NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 96 of 97

wai buƙatuwar ki koma gida". "Bhai zan koma ne kawai idan naga farkawar ƴar mutane, sannan naga fitowar Muntaƙa daga station domin ƴan sanda sun riƙe shi sun ce yana tuƙi ba bisa ƙa'ida ba". SJ ya kalla agogon damtsen hannunsa kana a hankali ya furta,"zata farka Maamee, zata farka ko don saboda samun natsuwar Mahaifiyata". Ya faɗa yana tsayuwa gefen da Ya Imam ya jingina da jikin bango tare zuba hannayensa cikin aljihun wando gami da fuskantar ƙofar ɗakin da Sa'ida ke kwace rai hannun Allah, kuma fuskantarsa ƙofar ɗakin yay daidai da farkawar Sa'ida wacca ta ƙwallara wata muguwar ƙara da ta amsakuwa a cikin asibitin gaba ɗaya kafin furucin Abbaana ya biyo baya a bakinta. Ai fa kamin ƙiftawar ido cikin sauri kowa ya miƙe anyi cuncurundo a ƙofar ɗakin ana leƙenta ta farin gilashin jikin ƙofar, tana daga kwance tana faman jujjuya kai tana kiran sunan Abbaa. Dr ya ƙaraso wajen cikin hanzari shi da nurses suna a ba su hanya, sai dai sam babu ma wanda ya san suna yi. A hankali SJ ya sauke numfashi yana barin wajen da yake tsaye wanda shi ɗaya ne dama bai bar inda yake ba, ya ƙaraso kusa da Dr ya karɓi stethoscope ɗin hannunsa, sannu a hankali ya ratsa ta tsakanin mutanen da ke ta faɗin Alhamdulillahi yana jin kansa kamar zai bindiga saboda hayaniyarsu har ya kai bakin ƙofar yasa hannu ya buɗe room ɗin, Dr da Nurses su ka zo suka shiga ciki kana shima ya shiga ya rufo ƙofar. Ba zuciyar Dr da Nurses kaɗai ba, hatta zuciyar SJ sai da tayi mugu mugun matsewa da tausayin critical condition ɗin da yaga Sa'ida, a hankali lumsassun idanuwansa ke kallon Finger pulse oximeter da aka sanya mata kafin ya sauke ƙarshen kallonsa kan Cervical Neck Collar da ya rufe har haɓar fuskarta. Ba ya jin a irin tausayin da yake da shi zai iya tsayawa kallon yanda likitoci ke gudanar da aikinsu akanta da kuma hawayen da yaga suna fitowa daga rufaffun idanuwanta suna sauka ta gefe. Takawar da zai yi ya juya ya fita yaji likita ya ɗaga murya wajen cewa da Nurses,"ku taimaka ku riƙe min ita". Kuma kafin wani yunƙuri na Nurses SJ ya riga su isa gaban gadon yayma Sa'ida rumfa tare da danne hannayenta biyu don ganin ta daina jijjigar da take yi. "Désolé(Sorry)". Ya faɗa a hankali bugun zuciyarsa na ƙaruwa. ____________________________________ *_ALHAMDULILLAH! Nan muka kawo ƙarshen littafi na ɗaya, mu gauraya da ku cikin littafi na biyu da na uku domin jin yanda labarin zai ci gaba da kayawa. Na san akwai tarin tambayoyi a cikin kanku, haka akwai hasashen da kuke a game da ƙarshen labarin da kuma Mafarin labarin, sai dai fa ku sani Alƙamin Halimahz a ko da yaushe saɓanin tunanin makaranta ne, duk da cewar a wannan karan na buɗe komai a labarin to amma still a wajena bai zama buɗaɗɗe a gareku ba. Ina da tabbaci gami da yaƙini akan littafin nan, babu danasanin siya balle nadamar karantawa, saboda haka na ke cewa kar da ku sake a barku da cizon yatsan rashin karantawa. Da ₦500 za ku mallaki littafi na biyu da na uku wanda zai fara zuwa nan ba da jimawa ba, a shirye na ke tsab wajen faranta zuƙatanku....Mun dai san SO tamkar rayuwa ne, sai dai fa ba ko yaushe ya ke zamowa abu mai sauƙi ba haka kuma ba a ko da yaushe yake wanzar da farin ciki ba, to amma menene ke yanke alaƙar soyayya cikin wata alaƙar soyayyar? Rabuwa ko yanke alaƙa na sanya rauni a jikin rayuwar wata halittar! Idan har akwai ƙaddara to akwai adu'a da ke canjata, kazalika idan akwai jinkiri to la shakka da alkhairi, tsananin haƙuri matakin nasarar cinye jarabawa...Takaicin ba kaɗan ba ne, Sadaukarwar me faɗi ce, haka ma butulcin ba kamar yanda sakayyar ke zamowa ba ne, yayin da aka ce akwai soyayya me tsuma zuciya ta sami mafaka a ruhi ɗaya cikin gangar jiki biyu ya tunaninku zai ba ku? Haƙuri ba ya yawa! Ƙunci ba ya dawwama in har da adu'a!...hallau dai ina ƙara nanata muku cigaban rayuwar auren gidan Nazifi da wakanar komai a ƙarshe zai zama saɓanin tunaninku ne tabbas sai dai akwai alƙawarin Happy Ending🥰.Kafin mu luntsuma cikin littafi na biyu zan so mu haɗe a comment section da ku domin bararraje abin da ke ranmu akan littafin ƘAYAR RUWA🔥...ku tura ₦500 via 6314170140,Fidelity Bank,Sa'adiyya Zakariyya Haruna...shaidar biya kai tsaye ta👉🏻07018098175....ƳAN NIGER KU TURA DA KUƊINKU TA Mkoudi 89356025 airtel, SANNAN KU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBA 08162576936...Sai mun haɗu da ku a paid group ƴan Amanar Nazifi😅Allah ya horewa kowa kuɗin siya...Show me love masoyana abin sona😍ku girgiza akawunt ɗina da kuɗin littafin ƘAYAR RUWA na san ba zaku bani kunya ba😘...masu son magana da ni chartup via whatsapp 07018098175._* Siyan Na gari mai da kuɗi gida💃🏼tarin godiya ga waɗanda su ka zaɓi fitattu biyar😍son so. _________________________________ ```Ya hayyu
🏠