Ɗan motsin da wayarsa tayi ne ya sashi sake furzar da huci, sai kuma ya sauke hannunsa dake cikin dawar nan ya cirota daga aljihu yana dubawa. Kallon wayar kawai yake babu wani yanayi dake nuna kirane ke shigo masa ya kamata ya ɗaga, harta gama ta yanke, sai kawai yay ƙoƙarin maidata aljihun, amma hanzarinsa ya katse saboda sake motsawar data shiga yi a karo na biyu. Yanzu kam hannu ya kai ya wani murza goshinsa, kafin ya sake ɗaure fuska babu alamar wasa sannan ya kai wayar kunne alamar dai da gaske kiran nashi akeyi..
“Hallo. My D!”.
Wata zazzaƙar murya mai sanyi da kwantar da kai ta faɗa daga can. Shiru babu alamar zai tanka, da sauri ta ce, “Oh I'm sorry dear. Assalamu alaikum”.
“Wa'alaikissalam”.
Karo na farko jarumar muryarsa ta bayyana cikin buɗaɗɗen sauti da ƙarfin lafazi irin na maza marasa son wasa da lokaci. Itama sai ta ɗan ƙara kwantar da murya ta gaisheshi. Maimakon amsawa tambaya ya jeho mata a kausashe.
“Kiran na miye?”.
Yanzu kam murya ta raunana kamar zatai kuka, ta ce, “Haba My D. Shike nan abu baya wucewa a wajenka, na baka haƙuri, na tura maka saƙo amma duk ka share ni. Dan ALLAH kayi haƙuri, nayi kuskure kuma na yarda nayi ina sake neman afuwa. Wlhy ni kewarka ma nake yi dan ALLAH kazo gareni, wata biyu fa ba sati biyu bace.”
Shiru yayi bashi da alamar tanka mata, har sai da ta fara kuka ƙasa-ƙasa tana cigaba da roƙonsa da ban haƙuri sannan ya motsa lips da ƙyar ya furta, “Naji”.
Baiwar ALLAH, dariya ta farayi cike da farin ciki, sai jera masa kalaman soyayya take masu zaƙi da taushi dake nuna tsananin kewa da begensa da take ciki. Shi ko yaƙi ya ƙara cewa komai. Cike da sake kwantar da kai ta ce, “Na faɗama Ummie?”.
“No!”.
“Ammafa itama tana kewanka D. Haka ma su Biebah kullum zancen ka ne a gidan nan, yau tunda na shiga hiranka kawai mukeyi”.
“Uhmm!”
Kawai yace. Bata damu ba ta cigaba da masa labarin ƙannen nasa, sai kuma ta koma na yaran dake tare da ita. Shi dai nashi saurare kawai, sai dai fuskarsa ta ɗan sassauta kaɗan ba kamar farko ba. Hakan na nufin koma wacece tana da muhimmanci a gareshi. Ya jima suna wayar kafin network ya fara rawa, kasancewar inda suke sai a hankali dama. Wayar ya maida aljihu, sai kuma ya ajiye robar dan dawar ta ƙare duka. Jejin ya shiga bi da kallo irin na nazari, kafin ya bar wajen gaba ɗaya ya koma cikin tantin da ya fito ɗazun..........✍🏼
_Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._
*_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_*
*_+227 98 94 12 81_*
*_My NITA_*
_Shaidar biya👇_
*_Whatsapp number_*
*_+227 98 94 12 81_*
*_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_*
*9032345899*
*_Moniepoint MFB_*
*_BILKISU MUSA IBRAHIM_*
*_KATI MTN (1k)_*
*_09032345899_*
*_Shaidar biya: 👇_*
*_Telegram Number 09032345899_*
*_AREWABOOKS (Vvip)_*
*_Chapters & Audio_*
@BilynAbdull
*_WHATSAPP (500)_*
*1487616276*
*_Access Bank_*
*_Bilkisa Ibrahim Musa_*
*_Kati MTN:- (500)_*
*_09032345899_*
*_Shaidar biya:-_*
*_Whatsapp Number +234 805 568 7449_*
*_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_*
*_WhatsApp Number 👇_*
*+234 805 568 7449*
*_Telegram Number👇_*
*+234 903 234 5899*
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
[10/2, 2:42 PM] Zeenaran 😘: *_Typing📲_*
*_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_*
*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*
*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._
_Chapter 3_
__________________
https://chat.whatsapp.com/GCVmfFguMEf49AFrOjSiMt
IMZEEDVENTURE
Duniyar kayan kitchen ƴan yayi dake maida mata ƴan ƙwalisa a gidajensu.
Shin kuna Neman in da zaku samu luxury kayan kitchen masu kayatarwa?
Kayan yara masu kyau unique na yan gayu?
To shiga link din grp na Imzeedventure🥰🥰🥰 Kisha mamaki🗣️ idan baki da kudin siyan kayan Yaro sabo to zaki iya yin order na kayan gonjo dinta mai Kama da sabo!
Idan kuma kayan kitchen ne baki da kudin siyan nan take to har adashi GATA tanayi🥳🥳.
IMZEEDVENTURE wata sabuwar duniyar ƙyale-ƙyale ce da ƙayatarwa da mata sukafi buƙata musamman ƴan ƙwalisa da son gwangwaje kawunansu harma da iyalansu.
Gaji ya kori ji, garzaya ki shiga wannan link ɗin namu dai domin ganema idanunki.
https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1.
Koki tuntuɓemu ta wannan layin *_+234 707 753 2253_*
Muna da account aTikTok@imzeed _venture.
https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90A6JG1PvXe&_r=1
Karku bari ayi babu ku,😘😘😘😘😘 Nima Bilyn Abdull tuni na antaya🏃
_____________________
*_TELEGRAM GROUP_*
https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk
*_WHATSAPP CHANNEL_*
https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F
*_TIKTOK_*
https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/
*_INSTAGRAM_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv
____________________
........Ɗagowa Imran dake zaune a study table yana duba wasu takardu yay yana kallonsa. Shi ko kallo ɗaya yay masa ya ɗauke kansa, zama yay a bakin gado ya jawo takalma daga ƙasan gadon, batare daya kalla Abbas dake cigaba da kallonsa ba har yanzu ya ce, “Zanje gida”.
“Gida kuma? Lafiya dai ko?”.
“Kawai zanje ne!”.
Ya faɗa a taƙaice.
Abbas yasan amsar ke nan, amma sai yay shiru yana kallonsa da nazari. Eh yasan in dai yace zai je gida akwai dalili, sannan sai ya tabbatar babu wani ƙalubale da zai bari mai girma a inda suken, amma haka kawai shi sai a yau sai yaji kamar tsoro ya tsarga masa akan tafiyar tasa, sai ya kasa cewa komai.
Dai-dai Zak-Shadow dake haɗa bindiga shima ya ɗan ɗago ya kalla Imran ɗin, ganin yanda ya zuba masa idanu sai ya sake tsuƙe fuska ya ɗauke kansa. Imran yayi murmushi, dan yasan ya tsani kallo. Cike da tsokana ya ce, “Anya ba kewar Madam bace ke tsikarin ka?”.
Bai kula tsokanar da yake masa ba, kansa ya ɗan girgiza kawai yana zuwa gab da shi ya ciri ƙaramar takarda ya ɗauki pen yay gajeren rubutu. Batare da yayi magana ba kawai ya tura gabansa ya nufi barin wajen, sai kuma ya juyo yana kallonsa, cikin ɗage gira sama ya furta, “Ka rage sa ido Imran, idan nayi kewar laifi ne?”.
Imran yayi dariya da faɗin, “A'a bakai laifi ba MAZAJEN FAMA, maza jeka ka ɗabbaƙa sunna abinka”.
“ALLAH ya shiryeka”.
Cewar Zak-Shadow. Imran ya amsa da amin yana ɗaukar takardar ya fara dubawa.
_“Bana son kowa yasan na fita, kamar yanda na faɗa maka 2 days ne, Kar abar ƙofar yamma a buɗe, dan haɗarinta yafi na sauran ƙofofi ka sani. Imran idonka ya zama sosai akan yaran nan da dukkan Captains ɗin kowanne sansani, sannan duk motsin da bai muku ba na sani, komai ƙanƙantarsa._
Takardar Imran ya ajiye ya juya yana kallonsa da faɗin, “Babu damuwa in sha ALLAHU. Amma dan ALLAH ka biya ka sayo min kilishi da gyaɗa. Zan sa a kawo maka saƙo daga gida ka taho min da shi..”
Wani kallo ya ɗago ya zuba masa, Imran daya san ma'anar kallon sai ya kwashe da dariya. “Maida wuƙar, ba ɗan aike zan maidaka ba ai ALLAH nace”.
A karo na farko Zak-Shadow ya ɗan saki wani murmushi gefen baki yana ɗauke kansa da ɗan girgizawa. Shima Imran ɗin murmushin sa ƙara faɗaɗa yayi. Yana matuƙar son aminin nasa, kamar yanda kowa yasan shima Zak-Shadow na sonsa matuƙar so ma kuwa. Dan shi mutum ne mai ra'ayin riƙau, idan baya yinka, baya yinka kawai. Idan ya soka kuma, to da gaske son naka yake. Mutum ne tsayyaye akan ra'ayi, kuma ɗan kai tsaye, baya iya kawaici akan duk abinda bazaiyi ba kuma baya buƙata. Idan har yace maka (eh) to ‘eh’ ɗin ce koda za'a kashesa, idan kuma yace (a'a) tofa ‘a'a’ ɗin ce. Zak-Shadow yasha baƙar wahala a lokacin da suke yaran soji saboda wannan taurin kan nasa a hannun manyansu. Dan a shekararsu ta biyu da fara aiki har zaman prison na sojoji yayi na wata shida saboda wata tirjiya da yayi akan umarnin wani ogansu. An azabtar da shi matuƙar azabtarwa a lokacin, dan bayan ya fito ma mutane da yawa sunyi zaton bazai sake rayuwa mai tsaho ba, amma da yake rayuwa ta UBANGIJI ce sai gashi ya miƙe, miƙewar data zama sanadin jajircewarsa a yanzu. Dan azabar da suka bashi sai ta zama kamar sun sake busar masa da zuciya ne ta yanda bai jin shakkar tunkarar kowane irin haɗari na rayuwa, daga nan kuma nasarorinsa suka fara bayyana har zuwa matakin da yake a yau.
Shi Dodo ne a idon wanda bai san ainahin halinsa ba, saboda a kallon fuska kai tsaye zaka kirashi mugu ne. Baida fara'a, bai san wasa ba koda da aboki ne. Duk wanda kaga yace maka yaga yana dariya lallai ya kai ai masa barka. Yana magana idan yaso, idan kuma bai so ba zaku iya kwashe awanni tare koma sama da haka bakinsa bai furta komai ba na hira sai dai kaji yana karatun Alqur'ani. Dan kuwa yana da addini sosai, hakama ilimin addinin. Tabbas da ace bai zama soja ba sai dai a kirashi malami, a yana sojan ma yana koyar da sojoji ilimin addini, kuma yana musu majalisi, sannan yana cigaba da neman nashi ilimin shi kansa.
Sai dai sirrin da mutane basu sani a kansa ba sai shi amininsa da mahaifiyarsa shine haƙuri. Zak-Shadow mutum ne mai haƙuri kwarai da gaske. Sannan mutum ne mai adalci da son tsayawa akan gaskiya komai ɗacinta. Yana da tausayi matuƙa musamman akan mata da yara. Zai iya saida rayuwarsa akan su. Sannan yana da kishin addini da yankinsa. Dan shi kai tsaye ma zai ce maka yana fara jin kishin yankinsa ne kafin ƙasa gaba ɗaya....
“Ka dinga tunani kamar wani mace”.
Buɗaɗɗiyar muryarsa ta dawo da Imran daga doguwar tafiyar tunanin da yayi. Cikin ɗan sauke numfashi yace, “Ai tunaninka nake yi”.
“Rashin aikin yi ne yay maka yawa da har zaka zauna tunani na halan?”.
Cewar Zak-Shadow yana ficewa a tantin. Tashi Imran yay yabi bayansa. Kamar ɗazun yaran sojin suka shiga kamewa da sake nutsuwa waje guda. Yanzu kam sunfi ɗazun yawa. Da alama wasu dama suna a cikin tantunan ne shiyyasa. Inda yake zaman yin alwala ya nufa, hakan ya tabbatar musu lokacin la'asar yayi, ruwa aka kawo masa shi da Imran, suma suka shiga haramar yin tasu musulman ciki kenan. Wanda ba musulman ba kuma suka amshi duty ɗin zagaye wajan. Koda suka idar da sallar shi da Imran sansanin suka bari gaba ɗaya, sun jima kafin can su dawo suna hirarsu.
Wajen wani ɗan bukkan kara dake gefe suka nufa, koda ya buɗe buhun da akayi labule a bukkar wasu irin garƙama-garƙaman karnuka ne marasa ƙyawun gani, sai dai kallo ɗaya kai musu dole ne hankalinka ya tashi, dan babu tantama waɗan nan idan suka kama mutum sai kufan jinin jikinsa amma ko ƙashi bazasu bari ba, dan marabarsu da zakuna ƙalilanne. Aiko suna ganinsa suka fara zallo da haushi kamar wanda suke gaishe shi.
A mamaki na sai naga ya ɗaga musu hannu yana faɗin, “Good Afternoon my Boys”.
Wani haushin suka ƙara yi a tare kamar masu amsa masa. Imran yay dariya da faɗin, “Kama yaran nan naka training mai wahalar gaske. Idan suna wani abun sai ka rantse mutane ne”.
Ƙaramin Murmushi Zak-Shadow yayi da ɗan taɓe baki. Idan yayi murmushi ƙyau yake masa, maybe shiyyasa baya son yi. Sun jima a wajen karnukan sannan suka fito, lokacin duhun magriba yayi. Yanzu kam sojoji ne sosai a camp ɗin, gaba ɗaya sun fito daga tantunansu, ashe a ɗazun wasu basa wajen shiyyasa, wasu kuma na barci, dan maimakon barcin dare su na rana sukeyi saboda tsaro. Tunda Imran da Zak-Shadow suka fito gaba ɗaya wajen yay tsitt kamar an musu tsawa, kowa ya nutsu. Kallo ya bisu da shi kaf ɗinsu, a ƙalla sun kai su ɗari, dan wasu basa a cikin sansanin a yanzu suna kan aiki a cikin jejin tako wace kusurwa. Wanda ke nan tare da shi bazasu wuce ɗari ba. Wucesu yay ya zauna kan dutsin da yake zaman yin alwala akoda yaushe, ai da sauri wani ya kawo masa ruwa dan in dai kaga ya zauna a wajen alwala zai yi. Daga nan kowa ne ya fara ƙoƙarin yin alwalar, sai wanda ba musulmai ba suka sake amsar dutyn zama garkuwa a yanzu ma kamar dai ɗazun. Sanin yau zai bar jejin kuma baya son su fahimta sai ya ce yanzu ma Imran ya jasu salla. Hakan baisa sun zargi wani abu ba suma, dan yana yin hakan a kowane lokaci, ba oga Imran ba har a cikinsu yaran masu addinin kan jasu salla, duk da dai duk wanda ke a ƙarƙashin Zak-Shadow duk iskancinka da sakacinka ga ibada wlhy sai ya saita maka haukan kanka. Dan in har kana cikin tawagarsa bakai ba wasa da salla, ba kai ba shaye-shaye koda na sigari ne kawai, bakai ba zama da jahilci dole ka cigaba da neman ilimin addini, shiyyasa ma ya saka musu ranakun karatu, bashi kuma kaɗai bane malamin harda wasu a cikin yaran masu ilimi na koyarwa suma, sai dai in ana kan matsannacin yaƙi ne. Hakan yasa Alhamdullah hatta wanda ba musulmai ba a cikinsu zaka gansu a nutse. Dan in ma kace zaka bijire kayi jikinka ne zai gaya maka a hannunsa..
Bayan sunyi sallar magriba Imran yay musu nasiha kamar yanda suka saba, har zuwa lokacin isha'i. Bayan an idar kowa ya miƙe suka kasu group-group dan kowa da abokansa da kuma abokan maganarsa suka kunna wuta suna hira, wasu na cin abinci. A lokacin ne Zak-Shadow ya sulale ya bar jejin, barin da da yasan sakamakon da zai so da shi da bazai yi ba. Dan kuwa tabbas wannan barin shine mafarin wata babbar ƙaddara da alkalami ya jima da rubutata a cikin rayuwarsa tun yana cikin Ummiensa.........✍🏼
*_Wace ƙaddara ce wannan? Mizai faru? Mike shirin faruwa ne da Zak-Shadow 😭. Ya labarin mace mai ciki kuma? Wace rawa zata taka mana a wannan labarin?. Amsar ku na cikin labarin KIƊA A RUWA MAI MAGANIN DODO. Kada ku bari a baku labari. Dan ni kaina Bilyn ku labarin nan tsumani yake yi💃💃💃._*
_Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._
*_NIGER🇳🇪- (500 Fcfa)_*
*_+227 98 94 12 81_*
*_My NITA_*
_Shaidar biya👇_
*_Whatsapp number_*
*_+227 98 94 12 81_*
*_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_*
*9032345899*
*_Moniepoint MFB_*
*_BILKISU MUSA IBRAHIM_*
*_KATI MTN (1k)_*
*_09032345899_*
*_Shaidar biya: 👇_*
*_Telegram Number 09032345899_*
*_AREWABOOKS (Vvip)_*
*_Chapters & Audio_*
@BilynAbdull
*_WHATSAPP (500)_*
*1487616276*
*_Access Bank_*
*_Bilkisa Ibrahim Musa_*
*_Kati MTN:- (500)_*
*_09032345899_*
*_Shaidar biya:-_*
*_Whatsapp Number +234 805 568 7449_*
*_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_*
*_WhatsApp Number 👇_*
*+234 805 568 7449*
*_Telegram Number👇_*
*+234 903 234 5899*
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu 😭🙏_*
[10/3, 1:48 AM] Zeenaran 😘: *_Typing📲_*
*_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_*
*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*
*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._
_Chapter 4_
*_Free page_*
_______________________
https://chat.whatsapp.com/GCVmfFguMEf49AFrOjSiMt
IMZEEDVENTURE
Duniyar kayan kitchen ƴan yayi dake maida mata ƴan ƙwalisa a gidajensu.
Shin kuna Neman in da zaku samu luxury kayan kitchen masu kayatarwa?
Kayan yara masu kyau unique na yan gayu?
To shiga link din grp na Imzeedventure🥰🥰🥰 Kisha mamaki🗣️ idan baki da kudin siyan kayan Yaro sabo to zaki iya yin order na kayan gonjo dinta mai Kama da sabo!
Idan kuma kayan kitchen ne baki da kudin siyan nan take to har adashi GATA tanayi🥳🥳.
IMZEEDVENTURE wata sabuwar duniyar ƙyale-ƙyale ce da ƙayatarwa da mata sukafi buƙata musamman ƴan ƙwalisa da son gwangwaje kawunansu harma da iyalansu.
Gaji ya kori ji, garzaya ki shiga wannan link ɗin namu dai domin ganema idanunki.
https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1.
Koki tuntuɓemu ta wannan layin *_+234 707 753 2253_*
Muna da account aTikTok@imzeed _venture.
https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90A6JG1PvXe&_r=1
Karku bari ayi babu ku,😘😘😘😘😘 Nima Bilyn Abdull tuni na antaya🏃.
__________________
*_TELEGRAM GROUP_*
https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk
*_WHATSAPP CHANNEL_*
https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F
*_TIKTOK_*
https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/
*_INSTAGRAM_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv
____________________
.........Gaba ɗaya hankalin yaran sojojin ya raja'a akan taɗi da jin ɗumin wutar da suka kunna. Amma shi yana gefe a saman wata bishiya ko tsoron dare baya ji balle wasu halittu daka iya fakewa a bishiyar koma aljanu. Shi ɗin ɗaya ne daga cikin amintattun yaran Zak-Shadow, dan haka duk wani motsinsa na yau da kullum zuwa yanzu ya haddace shi. Yakan fahimci yaren idanu daga Zak-Shadow, ya kan fahimci na gangar jiki harna ɗabi'a. Tun lokacin daya kai masa dawar daya zubama tsuntsaye ya fahimci akwai damuwa a tare da shi, dan haka ya laɓe yana nazartar shi, sai kuma akai sa'a aka kira wayarsa a lokacin, dan haka duk wayar da yayi acikin kunnensa take, duk da ba wani surutu ya zuba ba, amma da yake yana ankare da sai ya saka ma komai alamar tambaya. Sai kuma gashi da za'ayi sallar magriba yaga Major Imran Abbas ne yaja sallar, dan haka zuciyarsa ta bashi Lieutenant Colonel na shirin barin jejin kamar yanda ya saba fitar ɓadda sawu da tunanin basa fahimta. Eh tabbas basa fahimtar, dan a duk sanda suka daina ganin gilmawarsa kawai abinda zuciyarsu ke basu yana zagayen sauran sansanin ne ko meeting da sauran jagororin sansanin wato Captains, dan yakan yi hakan akai-akai. Dan kuwa runduna guda ce a ƙarƙashinsa dake rarrabe a cikin jejin da suka kai a dadin dubu ɗaya da wani abu, kuma shine Boss gaba ɗaya da suke ƙarƙashin umarninsa, Major Imran Executive Officer, sai Captains da su na ƙasa, duk da dai suma yaran hawa-hawa ne, kamar shi yana cikin Lieutenants. Akwai Sergeants na ƙasansu, akwai kuma Soldiers (rank-and-file).
Tun asali tun fari shi dama ya shiga aikin soja ne badan kishin ƙasa ba, dan kamar an ƙirƙireshi ne saboda manufar da yake akai a yanzu, kafin ma ya shigo aikin an bashi horo na musamman ta yanda yake iya duk wani aikin munafunci da leƙen asiri cike da wayo, musamman akan Zak-Shadow a yanzu, kuma yana da tabbacin akwai ire-iren sa ma dan bashi ɗaya bane kuma suna tare da Zak-Shadow ɗin kusa sosai dama wasu manyan jami'ai irin Zak-Shadow ko na sama da shi harma dana ƙasa da shi batare da su sun sani ba. Koda yake kwanaki an taɓa kama ire-iren nasu aka kuma hukunta shi da hukunci mai girma, dan amanar gidan soja ta wuce tunanin mai tunani, su kansu a lokuta da dama suna wannan sheɗancin ne a tsorace, matuƙar tsoron gudun randa zata tashi musu. Amma maƙudan kuɗin da ake biyansu da shi na tunzurasu da assasa gurɓataccen tunaninsu da jagorancin shaiɗan. Balle shi dake a ƙarƙashin babban ZAKI, dan bafa a banza aka saka ma *_ZAK-SHADOW_* ɗin wannan sunan ba a gidan Soja, Zakin ne na gasken gaske da ya ciyo sunan tunma a asalin sunan yankan sa. Maybe shiyasa ma sunan ke da tasiri sosai a rayuwarsa da ɗabi'arsa. (ALLAH ya ƙara kare ku jami'anmu a duk inda kuke🙏. Kai mutane na ku ba MAZAJEN FAMA jinjinar ban girma mana💪😄, a haɗa musu da kirari na musamman kuma, ƙarshe a sara musu👍🏼).
Waya ya zaro daga jikinsa, ƙarama ƙirar nokia, ya dannama wata number kira. Ba'a ɗaga ba sai da ta kusa tsinkewa. Murya ƙasa-ƙasa ya furta, “Good evening Sir!”.
Amsa masa da akai daga can ya sashi cigaba da magana cikin tsantseni da risinar da kai tamkar yana a gaban wancan ɗin.
“Sir! Yau ɗin nan ya fita. Dan sanda na kai masa dawar da yake zubama tsuntsaye bayan nabar wajen sai na laɓe, naji yana waya da matarsa kamar.....”
Sai kuma yay ɗan jimm alamar saurare. Kafin cikin yaƙini da son a yarda da shi ya cigaba da faɗin, “Tabbas na tabbatar baya jejin nan, dan yau ba shine yaja sallar magriba da isha'i ba. Na duba inda ake ajiye mashin ɗinsa kuma babu shi, na leƙa tantinsu oga Imran ne kawai a ciki, kuma in dai ba ana kan aiki ba baka raba su. Duk da haka na bincika dukkan sauran sansanin kuma an tabbatar min bai je ba”.
Sai kuma yayi shiru.
Zuwa can ya sake cewa, “Yes Sir!”. Daga haka ya cire wayar a kunensa yana murmurshi, yasan yau account ɗinsa sai yayi rawar girgiza kwankwaso saboda manyan kayan da zasu shigo cikinsa akan wannan albishir ɗin. Sakkowa yay a bishiyar ya koma cikin ƴan uwansa, koda abokinsa da bai san ainahin shi munafuki bane ya tambayesa daga ina yake sai ya nuna ya zagaya ne yin uzuri, dan haka babu wanda ya kula suka cigaba da hirar su......
_____________
A can ɓangaren wanda ya kira kuwa yana yanke kiran wata number ya lalubo ya danna mata kira shima. Ana ɗagawa ko gaisuwa bai tsaya yi ba ya fara magana kai tsaye.
“Congratulations Aboki, yau dai mun samu damar da muka daɗe muna fako tun a watan jiya, dan na samu tabbacin barin yaron nan jejin yanzun nan”.
Daga can aka furta, “Woow Zak-Shadow!, damar da aka daɗe ana jira kace ta samu. Lallai yau rana ce ta musamman a garemu, dan kuwa na tabbatar zamuja kaya iya kaya akan wannan albishir. Ba damuwa yanzu zan sanar da oga kuwa ai ba zancen wasa faka-faka kawai Aboki”.
Dariya yayi irin ta nasara shima, sai kuma ya ce, “Okay hakan yayi, amma abokina kadai tabbar babu matsala ko? Karfa mutanen nan su ci amanar mu. Bayan mun saida ƙasarmu sun sami biyan butarsu su zubar damu a banza batare da mun mori komai ba sai dukiya. Kasan fa halin ɗan Adam na wannan zamanin da wayo da iya cin amana, sannan mutanen nan a ankare suke komai nasu a tsare yake. Yaron nan yaron ƙasarmu ne na amana da kowa ke da hope a kan jarumtarsa, ba gidan soji da shugabanni kaɗai ba hatta al'ummar ƙasar nan ɗaukarsa suke kamar wani WALIYYIN SOJA”.
“Mtsoww!! Wato abokina wataran sai naji kana bani haushi. Wai miye damuwarka da batun wata ƙasa can, ƙasar data kasa gamsar da kai koda da albashin wahalar aikinka, su su minene ma kace duk basu suka so mu kasance a wannan hanyar ba, eh su suka so mana, tunda ai basai sunce muje mu aikata ba, sun gama tattare komai daga su sai ƴaƴansu da matansu dake ƙasashen waje. Muko an barmu da ɗumama kujera basir duk ya gama cinyemu”.
Dariya sosai wancan ya kwashe da ita, tare da faɗin, “Wlhy baka da dama, aiko bamace muna cikin masu ɗumama kujerar nan ba, dan mumafa tun farko karka manta munja kayan nan gwargwadon iko a gwamnati ta hanyar fakewa da ayyukan mu, kai dai a rufe rufau kawai. Ba lokaci faka-faka ka sanar dasu, kasan Yaron nan shegen kansa ne akwai wayo, komai a ankare yake yinsa”.
“Tabbas hakane. Ka bani 5minuts kawai, aikinka ya kammala a wannan gaɓar zakaji alert tare dana yaron shima”.
“Okay yayi, byeee!”. Ya faɗa yana ajiye wayar fuskarsa cike da murmushi, sai dai can ƙasan zuciyarsa wani kalar luguden daka take yi. Tabbas yasan wannan halayyar tasu mummunar halayya ce kuma abar ƙyama da duk wani ɗan ƙasa na gari bazai aikata ba koda a wanne addini yake kuwa. Sun rufe jinsu da ganinsu saboda dukiya, sun manta da basu da inda yafi ƙasar a wajensu, anan aka haifi kakaninsu, haka iyayensu, suma haka, sun kuma haifi ƴaƴansu. Amma sam basa tunanin makomar ƴaƴan nasu da ƴaƴan ƴaƴansu, su dai kawai su tara kuɗi a kirasu masu dukiya. (Lallai UBANGIJI mai rufin asiri ne, dan tabbas da wani zai san wanene ai nahin kai a take zai danneka ya maka yankan rago koda da wuƙar yankan albasar gidansa ce. Amma wata hikima ta ALLAH sai kaita warkajaminka cikin al'umma ana girmamaka batare da ansan girman na riga bane kawai. Anya waɗan nan sunma kansu adalci kuwa?, summa shugabanninsu adalci da a kullum talaka ke ƙalubalanta da gazawa batare daya san ba laifinsa bane shi kaɗai, dan da yawan tsiyatakun da irinsu da ba'a tunanin zasu iya dasu ake haɗa kai ayi ba shugabannin da kullum ake kallo da zargi kawai ba. Yanzu kamar dai shi da abokinsa, ba shugabannin komai bane na siyasa, kawai ma'aikata ne a ƙasa da suka samu dama ake