i durƙushen kanta kamar ba na lafiya ba tukunna ya ƙarasa ciki ya zauna kan kujerar dake kusa da ita.
yasa hannu ya ɗago kanta looking at her innocent face da yay ja, with the other hand ya taɓa forehead nata yaji zafi rau. ya rufe idonsa kaɗan ya buɗe yana ganin yacca hawaye ke suntiri akan kumatunta, kallon hawayen yake yana hango lokacin da yake zaune a gaban Hayyo yana faɗa masa cewar,"ehh kamar uba nake a wurinta amma ni ba mahaifinta ba ne, wannan yarinyar da kake gani ai ƴar zina ce, ƙwarai ƴar gaba da fatiha ce ranka ya daɗe, mahaifiyarta ma mahaukaciya ce, garin haukar nata ta gudu shekaru da yawa har yanzu bamu ganta ba, kuma har yanzu ni ban saketa ba. amma dai saboda a rufawa yarinyar asiri indai da gaske kake sonta ranka ya daɗe kawai ka biya sadakinta yanzu a take, batun sauran kayan al'ada da ake yi duk ba sai kayi mata ba, tunda dama ba faɗar addini bace, sadakin dai nata kawai ka kawo itama idan an bata babu hankalin riƙe su, tunda dama ni ne maɗaurin aurenta, babu wanda ya san danginsu tunda a titi na tsinci uwar naji tausayinta na aureta. ita kuma tsohuwar da kake cewa Yarinyar na hannunta gaskiya to ban ma san wace ba, ƙila ma ko irin tsaffin nan ne macuta".
ya ƙara hasko lokacin da yasa hannu a aljihunsa dan ɗauko kuɗi, amma sai yaji babu komai. sai ya ƙara kallon Hayyo wanda ya gano tsananin kama ta Fillo a tare da shi, ya sauke numfashi yana me jin wani iri a ransa, zuciyarsa na ƙara ƙarfafa masa miƙa sadakin Fillo, ko da bai aureta saboda taimakon da tayi masa, tabbas ta cancanci a aureta saboda rashin dace na uba da tayi, dan ko kaffara ba zai yi ba Hayyo shine mahaifin Fillo.
to amma da me zai bayar da sadakin nata?, yay shiru yana tunani cikin ransa, ko kaɗan baya so ya miƙe daga kan tabarmar nan ba tare da ya mallaki yarinyar da ta dinƙa cusa kanta a haɗari ba saboda kawai ta cece shi, ba don komai ba sai dan ba zata iya ganin an cutar da wani ba.
yana iya tuna yacca ya dinga jin kallon da Hayyo keyi masa, yana tuna furucin da Hayyo yayi masa kan cewar,"ranka ya daɗe in har babu sadakin yarinyar nan kazo ayau, to ina mai tabbatar maka da cewar ba rabonka ba ce, domin kuwa tun tana ƙarama akwai wani tsoho da ya roƙi a bashi ita, to banda ma dai tasa ƙafa ta gudu da maganar da nake shaida maka yanzu tayi ƴaƴa kusan uku. dan haka kana tafiya zan yi masa magana ya bada sadakinta, in yaso tunda Allah yasa kai kasan inda take, sai kayi mana jagora muje mu taho da ita".
"zan bayar da sadaki, amma sai naga shedu". haka yasan ya faɗa masa, kuma minti goma ba'a ƙara ba sai ga Hayyo ya dawo tare da mutum huɗu, ya shaida mutum ɗaya wanda Hayyo ya nuna masa yace shine limamin babban masallacin anguwarsu, saboda lokacin da ya shigo unguwar ya tsaya yayi sallah a masallaci, dalilin da yasa ya gane shi kenan, sai mutum ukun da bai sansu ba, amma daga tsufansu ya san ba mutanen banza bane.
yana tuna sanda Liman ya buɗe baki ya tambayesa ina waliyansa, kuma a lokacin magana ɗaya ya faɗa wadda daga ita ba wanda ya ƙara cewa komai Liman yace ya miƙo sadakin. "ni maraya ne, bani da kowa sai Allah".
hakan ya faɗa musu, kuma daga faɗar hakan babu wanda ya ƙara masa wata tambaya aka ce ya ajiye sadaki. still idonsa na kan Hayyo yace,"banda kuɗi yanzu". kuma tun bai rufe bakinsa ba Hayyo yace,"kana iya tashi ka tafi, yarinya dai ba rabonka ba ce".
zuciyarsa ta faɗa masa cewar in har Fillo zata iya sadaukar da ranta da kuma lafiyarta akan ta kuɓutar da shi daga wani ƙulli, alhalin ba dangi iya bare na Baba, to baya jin shi zai kasa iya sadaukar da komai nasa don ganin ya mallaketa, mallakarta kaɗai shine sakayya mafi kyautatawa da zai yi mata. saboda haka take a wurin a ajiye key ɗin motarsa a gaban Liman yace,"na bayar da motata a matsayin sadakinta".
ba zai taɓa mance yanda Hayyo ya dinƙa kallon maƙullin motar ba with so much expression, har ƙwayar idonsa irin ta Fillo na yin kamar zata faɗo waje. amma duk da haka sai da yasa aka shiga cikin gida aka kira masa wani saurayi, saurayin shima me kama da Fillo sak, idan bai manta ba sunan da Hayyo ya kira saurayin da shi shine,"Hamid". saurayin ya amsa masa da,"na'am Abba". sannan Hayyo ya ɗago kai ya kallesa yace ya zagaya baya, ya gano masa motar dake wajen kuɗinta zai kai nawa.
and abinda Hamid ya dawo ya sanarwa da Hayyo shine,"kuɗinta zai kai miliyan hamsin ko sama da haka". kuma ba tare da ƙara yin wani bincike ba Hayyo ya kalli ƙwayar idon Turaki yace masa,"kaje yarinya ta zama mallakinka, aure ya ɗauru".
haka ya baro garin Taraba a train zuciyarsa cike da tarikan mamaki iri-iri a game da lamarin Fillo da mahafinta, duk da cewar yaso ya keɓe da Hamid to amma bai samu dama ba.
Fillo ta buɗe idonta dake yi mata zafi tana kallonsa, idonsa a rufe yake, har sannan kuma bai saki kan nata ba.
in cool voice nata tace da shi,"please ka daina taɓani any how babu kyau. kuma dan Allah ko kuɗin napep ne ka bani na koma gida, Maama da Boɗejo zasu neme ni, turarenka ku