numfashi yana barin kallonsa ga tuƙin da yake, a hankali yace da ita. "Maama dan zatin Allah kiyi shiru ki daina wannan kukan, wallahi yana ɗaga min hankali, stearing nan nema yake fa ya ƙwace a hannuna".
tasa gefen hinabinta ta goge hawayent tana so ta tsayar da kukan. ta ɗago ta kalle shi idanuwanta duk sunyi jawur sun yi girma. cikin sanyin murya kuma a raunane tace da shi,"to ka kira min Baffan naku".
ya rufe idonsa ya buɗe ya sauke agabansa, da zafin nama ya kaucewa bishiryar daya kusa duka. ya furta subhanalla sannan yace,"Maama na faɗa miki insha'Allahu babu wani abu da zai sami Hammah, shima nasan bige mutum ɗin da yay ne yasa ya rikice har yake faɗa miki bai san a inda yake ba...".
ta katse shi da cewar,"ni dai idan ba zaka kira min Baffan ba to ka faɗa min, sai na sauka na nemi masu waya su ara min".
yace,"to me za kice masa?".
ta ɗan kalle shi yana mata abu kamar ba ɗanta ba, sai tayi shiru bata ce masa komai ba. shima shirun yayi, can ta ƙara cewar,"yanzu dai ba zanci arziƙin wayar taka ba Khalill?".
buɗar bakinsa yace mata,"kina so ki rasa mijinki ne?". ta girgiza kai da sauri. "to ki haƙura da wannan kiran dan baida amfani, kin san dai Baffa ya fiki shiga tashin hankalin akan lamarin daya shafi ƴaƴansa, yanzu idan kika faɗa masa ya yanke jiki ya faɗi a inda yake fa?, kin san dai yanda ba kya kusa da shi ɗin nan anything can happen. so kiyi haƙuri har mu ƙarasa ai mun kusa zuwa, na kira mijin Inna Falmata yace ga police nan da ambulance zasu biyo mu a baya, dan Allah Maama kiyi haƙuri kita adu'a kawai kinji uwa ta gari".
ta gyaɗa masa kai kawai tukunna tace,"to amma baka sauri ka ƙara speed". yace,"to Hajiya Maama yanzu kam za kiga mun isa...ai wurin ba wata tafiya me nisa bane".
tana kallonsa tace,"Yabayo fa Khalil". yace,"can ɗin fa, yanzu za kiga munje Maamancy, situation ɗin da kike ciki ne fa yasa ki ganin nisa".
ta kuma gyaɗa kai bata ce komai ba, taci gaba da tasbihin da take yi.
a wannan lokacin idanuwan Turaki a kulle suke ya kwantar da kansa jikin kujerar, abinda zai iya faruwa da shi dalilin accident ɗin nan ba shine damuwarsa ba, ran yarinyar kawai yake ji, baya so ta mutu, idan ta mutu bai san wanne hali iyayenta zasu shiga ba.
ya buɗe idanuwansa a hankali ya sauke su akan titin da duhun dare yasa ba'a iya hangen komai. yaji wani abu da bai san menene shi ba ya tsarga masa. ya juya baya yana kallon yarinyar, har yanzu zuciyarsa faɗa masa take da gawa yake tare, ta riga ta mutu, irin jinin da ta zubar ba zai barta ta rayu ba.
ya miƙa hannu ya ruƙo nata wanda yayi sanyi kamar ƙanƙanra, hakan ya wanzar da wani abu wai shi tsoro a zuciyar Turaki da bai taɓa ji ba tunda ya girma, babu wata shakka ta riga ta mutu yasan da wannan, shikenan haƙƙin rai ya hau kansa.
idanunsa ya kulle ya bawa kujerar duka yana jin kamar ya saka kuka. me ya yiwa rayuwa ne da take neman tayi masa ɗaurin goro, yana ƙoƙarin buɗe nauyayyun idanuwansa yaji an buɗe ƙofar motar, mamakinsa ɗaya ne ta ya aka buɗe ƙofar bayan yasa lock?, wa ya buɗe?, yasan dai 10minutes bata isa ta kawo su Maama wurin nan ba, duk da he dont have comfirmation of where he is, amma yasan ko ina ne nan da nisa yake.
kuma kafin yay wani yunƙurin juyo da kansa ga ƙofar sai yaji an daki wuyansa, duka bana wasa ba, irin dukan nan da zai yiwa jijiyar wuya lahani, ya rumtse ido saboda tsananin azabar daya ratsa dukka ilahirin jikinsa.
tabbas no any doubt wani ne zai yi attacking nasa, but wanene wannan?, and how comes aka san da wanzuwarsa a wannan dajin?.
Allah ya sa ni a situation ɗin nan da yake ciki ba shi da courage ɗin da zai iya encountering ko waye da faɗa don ganin ya ƙwaci kansa.
inda ace ba'a irin wannan halin yake ciki ba, da ace baya cikin fargaba da taraddadin mutuwar wadda ya kaɗe, to zai yi fighting da koma waye dan ganin ba'a cutar da shi ba, zai ƙwaci kansa ta ƙarfi even if ace 1% chance yake da shi, and he most win saboda ba zai taɓa bari yayi failing ba wajen kuɓutar da rayuwarsa, not becouse of burin da yake so ya cimma a rayuwa ko kuma saboda baya son mutuwa da wuri, no!, its just becouse of his Mom, Maama na buƙatarsa a raye, idan ya mutu ya barta bai san ina zata saka kanta ba, ya riga ya sani her only hope and wish is su rayu tare da shi.
but still bai karaya ba haka yasa hannuwansa biyu ya riƙe hannun wanda ke son shaƙe masa wuya, sai dai inaaa girman mutumin ya shallake tunaninsa, ko ace da kuzarinsa ba zai iya gwada jiki da shi ba.
haka yana ji ƙaton mutumin ya shaƙesa da iyaka ƙarfin da numfashinsa zai ɗauke gaba ɗaya, kuma take yaji yana neman shaƙar iska ya rasa, saboda haka kawai sai ya sare ya sallama.
yana jin mutumin na magana da wasu ta waje amma bai san me suke cewa ba, sama-sama yake jinsu. so yake yaji muryoyinsu, so yake yaji ko da kalma ɗaya ce tak ta abinda suke faɗa, ta yanda ko da Allah yasa yayi surviving zai iya samun hanyar da zai kama su.
daƙiƙa 1,2,3 ta wuce mutanen su