jin daɗin aibanta min Yaya da kike ko kaɗan, bana so kike faɗan mummunar kalma akansa, ki daina walaƙanta min shi a wajen mutane, idan kene na yiwa Yayanki haka zaki ji daɗi ne?". nayi maganar raina a matuƙar ɓace, sai tayi saurin dafe ƙirji tana faɗin, "ni ko ina na isa na yiwa Yaya Abba haka, rufa ni ki saya". ta faɗa tana nuna kamar bata gane inda maganata ta dosa ba. na jijjiga kai nace, "nasan kin san akan wanda nake magana, amma saboda kina so ki mayar dani ƙaramar ƴar iska shine zaki nuna wani waskewa ko". nai maganar dai-dai lokacin da muka ƙaraso inda motarta ke ajiye, kuma kamin ta buɗi baki tace wani abu sai kawai gani tai na wuce gaba abina, ina jinta tana jera min kira nai mata shiru ban tsaya sauraronta ba, dan banda lokacinta. sai gata ta tsaya da motar a gabana tare da zuge glass ta min magana. "Sabina wai mene kike yi haka don Allah, ya wani banza can zai ƙoƙarin rusa abotar mu tun ta yarinta...". Maganarta ta katse a lokacin dana juya ina cewa da ita cikin masifa,"Malama shi ba banza ba ne, ki fito kai tsaye ni ki kirani da banza tunda ni na shiga rayuwarsa. Kuma karki damu da tafiyata a cikin motarki domin nima ina da ƙafa, dama ban saba da ita ba saboda ban ganta a gidanmu ba. Kije kawai abinki". Daga haka na wuce nayi tafiyata, raina duk a dagule na shiga gida, saboda na gama tsara bayan an tashi makaranta zanje wurin Yaya domin ganin lafiyarsa, tun wancan ranar da yay min gargaɗin kar na ƙara zuwa ban koma ba yau gashi kwana takwas kenan, sai dai hankalina da tunanina duka na kansa, ga yau ɗin dana ƙwallafa rai da zuwa lokaci yay halinsa dan magriba tayi, ga itama Farhana ta ƙara ɓata mani rai, shi yasa duk kaina ya cunkushe. ina ɗaga labule nayi sallama cikin parlo, lokacin Gwaggo na zaman tahiyar ƙarshe na sallar magriba da ake, bayan ta idar da adu'ointa ta juyo tana kallona da yanda nake ta faman ɗacin rai. ta gefen ido na kalla Gwaggo na girgiza kai alamu na Allah ya kyauta kana tace min, "saboda kina fushi ba za ki yi sallar ba kenan ko mene uwar ƴan nurƙufanci". "ina hutu ne". na bata amsa a taƙaice. "to tashi ki ɗauko mana tourchlight a ɗaki, ga battery can kan abun tv ki saka na ciki yayi sanyi". na miƙe naje na ɗauko na kunna haske, sannan na koma kan kujera na zauna, ko uniform ban iya cirewa ba kuma banda niyyar zan cire, sai faman kumbure-kumbure kawai nake. Gwaggo dake ankare dani tai min banza bata bi ta kaina ba, Taci gaba da harkar abinda ke gabanta, can data gaji da ƙwafar da nake jerawa babu ƙaƙƙautawa ta juyo ta wurgo min harara da cewar,"ke wai ƙalau ki ke kuwa, kinzo kin sani gaba kina ta aikin ƙwafa, ko sallama ma fa ina jinki a ciki kika yi ta. Sabina bafa zan ɗauki wannan sabon halin naki ba, ke da waye a makarantar?". ina aikin tsuke baki nace, "ba Farhana ba ce". Gwaggo tayi tsaki tace, "Allah ya gyara ki idan kina da rabon gyaruwa, tun kuna cin ƙasa rabonku da yin faɗa ke da ita amma saboda mahaukacin yaron nan kina son zama fitinanniya ko Sabina. To wallah tun wuri ki shiga hankalinki, ki fita a sabgarsa tunda kinji dai yanda yake, amma zan gyara miki zama ne karki dawo kan layi ki gani". sai kawai na hau bori ina dukan ƙafa a ƙasa kamar zan fashe da kuka. "na rantse da Allah Gwaggo shi ba mahaukaci ba ne kuma ba ɗan iska bane, wallahi da gaske nake miki da kin kalle shi kinga mutumin kirki, sam bai ma yi kama da ƴan daba ba, kawai tsintar kansa a cikin ƙangi na rayuwa yasa ya jefa kansa cikin wannan yanayi, shine ita kuma Farhana saboda rashin sanin daraja ta ɗan Adam ta ke cewa mahaukaci ne. Amma wallah ba shi ba ne, kallo ɗaya zaki yiwa yanayinsa ki gane, kuma ma ai yace min ba zai kuma shan taba ba". baki buɗe tace, "au ya tabbata lahu dai ɗan daba ne kenan, to ai gwara da kika faɗa da kanki na ji. To bari kiji ko ki fita harkarsa ki manta da shi ko kuma na haɗaki da ubanki, tunda ni yanzu ban isa na faɗa kiji ba, zamanin na faɗa miki kiji ya jima da shuɗewa tun ba ki balaga ba". na sakko daga kan kujerar na dawo kusa da Gwaggo na zauna, na kamo hannunta ina cewa,"kiyi haƙuri Gwaggo nah, ba wai bana jin maganarki ba ne. Allah Gwaggo kika kalla bawan Allah'n nan sai kin tausaya masa, har kuka sai kin yi mishi wallahi, kuma ke da kanki za kiji kina son taimaka mishi". "mtswwww". Gwaggo taja tsaki tana watsa min harara tare da ƙwace hannunta. "tashi ki ɓace min anan wurin ko ranki ya ɓaci...insha'Allahu zan kaiki masallaci ai miki sauka". saina miƙe ina faman yarfar da hannu na wuce ɗaki, na kwanta kan katifa nai shiru ina mai jin raina duk babu daɗi, ni kaina na rasa dalilin damuwa da mutumin da ban san wane shi ba, haka kawai nake jin tsananin tausayinsa da son taimaka mishi, har sanda bacci ya fara ɗaukana, sai dai wani abu na ban mamaki dana rufe ido saina dinga ganin hoton fuskarsa na bayyanar min.
Washegari ya kasance Asabar, ƙarfe 9 na shirya domin tafiya Tahfeez, ina yiwa Gwaggo Sallama sai ga sallamar Farhana, ɗauke kai nayi daga kallonta a lokacin data ke shigowa, itama bata kula