kuɗin da Kaka ke fatan su samu ta cika burinta na siya mata fili, da kuma jarin da zata samu sana'ar yi.
cikin zazzaƙar muryarta ta fara biyo masa haddar karatun da yake biya mata kullum, acikin ƙira'a me daɗin gaske, kuma tartilan tajwidan, kace wata balarabiya. haka tai ta biyawa har sai da ta kawo inda suka tsaya sannan tai shiru, ta buɗe ƙur'anin yay mata ƙari.
yau ko tajweed ɗin bai biya mata ba ya miƙe yana mata sallama, muryarta a raunane tace,"tun yanzu?, kuma ba zamu yi tajweed ɗin ba? kayi haƙuri dan girman Allah".
bai juyo ba daga tsayen da yake, hannayensa na aljihu idanuwansa a kulle. abinda ba tai zato ba abinda bata taɓa tsammata ba daga gare shi, magana ce ya faɗa guda ɗaya tal, amma magana ce me zafi, wadda take daidai da tsawon kalmomi fiye da dubu, zafinta ke dai-dai da sukar mashi a ƙahon zuci. bata san lokacin da ta miƙe tsaye ba, ƙafafuwanta na rawa suna neman su gaza ɗaukarta, kallonsa take amma wani Amir ɗin na daban take gani ba Amir ɗinta da ta sani ba. tasan dai ɓacin rai kan iya saka mutum yay komai amma batai zaton ɓacin rai zai iya sa Amir ya huda ƙirjinta da kibiya ba.
zata jure komai ba, amma ba zata juri maganar ba, cin fuska baya ɗaya daga cikin abinda zata ɗauka, dole zata mayar masa, dole itama ta saka masa ɗacin da ya saka a tata zuciyar, ya kamata ace shima yasan wacece asalin Fillo, wannan Fillon da bata ɗaukar wulaƙanci daga ko waye, duk kuɗinka, mulkinka, matsayinka, muƙaminka, basu zasu hana ta rama abinda akai mata ba. ta tattaro sauran courage ɗin da take da shi, laɓɓanta suka tale da niyyar yin magana daidai lokacin shi kuma ya juyo ya fuskance ta.
taja dogon nunfashi ta sauke, ta haɗiye wani abu da bata san menene shi ba, ta dunƙule hannunta da zuciyarta ke ingizata akan aikata abinda dole zai saka tayi da na sani.
Amir kallonta kawai yake yana ganin yanda take haɗa zufa duk da iskar dake kaɗawa a wurin, ɓacin ran dake fuskarta na haɗewa da jin zafin abinda ya faɗa mata acikin zuciyarsa, yana jin tamkar wuta ce ke ruruwa a tare da shi, me zai ce yanzu?, ta ina zai fara?, me zai faɗa mata da zai goge tabon da dasa mata yanzu?.
_"akwai abinda bai sani ba, tabbas akwai abinda bai sani ba a tare dake, ki faɗa masa hakan Fillo"._ abinda zuciyarta ke faɗa mata kenan, sai dai at the moment da ta ɗago kai suka haɗa ido sai komai nata ya ruguje, dukkan plan ɗinta na cin zarafinsa ya rushe, ta sauke idonta ƙasa tana jin ba zata iya komai ba, ba zata iya yiwa wannan mutumin komai ba, wannan mutumin dake gabanta ba ɗaya yake da kowa ba a duniyarta.
ta duƙa ta ɗauƙi qur'anin da dardumar ta juya zata tafi, sai taji muryarsa a sanyaye ɗauke da sautin nadama da danasi yana cewa,"dan darajan Allah kiyi haƙuri ki yafe min, ba laifina ba ne, na kasa controlling zuciyata ne".
Fillo taji wani dunƙulen abu ya tsaya a maƙoshinta ya hana yawu wucewa, halaccin da Amir yay mata ba zata manta da shi ba, amma bata jin ko me Amir zai faɗa mata ayanzu zata iya ci gaba da tsayuwa a wurin nan, bata jin akwai wani mahaluƙi a wannan duniyar da ya isa ya hana ƙafafuwanta takawa ta bar wajen nan, ba zata saurare shi ba, ba zata taɓa sauraronsa ba, kuma ba zata ƙara zuwa wurin nan ta tsaya ba wai saboda Amir, ko da ace kuwa gawar Amir ce.
tana ɗaga ƙafarta taji yace,"ki tsaya ki fahimceni dan Allah". a ranta ta maimaita ta tsaya?, yana nufin ta tsaya su fuskanci juna ya bata haƙuri ta haƙura?, ai ba zata taɓa tsayawa ba balle ƙwayar idonsa ta karya alwashin data ɗauka. cikin ƙunar rai ta bar wajen, tana ji yana ƙwala kiran sunanta yana roƙonta, kuma wannan kiran sunan nata da roƙon da yake mata na dawo mata da rayuwar ta a baya, yana tuna mata wani lokacin a can baya, lokacin da ta haura katangar gidansu ta dire, cikin duhun dare ba da rana ba.
har ta isa ga ƙofar shiga ɓangaren nasu Amir bai daina kiran sunanta ba, kuma duk da irin tazarar dake tsakaninsu bata bar jin kiran sunan nata ba a bakinsa, kiran sunan da take jinsa ba daga muryar Amir ba, daga wata murya ta daban, muryar Yayanta abin ƙaunarta Hamid, Hammah Hamid. ayanzu Kaka kawai take lissafawa wadda ta rage mata a cikin rayuwarta, amma duk ranar da Kaka ta faɗi ta mutu to tasan tana da Hamid, shi kaɗai take da shi ko da ace kuwa har lokacin Hayyo na raye.
tun da Kaka taga ta shigo ɗakin a fusace tai shiru bata tanka mata ba, tana kallo ta wurgar da dardumar da ɗankwalin tai cikin ɗaki da qur'ani a hannunta, ko sallama ba tai ba.
Kaka ko ta girgiza kai a fili tana faɗin,"Allah ya shiryaki, banda me ƙaunarki wane zai miki wannan gatan na ɗaukar ɗawainiyar yi miki karatu kullum, karatun ma na qur'ani, kuma ba biyansa kike ba, ya kashe uzurinsa da lafiya ko babu yazo ya koyar dake, shi ɗin ma dai da zai iya kenan, idan wani ne tuni bai rabu dake da wannan halin naki ba...kina asibiti yaron nan sai daya zama kamar marayan da bai da gata".
Maijidda ta shigo bakinta ɗauke da sallama, Kaka ta amsa mata. a tunaninta ko Fill