uma da ba za'a bar yaro ya sarara ba saboda dai an liƙa masa ƴar gwal, to shima ai ɗan gwal ɗin ne tunda Uwayensa na ƙaunarsa".
ta shiga zazzaga masifa ta inda take shiga bata nan take fita ba, har sai Baffa ya kira sunanta, a sannane ma ta tuna da batun zamansa a wajen ta manta tayi ɓarin zance irin haka akan babarsa.
yanda ya kira sunan nata tasan ransa ne ya ɓaci matuƙa, taci gaba da cin abincinta da ta ƙoshi ba tare da ta kallesa ba tace,"Allah ya baka haƙuri ya huci zuciyarka, yi haƙuri na annabi sarkin masu biyayya".
tukunna ta ajiye spoon ɗin ta miƙe tana kallon Turaki tace,"me babban suna duk sanda ta ka sami space sai kaje musu, ba qai ka matse kanka ba, sanda ka sami space nace, Allah ya baka ladan haƙuri da ladan biyayyar da kake yi".
har tai gaba zata fice sai kuma ta dakata, dan tasan muddin ta tafi ba abinda zai hana Baffa zazzagewa Turaki kwandon bala'i, kuma Hajiya Ramla babu abinda zata ce, ƙila ma yasa shi tafiyar da bai shiryawa ba ayau ɗin.
ta dawo ta koma dining ɗin ta tattara abincin gabansa tace,"tashi muje kaci acan, duk an bi an sa maka ido ka rame kana neman fita hayyacinka, ana aure ai ƙiba amma kai kai duk an tsabtareka". Turaki ya miƙe yabi bayanta suka fita, Hajiya Ramla tabi bayansu ta girgiza kai tana murmushi.
after sun kammala break fast ɗin yaran duk suka miƙe suka fita, Mum ta dakatar da Khaleel ya koma ya zauna sannan tace da Baffa,"Khaleel yaga yarinya yana so, yana da buƙatar aje a nema masa aure".
kunya ta kama Khaleel ya shiga sosa ƙeya, Beffa ya ɗan dube shi sannan ya dubi Hajiya Ramla yace,"ina ce ku keda ikon aurar da yaran ga waɗanda suke so, ai sai kuje ku nema masa ko".
yana faɗin haka ya miƙe yana cewa da Khaleel,"ka ɗauƙo key zaka kaini Government house, da sauri fa 11 muke da meating".
daga ɗakin Maama kuwa suna shiga ta dire masa abincinsa saman table tace,"ba inda zaka je wallahi, ai ba kai zaka bata lafiyar ba, in sunyi hankali sun dawo maka da matar shikenan, amma ba zaka bi sahunta ba wallahi ai ba mijin Hajiya bane kai".
ta bisa da kallo tana cewa,"nace fa babu inda zaka je daka wani bi ka damu".
ta wuce toilet ta barsa sai mita take yi.
ya ɗauki wayarsa ya kira Bello, daga ɓangaren Bello yace,"sai yanzu kaga damar waiwayata". Turaki ya sauke numfashi yace,"ba wannan ba Bello, i want you to find a solution for me, kaina ya ƙulle wallahi, i don't know how to inform them about the other marriage, ban san kallon da zasu yi min ba ban kuma san ta yanda zasu ɗauki lamarin ba, and i want to be with my wife now".
Bello ya shafa fuskarsa daga inda yake yana kwantar da kansa jikin kujerar office ɗin sannan yace,"explaining to them is not that difficult, yanda zasu ma yarda da zancen is the biggest tension, MT dole dai ka ja mana faɗan da ba zai ƙare ba at this age da muke da shi da muka wuce ai mana faɗa". yaja tsaki,"shikenan yanzu abinda kowa zai ce shine bamu da hankali, alhalin ni ban ma san sanda kaje kayi haukar taka ba, in ace ma kai ɗaya za'aiwa faɗan da sauƙi".
Turaki yace,"now you have a suggestion for me, ko kuma magana zaka ci gaba da gaya min in kashe wayata".
Bello yace,"gaka da masifa da gajen haƙuri, to haka kawai zan baka shawara ban gaya maka magana ba?, faɗan da zaka jawo min ni kuma fa?, mtswww where are you now?".
"i am at home".
yace,"are you coming to office?".
"not sure".
Bello ya sauke numfashi sannan yace,"I will come after I leave the office around six o'clock, kar ka fita kuma ka barni da zaman jiranka".
muryar Turaki a sanyaye da kuma ban tausayi yace,"Baffa can break this marriage Bello, i am afraid that will happen, ko kawai inci gaba da barinsa cikin sirri?, ita kanta yarinyar ma fa matsala ce".
cikin bada ƙwarin gwiwa Bello yace masa,"babu abinda zai raba aurenka insha'Allahu, ai da kyakykyawar niyya kayi, kuma rainonka akayi akan taimakawa, kuma karka manta kana da Maama, ita kaɗai in ka tuna kana da ita ya isa ka daina jin fargabar komai".
Turaki ya furzar da iska daga bakinsa sannan yace,"thank you friend".
Bello ya bushe da dariya yace,"ya da godiya tun ba'a sami mafita ba".
Turaki zai yi magana Maama ta fito daga toilet, yaga ta nufa wadrobe ta buɗe ta ɗauko hijab ta tayar da sallah, ya bi kiran Bello da kallo da ke tafiya, he have alot to say amma dole ya haƙura ya kashe wayar ya bari sai sun haɗu anjiman.
around 4 Turaki ya dawo yazo shiga da mota gate sai ganin Fillo yay ta fito daga cikin wata jar mota, kuma ta fito daga motar ta tsaya suna magana da na ciki ta window, yana kallon motar ya shaida ta Dr Yusuf ce, yaji kamar ya fito yaje ya bankawa motar wutar duk su ƙone. kusan 5minutes sannan Fillo ta bar wajen ta shige gida Dr Yusuf na ɗaga mata hannu ta glass ɗin da ya zuge.
motarsa na barin wajen Turaki ya fito kamar kububuwa ya shiga gidan, yanda yake tafiya kamar zai tashi sama, yana zuwa ya sha gaban Fillo ransa a haɗe kamar hadari yace,"juya muje".
tayi kamar bata jisa ba ta raɓa ta gefensa zata wuje ya wani fin