Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 1
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels ASHE MATAR AURECE.....1 Rayuwa kenan ni kaina bansantaba, bansan daga ina ta fitoba, ban taba ganin taba, bansan yar wace ƙabila bace, bansan halayenta ba, Amma naji sonta ya Kamani lokaci guda har na ɗaukarwa kaina Alƙawarin Sai na Aureta kota halin ƙaƙa koda Duk abinda natara zasu ƙare Koda rayuwatace Zan iya sadaukarwa sabi da in Aureta koda Aranar da aka ɗaura Aure Zan Mutu... Tsaye nake abakin titin dake unguwarmu wanda ya ratsa daga konannan gidan mai zuwa cikin unguwar bello dake cikin Dorayi kano kowa yana ta hada- hadar kasuwancinsa... Idan kayi duba izuwa gareta hakika Allah yacika kamala da duk wani Dan'adam zai gani yaji ya yaba kuma ya kyasa Allah ya azurta wannan baiwa tasa da abubuwa kamar haka ga kyau ga kamala gata da kwarjini hade da daukar hankalin duk wani ɗa Namiji da sukayi Arba dashi dole ta sace xuciyarsa gata kuma da farin jini sannan bazaka iya banbance shin tafiya take da kafafuwanta ko kuwa injin ɗin tafiya ta hau yake yawo da ita...? Sannan abin da zai birgeka da ita shine Allah ya azurtata da idanuwa dara-dara koda cikin duhun darene zaka iya gane idanunta idan ta budesu wani abin haushi da baƙin ciki shine tare naganta da wani saurayi dan kimanin shekara 30 Baƙi mummuna ... Yayinda sukazo giftawa ta gabanmu gaba daya ilahirin mutanan dake gefan titin kamar su yaya Abbati da amininsa Ibrahim suraj da wani dattijo mai suna salisy da malan sagiru dukkan ninsu hankalinsu ya karkata zuwa gareta kai harma da wasu matan ... kai nima kaina ba abarni abayaba wajan kallon kirar fatar kyawun halittar dirin da Allah yayiwa wannan baiwara Allah ba yayinda sukazo suka gifta tare da Dan'saurayin nan gani nayi jama'a baki ɗaya suka bita da kallo kai ka rantse kauyawane amma ina sam ba haka bane ko kaine sai taja hankalinka wajan kallon dirin kyawun zubar gadon halittar da Allah yaiwa wannan baiwa tasa Kubiyoni kuji yadda ta kaya yin comment naku shine zai bani kwarin gwiwar cigabaASHE MATAR AURECE........2 ...........haka dai tsaya tsawan lokaci, kuma naci alwashin bazan bar bakin titinba har senaga abinda ya turewa BUZU nadi. A wannan rana ko kasuwa banjeba ina tsaye sai naga dawowar wannan baiwar Allah koda kuwa zanyi kwana in wuni ne! domin ta shiga raina.... Cikin daƙiƙu kaɗan misalin 5:00 na yamma kuwa nahangota tana tafe ita kaɗai lokacin, anan nacika da farin ciki mara misaltuwa, koda ta kusan isowa ƙofar layin mu zuciyata ta fara ayyanamin na bita kawai, banyi nawaba kuwa wayan amsa bukatar zuciyata, nayi niyar binta amma dana juya sai na hango wannan ɗan mummunan saurayin yana sauri ashe ya tsaya siyayya ne abaya... Saboda tsananin Baƙin ciki kawai senaji duk duniya babu wanda natsana lokaci ɗaya irin wannan mummunan saurayi da suke tare da wannan kyaikyawar halitta... Nan naga yafara kokarin yimata magana, ga mamaki sai tattausan murmushi kawai takeyi batare da naga tana bashi amsaba, hannusa na dama riƙe yake da waya BLACKBERRY kirar zamani, aikuwa nima tun daga ranar tuni nasamu abinyi, dan saida na shafe kusan kwana 26 ina saita lokacin wuce warsu dana dawowarsu, amma ina duk tsawan wannan lokaci. shiru kakeji .. Wata ranar Asabar da yamma na fito kamar yadda na saba zama a ƙofar layin mu dan jiran tsammanin sake ganin fuska ma'abociyar haske da walwala, can Da misalin ƙarfe 5:23 na yamma zakara ya bani sa'a... Masu sauraro tabbas idan natswa wassafa muku halitar wannan baiwar Allah zakuyi mamaki domin kuwa bazan iya tantace mutumce ko aljanace ba, "wai shin wacece wannan?" Tambayar da nakasa baiwa kaina Amsa kenan, Shawo kwanan danaga sunyi shine yayi matuƙar jefani cikin yanayi guda 2. Na farko na kasance mai tsananin Farin ciki da sake ganin wannan baiwar Allah wadda Rayuwata tashiga yanayin Ruɗani dominta! Na biyu kuma na faɗa cikin yanayin ƙunci da baƙin cikin sake ganinta danayi da wannan Saurayin da suka wuce Ranar farko dana fara yin Tozali da ita... "Shin wannan meye alakarsa da itane" wannan tambayar ce tasake fadomin cikin zuciya...Tabbas awannan lokacin na ƙara jin tsanar wannan saurayin ya ƙara shiga Cikin zuciyata, duk da. Cewa bansan dangantakar su da itaba, Yauma kamar ranar sai zuba mata surutu yakeyi amma ita banga tana mayar masa da amsa ba. Kamar kullum murmushi kaɗai naga tanayi yau ma, da alamun tana matuƙa jin daɗin zantukan da yakeyi mata.... Ganin haka danayi ya ƙara jefani cikin matsanancin kishi wanda naji kamar inje in Haushi da duka, to amma matsalar anan itace bansan menene matsayinsa awajenta ba, kada naje na aikata aikin da nasani, wanda hausawa kecewa "qeyace" ahaka dai zuciyata taita yimin Zantuka marasa fa'ida akan wannan saurayi, ina wannan tinanin har suka ƙaraso inda nake, ƙura mata ido kawai nayi na saki baki tamkar wanda yawu kezuba daga bakisa, ai tuni najini na faɗa cikin kogin tunani na irin tanadin da zanyi Mata idan ta zama matata, dan jinake a raina ko ƙuda bai isa ya gifta ta gabantaba. ballanta na yataɓa fatar jikinta batare dana kawar dashi daga doron ƙasa ba. sukuwa abinda ke gabansu Kawai sukeyi, domin nafahimci basusan ma inayi ba, na fahimci Baƙi ɗayansu suna cikin farin ciki da annashuwa. Lokaci guda kuma naji ƙamshin turare ya doki hancina, hakan yasa na dawo cikin haiyaci na daga wannan dogon tunanin da na afka, zuciyata ta fara dukan 3'3!!! Tab.....wannan shine ga koshi ga kwanan yinwa, Gadai dama ta sake samuwa wajen gabatar mata da kaina da irin halin da nashiga a dalilinta ga kuma wannan saurayin da suke tare na son zama Barazana wajen Aiwatar da wannan kudiri nawa Wajen Wannan kyakkyawar Halitta... "Qaq Qara Qaqa" zuciyata ta sake fada, wannan dama da na samu Itace ya kamata nayi amfani da ita wajen gabatar da kaina agareta dan bansan lokacin dazan sake ganinta ba, Yauce Ranar da yakamata na Furta mata kalmar Soyayyata dan gudun kada nayi Zurfin ciki Har lokaci ya ƙure, kokuma nayi rashin sa'a ta kuɓucemin.., Anan na yanke shawar Zuwa na tareta koda kuwa suna tare da wannan Saurayin yazama dole ya bani Uzuri idan kuma ba hakaba komai ta Fanjama fanjam... Ga mamakina.... Cikin dakakkiyar zuciya na nufi inda suke, Ina binsu abaya zuciyata na sake bugun 3 3, na riga nagama rikicewa, dan harma na rasa ta inda zan fara ina cikin wannan yanayin wata farar dabara tazomin, nayi tinanin bin bayansu har zuwa inda zasuje haka nata bin bayansu batare da sun ankara da ina biye dasu ba har muka isa wani makeken gida, anan na ja birki na tsaya daga dan nesa kadan dan ganin ikon Allah zuwa dan wani lokaci, ina tsaye naga saurayin nan ya fito shi kadai ya nufi hanyar.......... Kubiyoni kusa labarinASHE MATAR AURECE..........3 ........zuwa dan wani lokaci na ga saurayin nan ya fito shi kadai ya nufi hanyar da tabi daya bangaren, wato hanyar da bata inda suka biyoba dazu. Hausawa nacewa "Rashin sani wanda yafi dare duhu" Ashe wannan abu daya faru shine farkon shigata matsala, domin bai dade da fitowaba naga itama ta fito, tare suke da wata 'yar karamar yarinya, 'yar kimanin shekara 9, hakan dana gani naji zuciyata tayi fari, domin koba komai nasami sukunin yimata magana. Cikin tinkaho da farin ciki na doshi inda wannan kyakyawar halitta take, kodana karasa kusa da ita banyi watataba wajen yi mata sallama, ga mamaki sai naga tayin wani irin kallo me dauke da zargi, kana ta daga min hanu batare da ta amsamin sallama ba, ganin haka nakara bude bakina akaro na 2 tare da daga murya, dan a tunanina ko bataji sallamar da nakeyi mata bane, "A'a ikon Allah" Ga mamaki sai naga ta kara daga min hannu, murmushi kawai nayi da ganin haka, domin nayi zaton jan ajine irin nasu na 'ya'ya Mata,,, Na raya hakan a raina, amma kuwa indai haka ake jan-ajine to lallai wannan jan-ajin baiyiba, domin duk musulmin kirki idan akayi mai sallama yazama dole ya amsa, koda kuwa maiyin wannan sallamar makiyinshi ne, dadai naga Alamun bata da niyyar amsa wannan sallamat tawa sai nafara gabatar mata da kaina kamar haka Da farko nidai Sunana DAHURU, amma mutane da yawa suna kirana da me Allahu ,,,, Adai dai lokacin da muka hada ido da ita yamitsa baki kawai naga tayi, da alamun batani takeyi ba, dan naga ta dan matsa daga inda nake ta tsaya daga nesa dani sosai; ganin haka da nayi sai natambaye wannan yarinyar sunanta tacemi sunanta SUHAILA, amma kurma ce bata iya magana, amma kuma tanajin duk abin da aka fada mata, Yarinyar ta sake buɗe baki da alamun zataci gaba da magana na dakatar da ita Da cewa " yaisa, bari haka nagode" tabbas nayi Matuƙar mamakin ganin irin wannan kyakyawar suffar da Allah ya azurta wannan baiwa tasa dashi amma kuma gata Kurma ce... Lallai nayarda SO babbar cutace, duk da jin danayi ance Kurmace bai sanya zuciyata samin tsaiko dangane da bege wannan mata a raina ba, Saima jinai tamkar ana kwarara kaunarta azuciyata, Ahaka na ƙarasa kusa da ita naga tana ƙara ja dabaya tamkar wadda taga wani mugun abu na dosota, ashe kuwa kusan hakane, Domin. Seda nayi danasanin ƙarasawa kusa da ita, sedana zubar da hawaye mara adadi sana diyar wannan kara sawa kusa da ita, sedana cizan yatsa mara anfani a sanadiyar wannan abu, abindaya faru shine Ina ƙara sawa kusa da ita naga jikinta yakama karkarwa, kamar taga wata ɓaƙar Masifa ko bala'i yana dosota, ganin haka yasa na fara yi mata Magana ina cewa "Lafiyar ki kuwa, Sai wani guduna kikeyi kamar wanda ya zo miki da saƙon mutuwa" mamakin yadda naga jikinta yasake daukar bari...... Sannan naga tanamin nuni da abin dake Bayana, koda na juya kwatsam.......nayi arba dashi, bawani bane illa wannan mummunan Saurayin da suka wuce tare yanufo inda muke cikin yanayi na fushi da bacin rai, Ƙarasowarsa keda wuya naga ya wuceni ya isa inda take Baiyi watawata ba wajen Wanka mata Mari yana cewa Waton haryanzu bakiji....ASHE MATAR AURECE....... kashi na 4 .............Ganin kyaikyawan Marin da yayiwa wannan kyakyawar halitta danai bantsaya jin ƙarashen maganar dayake yiba, nayi kukan kura na sungumeshi na ɗaga sama na tafka katan banza aƙasa, nahau tumurmusarsa mitsiyaci, kafin kace kwabo tini jama'a sunyi ca akan mu suna ƙoƙarin kwakuleshi a hannuna, Saida nayimasa lilis kafin susami damar kwatarsa, wani babban Abin mamaki Abin takaici shine koda jama'a suka sami damar ƙwatarshi awajena ita kuma wadda nayi abin dan ita se ganinai ta ɗauki wani ƙaton itace ta rafka min akaina, har saida wajen ya fashe jini ya fara kwaranya, jiri ya fara ɗibata har nafaɗi ƙasa bansan inda kaina yake ba...... Daga inda nake a kwance ina iya hangota ta sanya mutumin nan gaba tana masa kuka tana share masa jini da majinar da na haɗamasa, hawaye naci gaba da zuba daga idanunta.... Ganin haka danayi nayi kokarin gyara zama ina naiman hanyar guduwa, ganin haka jama'ar dake gurin suka riƙeni aka fara mayar da magana:- Koda jama'a sukaji abinda yafaru se suka fara cewa "irinkune ƙwartaye, masu bin Matan Mutane dama " Dukda cewa nayi musu rantsuwa akan bansar matar aure bace amma sukaƙi yarda dani, Suka fara muhawara a tsakanin su suna cewa "aiwannan kam bazamu barshi hakaba, domin kuwa laifin nasa 2 ne ganabin Matar Aure ga kuma na dukan Mijinta dayayi" Nayi zuru-zuru. Cikina ya kada, narasa abinda zance dan tini Har muryata ta dashe wajen rantse-rantsan Ƙwatar hakina akan cewar Bansan Matar aure bace... Can bayan wasu ƴan Mintina naga anɗakko wata sharɓeɓiyar igiya ana shirin ɗaureni da ita da nifin kafin jami'ano tsaro suzo, tamkar wanda ya aikata sata, Ita kuwa SUHAILAT sai sharɓa uban kuka takeyi, Wani babban abin mamaki danagani a tattare da ita shine alokacin da nake cikin wannan tashin hakali saina lura da cewar ƙyawunta har yaso ya ninka nada, "ashe garama kukanta da murmushinta kenan ko?" Wata zuciyar tace dani, dan a lokacin naji wani Sabon shauƙin ƙaunarta ya ƙara kamani a zuciyata, har yaso ya ninka nadama, ashe bansani ba da sauran Rina a kaba agabana, (ma,ana ashe bala'i na GABA!!! domin kuwa wannan wanda nake ciki zan'iya cewa gabatarwa ne kafin inshiga cikin fasalin. Zuwa can wani dan lokaci saiga hukumar 'ƴan sanda sun iso gurin kusan mota 3, Da zuwansu kuwa sukayi arba dani an ɗaureni tamkar wuwun goro, gashi kuma har zuwa wannan lokacin jinin raunin da wannan kyaikyawar halitta tayimin bai dena zubar da jiniba, a haka suka ɗaukeni suka jefa a Mota batare da sun tausayawa halin da nake cikiba, Nikuwa ba abinda nakeyi banda kallonta, har izuwa lokacin da motar ta fara tafiya hawaye bai daina zuba daga idanunta ba, kafin motar jami'an tsaran da fara tafiya da sauri seda suka tabbatar na sume, Bantashi Farkawa ba sai acikin Cell ɗaure nake a jikin wata kujerar ƙarfe da ankwa, ga wani Baƙin ɗan sanda waishi GALLOBE wani gajere dashi kamar na kifeshi da koko a kusa dani, hannusa yana riƙe da wani ƙaton kulki, Koda yaga na bude idona da alamun na farka senaga yafara yimin dariya yana Cewa Nine maganin irin ku.... "Kai yanzu duk 'ƴan Matan da Suke garin nan ka rasa wadda zakabi Sai Matar Aure...? To yau zakaci Ubanka kuwa, ai kuwa beyi jira yaji koda kalma ɗaya daga Bakina ba ya hau Rafkata yata bugamin wannan kulkin da yake hannunsa, salati da salallami har nadawo ihu, tun Ina ihu har nagaza ko motsi. Tabbas nadaɗe inajin Ana cewa 'ƴan sandan basu Da....................... Ashe kuwa haka abin yake, dan kuwa masu faɗar hakan basuyi ƙarya ba, Idan akwai Abin da yafi haka ma Idan mutum ya kirasu dashi baiyi Laifiba a zatona, haka muka kwana da wannan Azzalumin gajeran dan sanda mesuna GALLOBE har gari yawaye, Saboda tsabar dakuwa danayi har bana iya tashi, Washe gari da Misalin ƙarfe 9:00am Wannan mummunan Saurayin da suka ce shine mijinta ya hallata a hukumar 'yan sanda, domin ni agaskiya har yanzu banyarda da cewar wai shine Mijinta ba, domin kuwa sam koda wasa basu daceba.. tare suke da SUHAILAT, sunzone dan rubuta (report) bisa ga abinda yafaru, basu wani tsaya ɓata lokacinsu wajen kula da lafiyata ba Gajeran ba Gajeran Ɗan sandan nan yana shigowa ya kama ƙafata ya fara Jana kamar wata gawa har zuwa inda za'a ɗauki report ɗin, Koda muka iso sena lura gabanta yayi mummunar faɗuwa harda dafe ƙirji ganin irin mugun yanayin danake ciki, nan da nan naga idanuwanta sun ciko sunyi jazur hawaye na shirin zubowa, cikin sauri naga ta kawar da fuskarta daga kaina, ta daina kallona tana kaɗa kai da alamun nuna matuƙar tausayawa halin da nake ciki. Shikuwa ɗan Banzan mijin nata ko ajikinshi dan wani kallon ƙasƙanci da wulaƙanci naga yanayimin, daga nan yafara bada bayanin ƙarya da gaskiya, dan ya faɗi abubuwa masu ɗinbin yawa waɗanda ban aikata ba, Ita kanta matar tasa saida naga ta riƙe baki dataji irin ƙarya dasharrin daya fara tafkawa akaina, ananne na Farajin sunansa.... Nikuwa ba abin da nakeyi banda kallonta gami da murshin nuna bege a zuciyata, harta fice daga police station ɗin kuwa, Ashe bansani ba akwai wani Sabon Bala'in da yake tunkaroni wanda yafi wanda nake ciki a yanzu, Dukda raunukan da suke jikina Wannan Gajeran ɗansandan bai tausayamin ya ƙyaleni ba Sai ma ƙarawa dayayi akan na Daren jiya, acewarsa duk Abinda yake wakana a tsakanina da ita na yanayin kallan da nake mata akan idansa nake, duk abinda nayi yariga ya Gama Samin ido, Haka yayi ta jibgata kamar bazai barni da raiba, yana fadin Wato haryanzu kai bazaka ƙyale Matar mutane ba ko? Koda jin Wannan kalma danaji yayi bansan sanda bakina ya canja daga ihu zuwa sututai ba, ina fadin " wallahi idankaga na Ƙyale wannan Matar Sai Ranar dana daina Nunfashi aduniya... muddin kuwa Ina Nunfashi a ɗoron ƙasa Bazan taɓa iya haƙura da Soyayyarta a raina ba, koda kuwa soyayyar tata itace Sanadin Mutuwa ta, nariga na ɗaukarwa kaina Alƙawarin duk runtsi duk Wahala sai na cimma Burina na Auran Wannan SUHAILAR...... da yardar Allah!!! kawai saukar kulkin danaji takaru a akaina shi yayi sanadiyar katse surutan da na keyi, Jirine naji ya ɗibeni na faɗ ƙasa amma Dukda Haka ban haƙura ba Sai da na ƙarasa Ambatar sunanta SUHAILAH... Daga nan na faɗi ƙasa sumamme... Jama'a ko kusan yadda takaya a gaba kuwa???? Kubiyoni kusha labari,ASHE MATAR AURE CE...? Part 5 FARKON SHIGATA MATSALA Rayuwa kenan ni kaina bansantaba, bansan daga ina ta fitoba, ban taba ganin taba, bansan yar wace ƙabila bace, bansan halayenta ba, Amma naji sonta ya Kamani lokaci guda har na ɗaukarwa kaina Alƙawarin Sai na Aureta kota halin ƙaƙa koda Duk abinda natara zasu ƙare Koda rayuwatace Zan iya sadaukarwa sabi da in Aureta koda Aranar da aka ɗaura Aure Zan Mutu... Daganan suka mayar dani cikin cell ɗina... Komawata ke da wuya na fito da wannan ledar ta tayar agabana domin in ɗauka... Ina buɗe bakin Ledar nayi tozali da abubuwa 2 aciki.., wato Gurasa da wata ƴar ƙaramar takarda a Anan naɗe.. Ga Alamun dai wasiƙace... Ganin kwana na 2 ban ɗanɗani koda ruwaba ballantana Abinci.. Na hau gutsurar gurasannan Batare da na tsaya Buɗe wasiƙar ba ballantana Nasan Abinda ta ƙunsa... Ai kuwa ina gama cin gurasar nan Na ɗauki takardar na fara buɗeta... Inagama buɗewa.. Kafin na fara karantawa naga An fisgeta daka hannuna... Ɗaga idona danayi.. Naganshi tsaye akaina... Ba wani bane Illah wannan Mugun ɗan Sandan da yariga yagama samin ido... Kafin in furta wata magana naga ya fitoda Lete daga Aljihunsa ya ɗannawa takardar nan wuta... Yace ai duk Abinda ya wakana atsakaninku ina gani... ashe itama Munafu..., Ban bari ya ƙarasa Abinda yake son faɗaba na sureshi na ɗagashi Sama ta Tafkashi a ƙasa na hau kanshi nayi ta dukanshi baji Bagani... Yayita Ihu kafin kace kwabo Sauran Jami'an ƴan Sandan sun kewayemu.. Suna ƙoƙarin Kwatar shi... Dadai sukaga bahali.. suka hau dukana da sanduna har nafaɗi sumamme... Bantashi farkawa ba Sai washe gari da Misalin ƙarfe 8:43 na safe.. Aka fito dani da Hankoof ɗaure a Hanuna akan za'akaini kotu... Jin maganar tafiya Kotun danaji Anyi shiyayi matuƙar tayar min da hankali har yafi na wanda nake ciki nasan Tabbas ba makawa Sai natafi Gidan Yari... Dan bawani Mai goyon Bayana daga cikin 'ƴan sandan Kuma bana son Koda mutum ɗayane Daga cikin Dangin mu Yasani... Ballantana Da misalin ƙarfe 10:00 muka isa Kotu... Mukatar da Kotu tacika maƙil da jama'a mu kaɗai ake jira.. Shigowar mu ke dawuya tundaga bakin kofa naga tana kallona har zuwa inda ake tsayar da wanda ake tuhuma da laifi... Mai gabatar da ƙara ya fara gabatarwa Kamar Haka... ANA ZARGIN MUSA DA BIN MATAR WANI ALHALIN KUMA YASAN MATAR AURECE ASAKAMA KON MIJIN MATAR YAYI MAI MAGANA YA HAUSHI DA DUKA SAI DA YA SUMAR DASHI DA ƘYAR AL'UMAR DA SUKA KAWO AGAJI SUKA ƘARƁE SHI... ASHE MATAR AURECE...6 sabuwar matsala ta Samu,,,, Aranar da nafito daga gidan yari Ban zame koinaba sai Gidah,,, tundaga Nesa naga Mutanen unguwarmu suna yimin wani irin kallon Ban mamaki mai dauke da alamun tambaya,, dayawa daga cikin su har nunani sukeyi da hannu,, yara kuwa har guduna naga sun farayi.. Tabbas nacika da mamakin ganin wannan sabon lamari dake faruwa har takai na fara zargin kaina akan kodai sunji labarin abinda ya faru tsakanina da wannan mummunan mutumin nan tare da matarsa kuma Masoyiyata..? Jikina gabaki daya yayi sanyi daganin wannansabon lamari har takai na fara tunanin Kada na Karasa.. Dana isa bakin kofar gidan mu ina tsaye zuciyata na bugun 3:3 kwatsam naga kanina AMEER ya fito daga cikin gida ganina da yayi naji ya kwalla wani uban ihu ya juya ciki da gudu.. Kafin inyi yungurin wani abu naga Mutanen gidan mu baki dayansu sun fito da gudu ganina da sukayi baki dayansu suka cika da Al'ajabi suna cewa SADEEQ daman kananan da Rai!!!!!...? Kaikuwa wace duniya ka tafi haka.. Har kowa ya dauka ka mutu..!!! Yau kimanin Wata 3 da kwana 2 kenan Tundaga ranar da kafita da yamma ba wanda ya kara ganinka ko jin labarinka.. An naimeka a waya an rasaka.. Ga yanayin garin namu tashin hankali yau tashin hankali gobe.. Yau sati 3 da kwana 5 kenan da gama zaman makokinka.... Dariya ce ta subucemin dajin danayi sunce har anyi zamanmakokina... Wannan shine abinda ya baiwa Mahaifiyata Haushi kenan har takai ta tafka min Mari... Dukda marina da tayi ban daina Mamakin cewa da sukayi na Mutu ba.. Abinda na cikaba da Maimaitawa shine.. Kallonsu nakeyi Ina cewa Wai na Mutu..!!! Sai in kyalkyale da dariya.. Bai fi minti biyar da faruwan wannan lamari ba kofar gidan mu tacika makyil da Jama'a sunzo kallona Suma suna Mamaki Na Mutu na Dawo... To wata sabuwa amma karku damu kudai kubiyoni kuji yadda zata kaya bayan fitowar tawa zanci gaba da son SUHAILAT ko kuma zan hakura ne An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 1 of 1