, Daadee ya zame Maamee daga jikinsa yana yiwa mahaifiyarsa barka da isowa. Marfu'a kuma ta wuce da Æaton basket na abinci taje suka gaisa da su Ummani kana ta dawo ta zauna kan kujerar da Samra ta tashi tana karÉar yaronta a hanun Nani.
"Saukar yaushe?".
Madam ta ce da Dadee suna tafe zuwa wurin su Ummani ita da shi.
"Yanzun haka, don ina shigowa kuna zuwa".
Daadee ya ce da ita daidai da Æarasowar tasu wajen dangin Sa'ida waÉanda suka kame kansu a gefe guda suna jiran tsammanin rai ko mutuwa na Æ´arsu. Madam ta miÆa hannu ga Ummani tana cewa,"Bayin Allah sannunku, ya muka ji da wannan tashin hankali?".
Daadee shima ya miÆa hannu ga Abbaa da Kaka suka gaisa. Kafin nan ya shiga basu haÆurin hatsarin da ya afku yana kwantar musu da hankali akan da yardar Allah Æ´arsu zata sami lafiya. Suka amsa da amin tare da godiya bisa karamcin tsayawa da aka yi akan Æ´ar tasu wannan kaÉai ma basu da bakin godiya sai dai su ce Allah saka da alkhairi, hatsari kuma ai afkuwa yake ba da gangan ba saboda haka babu buÆatar ake basu haÆuri ai an masu mutunci ma da aka Éauke musu Éawainiyar asibitin. Daadee ya kai Æwayar idonsa ga hanyar shigowa wanda yay daidai da shigowar SJ kuma take annurin fuskar Daadee ya Éauke, yay saurin Éauke idonsa daga wajensa yana kawarwa gefe fuskarsa na nuna Éacin rai, shima Éangaren SJ ganin mahaifin nasa a wajen yasa shi dakatawa da tafiyarsa ya tsaya daga can nesa, haka kuma yanayinsa na sauyawa zuwa wani yanayi me wuyar fassaruwa, tabbas in ace ya san mahaifin nasa ya dawo to bai ga abin da zai kawo shi wajen nan ba, kamar yanda a Éangaren mahaifinsa shima cikin zuciyarsa ke faÉin in da ya san SJ zai zo asibitin da babu abin da zai kawo shi a lokacin da zai zo.
Ahlan yaywa Maamee nuni da SJ, ta kai kallonta wurin suka haÉa ido da shi yana tsaye hannayensa sarÆe a Æirji sai kallonta ya ke babu Æiftawa, fuskarsa na nuni da rashin jin daÉin ganin Daadee da yay a wajen. Ta tashi ta Æarasa gare shi don ta san ba zai Æaraso ba kam, tayi mamakinsa ma da bai koma ba kamar yanda tayi mamakin Daadee shima bai fice a fusace ba, ita a duniyarta kam bata da wata damuwa bacin ta SJ da Daadee da basa jituwa ko na misÆala zarra kamar ba Uba da Æa ba.
Da isarta wajensa ya kama hannunta ya riÆe a nasa, tana kallonsa ta ce,"Me yasa ka baro aikinka?". Ta faÉa cikin harshen faransanci.
Yay shiru na Æ´an sakanni kana shima cikin harshen na su ya ce da ita,"Maamee karon farko da naji sautin kukanki, kinga har yau zuciyata motsawa take da zafin kukan da naji kina yi".
Yay shiru yana rufe idanuwansa yana shafa hannun mahaifiyarsa da ke cikin nasa, bayan numfasawar minti guda ya ce,"Yarinyar fa?".
Kasa ba shi amsa tayi, ya buÉe ido tare da sanya hannu ya Éago fuskarta ya ce,"Da ace kuÉi na siyan lafiya da ba'a kawo wannan lokacin ba, sai dai lafiya na wurin ubangiji bamu da yanda zamu yi, shi likita nasa taimakawa ne kawai. Don Allah Maamee ki yi haÆuri ki kwantar da hankalinki zata sami lafiya fa, Yanzu haka da na shigo sai da na fara zuwa wurin Dr yay min bayani kuma ya bani tabbacin zata farka lafiya lau wasu mintuna kawai ake jira, na dai jaddada masa suyi iyakacin iyawarsu wajen ganin Yarinyar tayi surviving and ba tare da zaman wani mummunan rauni a tare da ita ba".
Ya Æarasa maganar yana sauke numfarfashi tamkar wanda yay tsaren gudu tsabagen doguwar magana nayi masa wahala.
"Amma Bhai kana gani sama da 24hrs fa bata farka ba, kar ya zama na yi sanadin rai".
"Maameeeee".
Jin yanda ya ja sunan nata yasa tace,"To nayi shiru Allah ya tashi kafaÉunta".
Hannunsa bisa fuskarta ya ce,"Marci".
"Ga mahaifanta can da Æ´an uwanta muje ku gaisa ka tayani ba su haÆuri".
"Ok let's go". Yana riÆe da hannun mahaifiyar tasa suka nufa wurin. da zuwansu SJ ya duÆa har Æasa ya gaida su da girmamawa tare da tambayar,"Ya mai jikin?". Sautin muryarsa ya fito da rashin Æwarewar hausa a bakinsa.
Abbaa ya dinÆa kallonsa lokaci Éaya sai yaji ya shiga ransa, saurayi mai kamala da natsuwa gami da girman kwarjini. Ya ce da shi,"To sauÆi yana wurin lillahi, tana can kwance dai har yanzu bata farka ba amma likitan ya ce wai zata farka duk da mun barwa Allah yay ikonsa".
Kan SJ sunkuye a Æasa, cikin tausashshiyar murya ta son kwantarwa da mutun hankali ya ce,"Zata farka kuma cikin sauÆi in sha Allahu, likitoci za su yi iyakar bakin ÆoÆarinsu akan lafiyarta babu wani damuwa ku kwantar da hankalinku".
"To mun gode Allah ya saka da alkhairi".
Ummani ta faÉa tana kallonsa. Ya miÆe yana yi musu sallama. Ummani ta kasa Éauke idonta daga kansa, kallonsa kawai take yi tana so ta tattara yanayin da take ji akansa ta Éora a ma'aunin lissafinta kana ta fassara shi, zuciyarta ta harba Éaya, biyu, uku, tare da kalmar GARKUWA. Duk da halin jimamin da ake ciki hakan bai hana ahalin Sa'ida furta yabo da burgewa ba akan SJ da ahalinsa.
"Ak