e ƙara yowa kansa ba, ya fizgo shi gabansa ya zare bindigar dake gaban wandonsa ya koma ya haye ruwan cikin Amir, ya cije fuska yana ɗaga bindigar ya bugawa Amir a kansa, ta-ke jini da ƙwaƙwalwar Amir suka haɗe wuri guda yaji kamar kansa babu komai, tukunna Turaki ya saita ƙirjinsa da bindigar yana bala'in huci yace,"for the last time i will ask you, tell me who are you?, in ba haka ba wallahi sai na sakar maka harbi a zuciyarka".
in ace da damar magana Amir zai yi, to amma ankai stage ɗin da yatansa ɗaya ma ba zai iya motsawa ba, balle kuma ya buɗe bakinsa da uban jini ya taru aciki yana tsiyayowa ta waje, shi da wannan mahaukacin dukan da Turaki ke yi masa ma da harbe shi ɗin yayi da ya huta, kuma baya jin ba zai mutu ba muddin Turaki ya ƙara dukansa, azzakarinsa kansa jini yake saboda Turaki ya daki wajen ya kuma ya daka yasa hannu ya kama ya murɗa, to ko da iyaka haka aka barsa ai yana jin sun gama ɗaukarwa Fillo fansa dan yasan ko ace ya tsira da ransa to tabbas a hoto zai tashi dan yana da yaƙinin Turaki ya gama kashe masa gaba, bai da burin da ya wuci a yanzu irin ya buɗe baki ya bawa Turaki haƙuri, kuma yaga Fillo ya nemi yafiyarta.
Turaki na ƙoƙarin sakin bullet a ƙirjin Amir B
Dsp ya taho da sauri ya bige hannunsa bullet ɗin ya sauka a kafaɗar Amir, Amir ya saki wata gigitacciyar ƙarar da shi kaɗai yaji kayarsa babu wanda yaji, don hatta wurin fitar sautin muryarsa Turaki ya gama kashe shi.
Dsp ya fizge Turaki daga kansa yay gefe da shi yana faɗin,"wa ya baka izinin yin harbi?, are a police?, to ko mu ba'a bamu umarnin yin harbi kai tsaye ba".
Turaki da duk ya gama ficewa a hayyacinsa yana ta uban huci yace,"yallaɓai na taɓa ganinsa a ƙofar gidanmu tare da ita, yafi ƙarfin rabin awa awajen kafin ya ƙyaleta ya tafi, and am sure shine ya ɓoyeta ma a yanzu, ka tambayesa inda ya ɓoyeta tun ban ƙarasa shi ba wallahi".
Dsp ya dafa kafaɗarsa yana faɗin,"calm down mana, yanzu idan muka kashe shi waye zai faɗa mana inda ta ke?, to dole mu bi komai a hankali ba wai mu ɗauki mataki mai gaba ɗaya ba".
Turaki ya dunƙule hannayensa duka biyun yaja da baya yana zaunawa kan kujera tare da fesar da zazzafar iska daga bakinsa.
ya rumtse idonsa sosai yana ɗaga kansa sama, ba komai yake hangowa ba sai sanda Amir ke tare da Fillo, muryarsa na fita a hankali yace,"Fulani where are?, bana ce miki zan zo ba yanzu, why did you leave?".
sai ya rumtse idonsa yana tunawa da maganar da ta faɗa masa,_"wai sai sunyi amfani da ni"._ bai san lokacin da daki hannun kujerar ba har sai da ƙashin hannunsa yayi ƙara.
ya kifa kansa a hannun kujerar yana faɗin,"ina kika tafi?, Fulanii why?, why Fulani?, how do you think i will survive without you by my side?, please tell me where you are zanzo na ɗauke ki ko da ace daga na ganki zan mutu".
ya faɗa a sanda wannan jarumtar tasa ta karye, raunaninsa ya wanzu, kukan dake can ƙasan zuciyarsa ya ɓalle, hawaye ya sauko masa ƙwayar idonsa na haska masa hotunan faruwar abubuwa kala-kala a tare da Fillo.
"idan kika tafi da wa zanyi rayuwar farin cikin gidan aure irin wadda na tsara mana ni da ke kaɗai?, wa ye zai tayani nemo Mum idan ba kya nan?, dan Allah karki min nisan da ba zan saka miki da ceton rayuwata da kika dinƙa yi ba".
sai kawai ya cije leɓensa na ƙasa ya kuma yin kukan kura yay kan Amir a fusace, da hanzari police suka ruƙo shi akai waje da shi.
*A dai-dai wannan lokacin.*
gudu suke sosai babu waige babu tsayawa har sai da suka ga cewar sun shigo cikin gari, kuma a lokacin ne Fillo ta faɗi tana kuka tace,"Mum ba zan iya ba na gaji".
tausayin kansu ya kawo zubar sabon hawaye saman fuskar Hajiya Ramla, ta duƙa ta kamo Fillo tace,"ki daure mu ƙara yin gaba, kinga nan wajen ma ba kowa zasu iya kama mu anan".
Fillo tace,"Mum ki barni ke ki tafi, su Adda Zaytuna suna can suna jiran dawowarki, Turaki kullum sai yayi kuka akan rashinki, dan Allah ki tafi Mum ƴaƴanki na buƙatar ganinki a raye".
Hajiya Ramla ta dafe kanta da ta-ke jin wani abu na mata yawo aciki, so ta-ke ta ɗauki magangun yarinyar ta saka su a ɓangaren tunaninta ko Allah zai sa ta gane abinda ta-ke cewa.
kuma kamar gimlawar Jinnu haka Hajiya Ramla taji maimacin furucin da Fillo tayi acikin kanta. ta dafe ɓarin kanta tana ta ambaton Allah har sanda taji wani abu na tafiya acikin kanta yana fitowa yana barin jikinta. lokacin kuma ta saki ƙara tana dafe kan sosai tana ƙara ambaton Allah.
wucewar daƙiƙa biyu ta buɗe idonta ta sauke su a wurin da ta-ke, hankalinta da tunaninta da suka dawo dai-dai suka fara tambayar a ina ne nan ɗin?.
magana ta farko da ta fara tunawa kamin gushewar hankalinta itace,_"ni Fulani Azima ni ce nayi miki asiri Ramla, saboda kin aure min farin cikina, dan haka kamar yanda na rasa Dikko kema kin rasa shi har abada domin asirin dake kanki har ki mutu ba zai barki ba, ƴaƴanki kuma zan saka su a tafin hannu dan suma sun shiga gonata tun da har ubansu yay kuskuren haifarsu da wata ba ni ba"._