cike da rashin imaninsa yasa ƙafa ya ta-ke ƙafarta yace,"ka san menene yaro?, ko iyaka motan gidanku da muka ƙwamusoka daga wajen da muka ganka ranar idan siyar da shi za'ai ya haura sama da miliyan asirin, saboda haka ku daina ce mana baku da shi. for the last time zamu kira waya ka faɗa a gida kace aciko mana miliyan uku, ana cikawa mu kuma munyi alƙawarin zamu sake ka".
cikin tsananin azaba da wahalar da take ji tace,"ni Kakata kawai nake da ita a duniya, bayan ita banda kowa. wannan motar ba tamu bace ta gidan da nake aiki ce, dan Allah ku taimaka min, na tabbata Kakata duka gadonmu na wurin mahaifiyarmu ta siyar aka sami wannan kuɗin, a yanzu kuwa na san babu wani abu da zata ƙara ɗagawa ta siyar, kuyi min rai dan Allah".
shirunta yay dai² da shigowar wani mutum dogo kamar sanda, ya ƙaraso gaban ƙaton mutumin yana miƙa masa waya yana cewa,"oga ka duba news ka gani".
Ogan ya shiga kallon shafin facebook da yake nuna masa yana karanta bayanan dake jiki na ɓatan Fillo ƴar aiki a gidan Judge Alƙali Dikko, da kuma hotonta a ƙasa sanye da hijab.
sai ya bushe da dariya yana sa ƙafa yayi fatali da kujerar dake kusa da shi, ya mayarwa da mutumin wayar yana faɗin,"ashe kamu muka yi me soka bamu sani ba, har muna ɓata lokacinmu wurin amsar 5million only".
sai yay shiru yana ƙara sakin dariya yace,"Hardo kaje ka nema mana numban waya na gidan Alƙali, wannan yaro yana da taurin kan jaraba ba zai bamu wani number ba...kayi sauri ka kawo min in the next few minutes, yanzu ba miliyan 10 muke nema ba, miliyan 200 zamu karɓa".
ya faɗa yana miƙewa daga kan kujerar yana ƙara sakin dariya cike da nishaɗi.
sannan ya ƙara kallon ɗaya acikin yaran nasa yace,"Jibril, ka siyo kaza ka bashi yaci, domin ina sha'awan wannan yaro, ina so na huta da shi. a siyo masa kayan gina jiki a bashi yaci kafin nazo na biya buƙatana akansa, tun a ranar farko naji ina sha'awan budurci nasa, i know by that time uban Alkalai ya kawo mana 200Million namu, sai muna sakinsa yana tafiya".
Kalmar Virginity yay wani duka a ƙwaƙalwar Fillo da yasa taji ta girgiza gaba ɗayanta, her virgin?, kamar dai bata fahimci maganar tasa ba da kyau, sai kuma taji wanda aka barta da shi na faɗin,"kash Oga banji daɗi ba kana riga ni shiga daɗin wannan kyakykyawan yarinyar, nima ina ta kwaɗayinta tuntuni, amma da zarar ka sha naka rabon daɗin nima zan sha nawa kafin a sallameta". yaja igiyar ƙafarta ya ƙara ɗaurewa da kyau yana cewa,"kai Budurci yana da daɗi, gaki da ganinki za ki daɗi ƴan mata".
ƙwayar idon Fillo tun ɗazu ƙafe take a wuri ɗaya, tun bayan fitar wancan mutumin take so ta fahimci abinda ya faɗa kafin ya fita, kuma bata gane komai ba sai a yanzu, sai yanzu ta fahimci abinda yake nufi daga shi har wannan, suna maganar zasu amshi budurcinta ne kafin ta fita daga hannunsu.
da sauri ta shiga jujjuya kanta da ke barazanar tarwatsewa, hawaye masu zafin gaske na daɗa biyo kuncinta, ta jinginar da kanta jikin bango tana jin ƙirjinta yay mata wani irin nauyi tamkar an ɗora dala da goron dutse akai, a hankali ta shiga ambaton sunan Allah tana fashewa da wani kuka me ƙarfin sauti cikin fitar hayyaci.
ta jima tana kukan tana kiran sunan Allah, bata ma san time ɗin da mutumin da aka barta da ahi ba ya fita ba. zuwa yanzu ta san ruwan hawayenta sun ƙare, ƙazaman maganganun mutanen ke tayi mata yawo acikin kanta.
ta sa ni shikenan tata kuma ta ƙare, dan haka ta sallama da rayuwar gaba ɗaya, kanta ta buga ajikin bango tana addu'ar,"Allah ka ɗauki raina kafin waɗannan azzaluman su cimma burinsu akaina, Allah ka ɗau raina ayanzu ko na huta da wannan bala'in".
tsananin tausayin kanta ya lulluɓeta, babu ta yanda ta-ke tsammanin zata iya guduwa daga wajen nan, dan tayi attempting sau ɗaya suka kamata, shine tun daga ranar suka ɗaureta basu ƙara ƙunceta ba har zuwa yau, jini har ya gaji da daskarewa waje ɗaya a jikinta.
idanuwanta a rufe taji kamar mutum na taɓata, a mutuƙar firgice ta buɗe ido tana sakin ihu cikin ƙaraji da bala'in tsoro, da sauri farin mutumin dake gabanta yasa hannunsa ya toshe bakinta.
ta ƙwalolo ido waje tana kallonsa, ta san shi sosai kullum shine yake kawo mata abinci. a hankali taji yace,"ki shiru zan taimaka miki ne ki fita daga wajen nan, ki yarda da ni wallahi ba zan cuceki ba saboda haka karki yi ihu"
ya sauke hannunsa a bakinta, cike da tsoro dan bata tunanin za ta yarda da shi. ya miƙa mata plate na abinci gabanta yace,"ki fara cin abincin tukunna".
tace,"dan Allah karka yi min komai".
yace,"wallahi tallahi banda niyyar cutar fa ce taimakonki, amma kici abincin ko kaɗanne kinji".
tana ta kallonsa tace,"ba zan iya ci ba. dan Allah ka taimaka min".
yace,"zan taimaka miki amma in har ba kiyi wani yunƙuri na tona min asiri ba".
da sauri ta jijjaga kanta tana cewa,"zan bi duk ubarninka in har ba wanda zaka cuceni ba".
yasa hannu ya kunce ɗaurin igiyar ƙafarta, sannan ya kunce ɗaurin na hannu, amma sai dai bai warware ba.
yace,"k