anyan botikan da ake wanke kalwar yin daddawa, shima babu haske sai na farin wata da ya ratso ta Æatuwar Éular langa langar soron, duk da cewar dare ne a lokacin kuma babu hasken fitila amma kana iya ganin Æ´an tsirarrun Æudaje sun yi yaÉo a saman bokitan kalwar.
Daga cikin gidan kuwa tsakar gidan yay Æal, ko'ina fes fes, duk kuwa da rabi da kwatan simin Æasa ya farfashe. kai da ganin yanda komai yake a killace a tsabtace kasan ba gidan Æazamai ba ne duk da cewar gidan talakawa ne sosai, ba zaka taÉa cewa gida ne da ya tara iyali da yawa ba saboda tsananin tsabtarsa, kuma da zarar ka zuÆi kyakykyawar iska zaka zuÆo Æamshin turare Éan tsinke sama-sama.
"Kambun-baka gaskiya ne domin yana faruwa kuma yana iya kai mutum ga mahallaka (mutuwa) saboda tsabar tasirinsa a jikin mutum, saboda haka ya zama wajibi mu nemi kariyar ALLAH Shi kaÉai, sai riÆo da hanyoyin samun waraka ko riga-kafi wadanda suka inganta a shari'ar Allah wajan kare kanmu da iyalanmu daga sharrin Kambun-baka da hassada. Kambun-baka ko Kambun-Ido, Nassi ya yi bayaninsa kamar yadda itama Hassada akayi bayaninta, kuma duk an bayyana mana irin illar da Kambun-baka yake yi ga lafiyar mutane domin yana iya hallakar da mutum ko kaga mutum yayita fama da rashin lafiya mai tsanani. Addini ya koyar da mu hanyoyin da za mu nemi ALLAH ya kare mu daga sharrin dukkanninsu da ma masu yin su gaba Éaya, mu nemarwa kanmu, iyalanmu, dukiyarmu da duk wata ni'imar da mu kasan muna da ita kariya da tsarin ALLAH Ubangijin kowa da komai kuma mai iko akan kowa. yana da kyau muyi Riga-kafi akan kambun baka, wato (neman kariyar Allah kafin abin ya faru da mutum har yayi tasiri akansa), da kuma yin maganin da bai saÉawa Shari'ar Allah ba idan abin ya faru har yayi tasiri akan mutum. saboda haka mu yawaita karanta Ayatul Kursiyyu da Surorin Falaqi da Nasi musmaman a lokacin da za mu kwanta bacci saboda neman Allah ya kare mu daga sharrin Kambun-baka da na hassada, saboda tasirin sharrinsu a jikkunan mutane ya zarce wanda shafar jinnu ke haddasarwa, ga naci da Æalata wajen son dauwama a jikin mutum da sanya cututtuka iri-iri, ubangiji ya kare mu da kariyarsa".
Maganar da ke fitowa kenan daga cikin Éaya daga Æananun Éakuna biyar Éin gidan, Kowa a cikin Éakin zaune yake bisa Æatuwar tabarmar da ke malale a tsakar Éakin, kamar dai yanda suka saba kullum a gidan duk bayan sallar isha'i, sun kasa kunnuwa cikin natsuwa suna sauraron karatun da mahaifin su Malam ke musu.
Ummaa kishingiÉe a kusa da Malam, sai Iyam kwance gefen Malam Éangaren damansa Gwaggoje mahaifiyarta na yi mata firfita, Amarya daga bakin Æofa riÆe da tourchlight mara haske dalilin sanyin batir, sai yaran su a kusa da juna rabin hankalin su akan Malam sauran rabin akan Iyam da bata da lafiya tana fama da ciwon Æafa da ko takawa bata yi, yayin da duk wani rai zuciyarsa kema Iyam adu'ar samun lafiya domin kusan ita ce garkuwar iyalan Malam Bala Mai Kalwa.
Jummai(Iyam) ita ce matar Malam ta farko wadda aka yi aure tun Æuruciya, tana da bala'in kishin mijinta ga fafutukar sana'a don kusan ita ce jigon kasuwancin kalwar da Malam ke yi a Æauyuka da birni, ita ce take dafawa tayi aikinta tas shi kuma ya fita da ita kasuwa a siyar. ƳaÆ´anta goma banda waÉanda su ka rasu, Hashimu(Yaya Babba) Maijidda(Yaya), Najibu, Aisha(Anti), Rabilu(Yayan Shago), Nazifi(Yaya Æarami), Adamu, Lubabatu, Basira, sai auta Fati.
Asiya(Ummaa) ita ce ta biyu yaranta bakwai; Basiru, Sadiya, Zubaida, Habiba, Musa, Jabiru sai Garzali.
Fauziyya(Amarya) ita ce ta uku yaranta biyar; Radiya, Musbahu, Naziru, Sumayya, Sharifa.
"Salamu Alaikum". sallamar da akayi daga tsakar gida taja hankalin su, Amarya ta Éaga labule ta leÆa bayan ta amsa sallamar.
"Nazifi". ta kira yi sunan nasa idonta a kansa.
"Na'am, ya naji ku a Éaki kuma".
"ummm yau bamu zauna a tsakar gidan ba saboda sauro".
"kuma kinga na sha'afa ban taho da magani ba". yay maganar a sa'ilin da yake Éiban ruwa a buta yana kaÉe sumar kansa da Æasan wandonsa.
Ta sake cewa,"Ka kira wani a cikin su ya taho da shi, a haÉo da battery wannan yayi sanyi neman mutuwa ma yake gaba Éaya".
"Ai na ma siyo sabuwar tocilayit Éazu ta caji, na barta ne a gidan su Muntari anjima zan karÉo".
"Ciniki aka yi ne naji fa ana ta cajin da tsada".
"Wallahi yau kasuwar rake kam Alhamdulillah anyi ciniki dan duka wanda na fita da shi sai da ya Æare, shine ina tahowa naga fitar na siya dubu Éaya amma Æ´ar Æarama ce".
"To masha'Allah, Allah Æaro kasuwa me albarka, an gode".
Ya amsa da amin sannan ya bankaÉa labulen Éakin ya shiga, ya nemi gefe Éaya ya zauna yana gaishe da mahaifinsa tare da Gwaggoje da Ummaa, sannan yabi mahaifiyarsa da ido itama yana yi mata sannu da jiki, duk sai sanya masa albarka suke yi shi kuma yana amsawa cike da jin daÉi da farin cikin alfaharin da ahalinsa suke da shi. Kamar ba shine na Éazu d