels HAUSAВООК.COM BILKISU HNI 1 ADO BAYERO HANIFA BILKISU ADOO BAYERO Harafi Publlshers KaAure Ni BILKISUHAMUHD BABI NA DAYA "Allah sarki Aslam koyanzu yana ina? Allah shi ya bar wa kansa sani" Hanifa ce take zancen zuci. Tana zaune a kan dan gadon su na bacci na karfe, amma maimakon gado mai hawa biyu, kamar yadda na kowacce makarantar kwana yake kasancewa. Wannan nasu mai gudadaya ne. Gadajen guda biyar ne a jere, ko wanne da dan karamin lokarsa a jikin bango kusa da gadon. Dakin babba ne, ba wai can can ba. Idan mutum ya shigo {Orange house} sunan gidan nasu kenan a makarantar, a kwai dakuna guda goma a jere {room 1- 10} ko wacce da kofar shigarsa. Idan ka shiga akwai {wardrobe} ta ajiye kaya ta raba dakin gida biyu,ya zama kowanne dakin akwai {part 1& 2}. ko wanne {part} akwai gadaje biyar-biyar. Makarantar su Hanifa sananniya ce a. birnin Dabo, Kano Model Private Secondary School, kenan. Amma kawai mutane suna kıranta da Kano MODEL. Makaranta ce ta gani ta fada domin ta masu da shi ce {Masu kudi), akwai karatu sosai a makarantar, da kwararrun malamai. Malaman makaratar sun hada yare da yawa a kwai farar fata, akwai Hausawa da Yarbawa kowa da irin fanni da yake karantar wa. 3. Idan aka shiga makarantar daga gåte na biyu sai wajen {Parking} ajiye motoci na malamai, daga bangaren hagu ofishin shugaban makaranta ne a kusa da shi na Vice dinsa ne. sai ofishin guardian & council, daga daya bangaren ofishin malamai ne da kuma store din makaranta a wajen. Bangaren dama kuwa wani katon filine na gaske wanda kana iya hango coach din wasanni. da kuma wajen basket ball. Akwai 'yar tazara kadan zuwa ajin dalibai. Daga an wuce na 'yan aji daya sai na 'yan aji uku. Ko wanne aji akai azuzuwa uku wato (ABC) (3A BC). Dayan sashin kuwa ajin 'yan aji biyu ne da 'yan aji hudu sai sashen karshe 'yan aji biyar da 'yan aji shida amma akwai Library a tsakanin su. Akwai laboratories a dan bayankadan da azuzuwan dalibai. Masallacin makarantar ya na gefen yamma akwai tafiya daga (classes). Masallacin kato ne sosai har da library aciki,an tanadi kur'anai da hadisai da dai sauran litattafan addini Daga wajen masallacin sai an yi tafiyar a kalla minti biyar sai ka bullo ga Dining hall dinsu inda a nan ne suke cin abinci da gabatar da tarurruka idan za'a yi wani wani wasa ko wa'azi. 4. Daga bayan dinıng din kitchen ne in da masu aikin abincin suke sannan da wanı dakı dabandaki saboda amfani (Kitcheners) din. dalıbai. Daga dining hall ana hango hostels din A kwai houses da aka rarraba kowanne dalibi akwai dakinsa da bandakunansu a gaban ko a bayan dakunan. Hostels din guda shida ne kowanne guda uku suna kallon junansu. Akwai pink house da yellow house da orange house ko wanne yana da A da B (Pink A da pink B) (yellow A da yellow B) (orange A da orage B). Hanifa tana orange B. shine na seniors orange A kumana Juniors. Hanifa ajinta biyar, tana karantar Account wato ajin 5A amma SS2A shine abin da ake amfani da shi a yanzu. Suna term dinsu na biyua SS2 saboda haka, sun yi matukar ba da himma ne kawai a karatunsu basa wasa sam. Daman ba irin makarantun da dalibi zai tsaya wasa ba ne, don idan yaro ya ce wasa zai yi sai ya dau na karshe don makaranta ce da kowanne dalibi yace idon ba ka yi ba ni waje, kowa kokari yake ya wucedan uwansa. Saboda haka babu wanda zai yarda daga kallon ruwa kwado ya yi wa mutum kafa. Hanifa ta fitone daga tsatson wani hamshakin mai arziki ne, wanda ya yake da 5. mutumci da sanin ya kamata mai suna Alhaji Aminu Abubakar Alhaji Aminu yana zaune ne a cikin garin kano, a unguwar Babura road. Yana da mata biyu da 'ya'yansu. Hajiya amina da Hajiya Salamatu Hajiya Amina itace uwargidan Alh. Aminu auren saurayi da budurwa suka yi. mata ce mai hakuri da juriya ba ta da yawan magana samsam. Kyakkyawa ce ta fita cikin taro, kallo daya mutum zai yi mata ya tabbatar wa da kansa, an yi rububinta da tana 'yan matancinta. Tana da 'ya'ya biyar biyu maza uku mata. Salisu shi ne na fari; sai Sadiq wato Abubakar sunan kakansu uban Alh. Aminun, sai Hamida da kuma Sakina, sai 'yar autarsu Hanifa. Hajiya Salamatu, Amaryar Haj. Amina Kamilalliyar mace ce, mai ilimi da kuma kunya. Tana da 'ya'ya uku, Abdulra'uf sai Salim da kuma autar gidan gaba daya wato Fatima Binta. Alhaji Aminu haifaffen garin kano ne, baban su Alh. Abubakar shi ne limamin unguwar sharada, yana zaune da matarsa Hajiya Zainab, ita ce mahaifiyar su Alh. Aminu. Alh. Aminu sun kasance su biyar ne a wajen iyayensu, Alh. Aminu shi ne babban sai Alh. 6. Sani yana binsa, sai Haj. Hafsatu ta ukun su da Alh. Kabir da kuma autarsu Ummul kursum. Alh. Aminu babban dan kasuwa ne yana zuwa irin su Dubai, China, da su Morocco yana shigo da kayayyakin amfani na gida, kitchen da kuma office. haka zalika yana shigo da sarkoki da agoguna irin fashion da kuma gold. Alh. Sani yana aiki a First Bank of Nigaria Manager ne shi a wajen. Haj.Hafsatu ta yi aure amma tana aikin jinya a asibitin Nassarawa dakin 'yan haihuwa. Alh. Kabiru Custom ne shi Portharcourt yake aiki da matrsa Haj. Asabe. Auta kuwa Ummul Kulthum tana matakin karshe a jami'a, tana karanta political science. Salisu shine babba a gidan su Hanifa yana zaune a Tarauni Quarters da matarsa Hajara da dansu Amir. Sadiq yana zaune a unguwar 'yan bulo da matarsa Ikram da 'ya'yansu guda biyu (twins) Hassan da Hussein. Duk kansu harkar kasuwancin ubansu suka bi hanya. Sai Hamida yanzu haka tana da 'ya'ya uku, Hasiya, Kabir, sai A'isha suna zaune a Zaria da mijinta Ahmad likita ne a Teaching hospital. Abdulra'uf yana zaune a Bauchi da matarsa Rahma da 'ya'yansu uku Pamela, Saddiqa da Yusra, yana aiki a Bank of the north reshen su na Bauchi state. 7. Sakina tana aure a Badawa GRA da danta Naifal, mijinta yaha aiki a Total gidan mai, sunansa Aliyu. Yanzu gida sai Hanifa da Salim da Zahra'u su ya rage, suna karatu Salim shekarar sa Ashirin da daya Hanifa kuma shekararta goma sha shida, sai Zahra tana da shekarar tara. Alhaji Aminu mutum ne mai son sakewa tare da iyalansa, ko da yaushe suna tare, koda office ya je yana Allah-Allah yamma ta yi ya dawo, domin ya kasance tare da iyalinsa, domin suna matukar kyautata mashi da kuma ririta shi, suna kwantar masa da hankali. Haj. Aisha da Haj. Salamatu sun hade kansu sun zama tsintsiya madaurinsu daya, babu abin da suke boye wa junansu, kullum kansu kara haduwa yake yi. indai ba 'yan uwa na jiki ba ba'a tantance 'ya'yan wannan da 'ya'yan waccen, domin 'ya'yan suma kansu a hade yake. A takaice dai ga bakin mutane, idan dai ba'a gaya maka ba sai dai ka kira su a Ya da kanwa ba dai kishiyoyi ba. Ba irin kishin wannan zamanin ba da za'a zauna kamar jahilai. Daga kishiya har 'ya'yanta su sa amarya a gaba kamar dabbobi, wai su ana kishin amarya ta zo. Idan dai ba Jahilci ba ina ruwan 'ya'ya a taya uwa kishin, ai ko a nan an yi asarar kudin tara da kudin laraba. Kishin dabbanci kuwa don bakin 8. hali har yaran ma sai a hana su gai da matar ubansu, ni a ganina ai ba wáńi suke yi wa ba sai uban nasu, shi mahaifin nasu, ai shi ya kawo Amarya to ina laifin amarya, kuma rabon auren ina za'a kai shi? Ga na 'ya'ya? Ni ina ganin da uban nasu yaje neman mata, har bacın rana a kai ga haifo la'anannu, ai a yi auren yafi. Wannan kuskure ne babba mu ce za mu yi kishin dabbobi idan mun hana 'ya'yan zuwa ga matan ubansu za mu hana su matan uban nasu haihuwa ne? kuma ma dai 'ya'ya ai na kowa ne da wanda ya haifa da wanda bai haifa ba, duk dai ubangiji muke bautawa. shi ne kuma ya bamu 'ya'yan to takamar ta menene? Idan kai ka haifesu to kai ne ka halicce su? Hanifa tana makaranta a kano Model, yayin da salim ya shiga Jami'a a Uni maid (university of Maiduguri). Zahra kuwa tana Excel primary, class 5. HANIFA AMIN, yarinya ce kyakkyawa, son kowa kin wanda bai samu ba Hanifa Allah ya yi mata kirar jiki mai kyau ita ba doguwa ba can haka nan ta zarce matakin gajeru. Fara ce tas da ita, ga hancin dogo har baka, bakinta dan dai-dai fuskarta. Gashin kanta ba shi da yawa sosai amma duk da haka idan ta sake shi yana kwantawa a kafadarta. Kyan Hanifa sai wanda ya gani. Ga ta da son addininta don ta sauke 9. alkur anı da litattafai da dama tun tana (JSS class): Hanifa ba ta da makusa a jikinta dá halinta sai dan abin da ba za'a rasa ba, don mutum tara yake bai cika gomaba. Kawayenta a makaranta sarauniyar kyau suke ce mata. Tana da kawaye a makaranta da dama don ba ta da abokin fada, idan har ka kaita makura ta gwammace ta gayawa babba ya yi maka magana a kan ta tanka maka. Hanifa tana da farin jini a wajen samari da duk wani cikakken namijin da ya hada ido da ita. Har ta kai yanzu a garin kano duk wani saurayi da ya san ya hadu, ya kwana ya tashi da sanin Hanifa Amin. wala'Allah yana takama shi wani ne, ko kuwa babansa wani ne, ko mamansa wata ce, da wanda ba kowan kowa ba ma, ina tabbatar wa da mai karatu yana daya daga cikin masoyan Hanifa ko a boye ko a bayyane. Hanifa tana da wani hali wanda duk wanda ya santa to ya santa da shi. Wannan hali kuwa shine, duk wanda ya tako kafarsa ya zo gidansu ko makarantasu, ko ya aiko ko ya rubuto yana sonta, to bata taba wulakanta mutum. Da yawan kawayenta a makaranta suna ce mata wai zara ne da ita, wasu kuma su cе mata ya ya za'a yi duk kyan nan nata ta tsaya tana kula tsamaye da 'yan karya? Wasu kuwa cewa suke yi da su ne da matsayinta, kyanta da kudinta wallahi ko dan waye a garinnan sai sun 10. ga dama su saurareshi, kuma ko da ace ya samu zasu dan' kula shi to sai sun ja masa rai, sun kuma ja masa aji, sannan ya kaskantar da kansa a wajensu, ita kuwa duk wanda ya tare sai ta yi murmushi ta ce "to ai ku kenan, ni kuma ni ce!" iyakar amsar ta da su kenan. Hanifa ta yi makarantar ta ta prinary a Bennie nursery & primary school. Yarinya ce mai kokari sosai, har yanzu da ta shiga SS 2 ba ta taba daukar na uku ba daga ta daya sai ta biyu. Idan ta yi na biyu ma sai ta shafe term guda tana kukan bakin ciki wani term din kuwa sai ta dau kofi don tsananin dagewa. Saboda kokarinta kowa yake yaba mata, ko da yaushe iyayenta suna cikin shi mata albarka. Tun daga aji biyu na karamar Secondary Jss 2 Hanifa samari suka yi mata caa aka, kowa ya zo idan ba ita ba sai dai rijiya amma idan an rabu: ba wanda yake kara tuna guga ma ballantana a tafi ga batun fadawa rijiya. Duk da samarinta amma ba ta yadda da zancen soyayya ita dai karatu shi ne a gabanta. A lokacin da ta shiga SS 1 ta yi wani saurayi Anwar, ya zo da kokon bararsa gabanta, Allah da ikonsa sai tashi daya ta ji tana son sa, amma sam karatunta ne a gabanta sai dai a bayan fage to ya samu dan wajen rakabewa zuciyarta. a 11. Allah ya dorawa Hanifa wani hali a cikin ranta bangaren soyayyarta da ma' śsoyanta. Nan da nan idan kun hadu kana sonta za ta ji ka shiga ranta haka nan idan ta samu wani za ta canza ra'ayi daga kanka. Amma da wuya masoyinta ya gane hakan don ba za ka taba ganin canji ba a wajenta, don tana ganin idan dai ta yi hakan, mutane za su ce ta zama maci amana, hakan kuma ko kadan ba yin kanta bane halinta ne. (Ba kuma Hanifa kadai ba, 'yammatan yanzu matsalar tana addabar su, yarinya tana ganin ko wacce rana tana da sabon saurayi (new catch) to akwai rana zata zo, zaku daina jin son ko wanne saurayi a kowanne wata (new catch). Ranar za ta zo da son nan zai tsaya a ranku na sati, zuwa wata, daga nan sai ya zarce har shekara, har kuma karshen rayuwa. Lokacin da wannan son ya tabbata to an samu abokin rayuwa, tabbas wanda son nasa ya kamaka shi ne abokin rayuwarka wanda za ka so kasancewa gaba dayan rayuwarka. Kada matasa ku dauka .shi ga cikin soyayya, daya yakeda kasancewa a. soyayya.abin dubawa da tunani a nan shine yaron ko yarinyar da aka hadu wancan satin, shine?ko itace? Zai iya kasancewa, idan kukashiga cikin soyayya sannan kaunar junanku ta zama kun kasance a cikin soyayyar. Kuma ina tabbatarwa da mai karatu don mutum ya ce "Ina son ki/ka" yana da masifar sauki a baki, amma kalmar "Nima ina 12. son ki/ka" yana kasancewa tabbas ka sami masoyin kwarai) Hanifa da farko ba ta farga ba sai da 'yan group din ta suka dameta da suka da nasiha Duk da haka Hanifa gani take kamar dai kawa ra'ayinsu kawai suke fada, sai a hankali da ta kuma girma ta kara hankali yanzu kuma take fahimtar gaskiyarsu. Hanifa koda yaushe rokon Allah ta ke yi don ya fito mata da masoyinta na gaskiya don tasoshi har karshen rayuwarta. Ta kuma kara da rokon Allah, Allah ya yaye mata wannan hali don ba ta son abin da za'a sako wulakanci a harkarta. Ba ta son ta yi wulakanci, kamar yadda taki jinin wani ya yi mata wulakanci. ANWAR yana kaunar Hanifa sosai a ransa, duk bayan ko wanne minti sai son ta ya dada shiga cikin ransa don super market babanshi ya bude mashi a beinnit "ANWAR SHOPPING CENTER" aka zuba masa kaya duk ribar a account dinsa take zarcewa. 'Yanmata da yawa sun mato a kan sonsa amma sam ba sa gabansa sai dai Hanifa. Lokaci guda sai Hanifa ta canza son Anwar ya fita daga kanta, sai dai hakurin kasancewa, har dai Anwar ya fahimta. To da yake yaro ne mai ilimin zaman duniya sai ya hakura, ya kama gaban shi. Ba wai don ya daina 13. sonta ba sai dai kawai turbar lafiya a bita da shekara. Ba kamar måzan yanzu ba da sai dai a bude sabon babin naci, kamar kutare. Bayan Anwar ya kama gaban shi, sa Allah da ikonsa ya hada Hanifa da wani tsalelen saurayi dan kwalisa, mai ji da kansa. Suhal shima ya fada cikin so da kaunar Hanifa kamar zai ci babu. Hanifa dai karatun ta ne kawai ranta sai dai dan abin da ba'a rasa ba da ya zama dole tun da samari ba'a sati biyu sai an zo makaranta, ranar visiting day kuwa har buya take a bayan Library ko kuma ta tafi masallaci sai dai idan an tsananta bincike a gano ta. Da farko Hanifa ta nuna wa Suhal itama tana kaunar shi, amma da suka fara soyayya, sai ta ce wai ya takura mata a harkar makaranta, saboda haka sai ta daina sonsa. Ubangiji da ya sa mata sonsa haka kuma soyayyar ta zo karshe, kamar yadda ta kasance da Anwar shima hakan ta faru gareshi, sai kawai ya tattara tsumman rayuwarshi yakama gabansa. Hanifa abin duniya ya dameta don hankalinta ya yi masifar tashi, ganin yanda cikin lokaci soyayyarta take watsewa. Ita dai a kan kanta da zuciyar ta yanzu duk kansu ba su gabanta, sai dai wani zazzafan tausayinsu da yake damunta. Abin da yafi damunta da wannan halin nata kuma yake kara sa ta a halin damuwa bai 14. wuce tantamar ta a kan wai shin haka rayuwarta za ta cigaba yau ga wannan gobe ga wancan ga shi lokaci yana tafiya tabbas nan da shekara daya za ta gama makaranta, ta san kuma tabbas daga gama karatu sai aure. Don a danginsu mace ba ta cigaba da karatu sai dai a gidan MIJINTA. BABI NA BIYU Hanifa suna makaranta a zaune a bayan library ranar asabar, ana ta hira da kawayenta, 'yan set dinsu ne, Hafsat ce ta fara katse Umma Amin wadda ke. ta zuba kamar kanya, tana labarin wata fitinanniyar yarinya new comer da cewar: "Wallahi tunanin Auwal nake tun dazu ni sai wani jin haushin zaman makarantar nan nake yi, makarantar da zaka gama, a yi maka aure". Ta dan yi ajiyar zuciya a hankali. Za ta kara magana ne sai Halwa ta katse ta "Wallahi Hafsat daniceke Allah babu abin da zai dame ni, ina da 15. miji a hannu, ai niko yanzu na samu mai aure na, wallahi 'na bar makaranta...." Gaba dayansu suka kwashe da dariya Umma ta ce "Allah Hafsat Auwal din ki, wani bagidaje ne shi.... Caraf Hafsat ta katseta da cewa: "Lallaikam na gode, Amma dai duk haduwar Hamisun ki ai bai kai haduwar Inuwan Rahma ba". Rahma ta budebaki za ta yi magana sai Halwa tariga ta, a can cikin muryar ta zaki ji alamar dariya ta ce: "Gaskiya an zagi Rahma, don Wallahi duk cikin su Auwal da Hamisu da Inuwa, ba wanda ya kai haduwar Abdul din Hanifa" Ai kuwa sai Hanifa ta daka mata duka tana dariya ta ce: ne?" "Kin ji na saka muku baki a maganar ku zancen yaushe kuma gashi nan kin shigo layin". Sai suka kwashe da dariya. Hanifa ta kalle su a lokaci daya kuma ta waiwaya ta kalli filin wasan makarantar tasu, ta kuma kara da cewa: "An gama (games) fa, ina ganin mu tashi mu tafi dining hall". Hadiza Aliyu ta ce: "Wallahi ni dama yunwa nakeji Allah yasa a kada (bell) dinner yansu" suka dada kwashewa da dariya a tare. 16. Kai Hadiza ciki a ka kawo duniya "In ji Halwa "Ko don ba'a ambaci Mansur dinki ba, shi yasa kike son a tashi?". Hadiza ta kalleta tace: "Shiyasa nagake anfadi Sanin ki ko?" Suka karasa dining hall har 'yan Juniors sun bi layin "Zokar" (abincinda suke gayawa haka, wake da shinkafa). Bayan sun yi Magrib da Isha a masallaci anayi musu wa'azi harzuwa 9:00 na dare, Imam din masallaci. Amma yawancin wasu daliban ba sa tsayawa, saboda ranar lahadi da safe ma anayin M.S.S. safe zuwa azahar. Su Hanifa suna zaune da yamma ranar Juma'a a hostel dinsu sai ga Sa'a Gambo. Sa'a ta cewa Hanifa: "Wallahi Hanifa ba ki kyauta mini ba, ace zuwa na gidan ku uku, amma ke ko tambaya ta hanyar gidanmu ba ki taba yi ba. Kin kyauta kenan?", Hanifa kunya tai bala'in kamata don Sa'a Gambo kam ta nuna mata halacci, sannan sai ta dago kanta a hankali ta ce: "Don Allah Sa'a ki yi min Afuwa Wallahi ina son nazo, kawai dai Allah ne bai nufa, don 17. Wallahi nima wanı lokacin har kunyar ki nake ji. 'Don Allah ki yi hakurı wallahi zan zo". Sa'a Gambo class captain din suce. Kuma room mate dinta ce. Halwa tayi caraf ta cе: "Lallai Sa'aye, ai in dai Hanifa ce kya gaji da jirgi irin nata. Ni kaina sai na kirga miki zuwanta gidanmu. Ba tasan mutane sam!". Hanifa ta ce: "Halwa banda kari, ke da ya kamata ki tayani ba ta hakuri kya batani a wajenta?" Halwa ta ce: "to tsaya Hanifa karya zan miki?" Hanifa ta ce: "Ba wai batun karya, amma kin san ba'a barin mu fita ne shi yasa". Sa'a Gambo ta ce: "to mu din barin mu ake yi, ko mu ba 'ya'ya ba ne? amma sada zumunci ai ba'a hana zuwa". Hanifa ta ce da Sa'a tare da nuna tsananin damuwa a fuskarta: "Don Allah Sa'a kyale Halwa hada mu kawai take son ta yi, na ce miki zan zo in sha Allah, zan bawa Halwa mamaki, don yini zan yi miki". Halwa ta tuntsire da dariya ba kakkautawa, ta ce da Sa'a: 18. "To Sa'a, ba girin-girin ba dai tayi mai Allah ya tabbatar" Hanifata gama kulewa da Halwa sosai, Sa'a na fita, ta hauta da duka. Kamar ta Sani sai ta fada karkashin gado, tana dariya. "Allah ya isa Halwa" in ji Hanifa. Suka cigaba da shrin kwanciya saboda an kada (bell) light out. Halwa Nafi'u Ringim, Kawar Hanifa ce tun suna JSS 2 a lokacin aka kawo Halwa daga oxford school, Lodon a can ta yi Nursery dinta da primary, za su tafi JSS 2 ne sai suka tarkato daga London suka dawo Nigeria shine Daddyn su ya samar mata Kano Model. Halwa 'yar wani Babban likita ce, da ya kware a fannin aikinsa. Bai cika zama a Nigeria ba, koda yaushe sai an aiko mishi da transfer daga wannan. Kasa zuwa wata, ko wanne lokaci idan yatafi ya kan yi shekara daya zuwa biyu a duk garin da aka turashi. Alh. Nafi'u mahaifin Halwa yana da mata guda biyu, Haj. Ladi da Haj. Hadiza suna zaune matan fada road, a Kano. Sai dai sukan ziyarci Ringim wajen dangin mahaifinsu. a Haj. Ladi uwargida ita ce matar Alh, Nafi'u ta biyu, kasancewar matarsa ta farko, ta zo haihuwa Allah Ya karbi ranta. Tana da 'ya'ya 19. uku Aslam. Ilham, da Abba. Aslam shine babban yana da shekara Ashirın dà biyu. Ilham tana da shekara ashirin, ta yi aure bayan ta gama makarantar st. Louis Secondary da yake ita ta zauna ne a wajen yar babarta a katsina road, tana aure a lodge road No. 12. Abba kuwa shekararsa goma sha biyar. Haj Hadiza Amarya ita ce maman Halwa, tana da ya'ya hudu duk mata. Halwa, A'isha, Rahma, da Maryam. Alh. Nafi'u yana da son 'ya'ya, sosai. Amma duk da hakan ya fi damuwa da Aslam yana sonsa sosai da sosai. Kowa kuma a gidansu Halwa yana kaunar 'ya Aslam" haka suke ce masa. Duk da kawancen Hanifa da Halwa ba ajinsu daya ba, domin ita Halwa commerce take karanta. Amma ko da yaushe suna tare da junansu, wasu a makaranta har (twin sisters) suke ce da su. Ranar da su Hanifa suka samu hutun good Friday, Ester Monday sun yi mutukar farin ciki domin duk kwana hudun ya zamar musu kamar visiting day. Ko wacce rana sai an zo musu, azo daga gida sannan da yamma samari su zo. Bayan zun idar da sallar Isha'l ne suka zauna suna addua'r samun saukin karatu da 20. kuma neman sa'ar Jarrabawar da aka kafe musu time table, za su fara sati daya! Wannan hutun ne su Hanifa za'a shiga form Six (SS-3) Bayan sun fito suna tafiya ne Halwa ta fara ba da labarin 'yan gidansu (as usual) Hanifa har ta haddace farkon zancen Halwa in dai hirar gida za a yi. "Allah sarki ya Aslam, ko yana tuna wa dani kuwa, 'yan Paris sun dauke min yaya". Shi ne abin da Hala ta ke fara fada a duk lokacin daza'afara hirar gida. Hanifa ta ce da Halwa "Kai ni dai gaskiya Halwa na gaji da wannan zancen Aslam - Aslam, wai shi kadai ne a gidan ku ne? kullum ba ki da wata hira sai ta Aslam! Ni Wallahi har so nake na ga yayan nan naki". Halwa tayi shiru tana kallon Hanifa, а hankali. Hanifa ta cigaba da cewa "Kuma na san bani kadai ba ma duk wanda yakejin hirar Aslam a wajenki, yana muradin ya ganshi, saboda kullum zancen sa ake yi". Halwa ta yi murmushi sannan ta ce; "Ke kuwa Hanifa idan ban yi hirar Ya Aslam, to hirar wa zan yi? wallahi don ba ki ga yanda na matsu a yi mana hutu naje na ganshi 21. ya ganni don na san yanzu shima yana ta tunani na ya damu ya' ġanni. Hanifa ta yi wata isashshiyar dariya, sannan ta ce da Halwa: "Kin ji ki da wata irin magana wai yana tunaninki ya damu da ya ganki sai kace wata matarshi". Caraf Halwa ta karba ta ce: "Ai wallahi bari ná gaya miki ni nasan nafi matar ya Aslam, don na san da su Mama za su barni, ba abin da zai hana, idan ya Aslam ya yi aure mu tafi tare ba, don ba zai iya zama babu ni ba, kin gakuwa ai kinsan nafi matar sa matsayi. Don wallahi wata

Chapter 1 of 3