n duba kayan tasan yaje inda zai je.
tun shigowarsu gate Fillo ta dage sai sun wuce inda ake zubar da bolar gidan sun zubar da maganun, wanda zatonsu abinda ya faɗa hakan yake. kuma sai da suka je zasu zubar ne suka tsaya suna kallon uban kayan da mamaki.
leda ɗaya tulin kayan ƙwalama ne kamar hauka, madara, snacks da choculates da lemukan kwali, tarkace dai iri-iri. sai ɗayan ledan kuma kayan makeup ne aciki, shower gel manyan roba guda biyu wanda mutum sai yafi wata yana wanka da roba, sai lotions da su powder, duka dai dangin kayan kwalliya, kuma da gani kuɗi ne ba na wasa ba aka kashe wajen sayayyar.
Fillo ta shiga parlon da sallama tana tafiya a hankali, kanta a ƙasa sai jan yatsun hannunta take yi, Hajiya Madina na zaune akan kujera, ƙafafunta duka biyu akan tum-tum, Sameer na zaune a gaban ƙafafun nata ya tankwashe ƙafa yana yanke mata farcen ƙafarta. sai Nihal dake ɗaya kujeran a zaune tana duba wata handout, daga dining area kuma Zaytuna ce a zaune tana danna waya.
Fillo ta ƙarasa ta durƙusa a gefen kujera tana gaida Hajiya Madina. Hajiya Madina ta ɗauke idonta daga karanta story book ɗin da take yi ta kalli Fillo tana amsa gaisuwar tata.
"Halimatu anji sauƙi kenan". tace,"ehh Maama na wartsake gaba ɗaya". "to masha'Allahu, Allah ƙara miki lafiya. kina da ƙwarin dai da zaki iya aiki ko?". Fillo tace,"ehh Maama".
Hajiya Madina ta gyaɗa kanta, tai shiru for some seconds sannan tace. "to jiya an kawo miki ƴar'uwa da zaku ke aikin tare, ta kammala komai tun ɗazu, yanzu sai ki tashi kije lesson teacher ɗin ku yazo, idan kuka kammala ke sai kiyi aikin rana".
wani daɗi ya mamaye Fillo, ko babu komai burinta na yin karatun boko zai cika, abunda mahaifinsu ya kasa yi musu yau wasu bayin Allah zasu mata shi. tunaninta ya tafi can wani lokaci baya, tana wannan tunanin taji Hajiya Madina na ƙara cewa,"dan Allah ku mayar da hankali kunji ko, abunda za'a muku a makaranta shi zai muku, kuɗi masu yawa aka biyasa, akwai percentage ɗin da za'a ke cirewa a cikin kuɗin aikinku, so idan kun mayar da hankali akan karatun kanku kuka taimaka, idan kuma kunƙi kunwa kanku asara babba".
Fillo tace,"insha'Allahu Mama zamu mayar da hankali, insha'Allah ba zan baku kunya ba zanyi abinda kuke so nayi". Hajiya Madina ta jinjina kanta. a lokacin sabuwar maid ɗin da aka kawo ta iso wurin ta tsuguna kusa da inda Fillo take. tace,"Hajiya gani".
Maama tace,"yauwa ga ƴar'uwar aikin naki nan. ki bata nata reading materials ɗin da Zaytuna ta baki ɗazu, sai kuyi maza ku wuce me karatun na can na jiranku, awa biyu zaku dinƙa yi, da zarar kun kammala ku yo cikin gida, a kama kai bana son shashashancin banza if not zan sallami yarinya".
duka su biyun suka amsa da,"to". sannan Fillo tace,"aina zamu sami Malamin?".
Nihal tace,"ku tashi muje let me escort you". ta faɗa tana gyara zaman glasses ɗinta, da gyara dogon wandon dake jikinta.
"je ki ɗauko littafan naku". ta faɗa tana nuna Ɗausiyya ɗaya ƴar aikin. da ganinta tana da hanzari akan yin abu, dan cikin sauri ta ɗauko ta dawo, kuma kallo ɗaya zaka mata zaka san she is typical ƴar ƙauye, balle kuma ka kai ka ga kallon the way take abubuwanta, maganarta duka hi da ha ne, jiya ana kawota Hajiya Madina tasa Baba Jummai dake kawo mata ƴan aiki ta kaita saloon aka wanko dattin kanta, kuma suna dawowa tasa tai wanka me kyau da dettol da turaren ƙamshi. haka Hajiya Madina take, bata nuna ƙyama ko ƙyanƙyami ga duk yaran da ake kawo mata, karɓarsu take ta nuna musu hanyar gyara kawai.
Nihal na gaba suna biye da ita a baya, zasu fita daga falon Zaytuna ta kira sunan Fillo, ta waigo tana kallonta bayan ta amsa kiran. ta mayarwa da Zaytuna murmushin da take yi mata. "i wish you all the best in your studies dear". abinda Zaytuna tace mata kenan, kuma kamar yanda bata fahimci me tace ba haka itama Zaytunan ta fahimci bata san abinda tace mata ba.
Zaytuna ta ƙara mata wani murmushin tace,"ina yi miki fatan alkhairi a karatunki, Allah ya bada sa'a". kan Fillo na ƙasa tace,"amin ya Allah, na gode Adda". da haka tabi bayan su Nihal da suka riga suka fice.
awa biyu suka ɗauka suna karatun kafin su gama, kuma sosai Fillo ta gane duk abinda aka koya musu ɗin, karatun ya mata daɗi fiye da yanda ta tsammata, ashe shima karatun boko haka yake da daɗi?, shi kansa teacher ɗin nasu sai da ya mata kyautar biro, har yana tambayarta ko ba yanzu ta fara ɗaukar darasi ba, dan ko da ya basu class work guda biyu ta faɗi a examples ɗin da ya ce su bayar, rubutun ta kuwa baka ce wacce ke koyo ba, Ɗausiyya ce yay ta fama da ita, to itama kuma da yake tana da kishi sai da tai ƙoƙarin iyawar. teacher ɗin nasu ba bahaushe bane, amma yana jin hausa sai dai bata kama bakinsa sosai ba. yay da hausa ya haɗe da turanci, su gane hausar da yake yi su bagarar da turancin nasa, idan ya faɗi wani abin da hausa Fillo har gimtse dariyar dake taho mata take yi. dan da ace ita da Maijidda ne ma sai sun saki kayarsu.
suna komawa sallah kawai