NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 9 of 97

da shi amma duk da haka sautin kukana bai ɓuya ba. Lokaci ɗaya jikina ya ɗauki zafi na kama kyarma dama ni ban iya zazzaɓi ba. A wannan lokacin duk wani mai imani ya ganni sai zuciyarsa ta motsa da tausayina. Haka na ke ta faman zubar da hawaye, ban isa na goge su ba don ina gogewa wasu na sakkowa. Na daɗe ina kuka don har wajen sha ɗaya da rabi, zuwa wannan lokacin kam na fidda ran dawowar Hubbi, banga alamun yau zai kwana a gidan ba. saboda haka na miƙe na shiga banɗaki na wanko fuskata ina hana kaina ci gaba da kukan da baida amfani gare ni, adu'a maganin annoba ita ya kamata in riƙe ba wai damuwa da kuka ba. Ina fitowa na wuce nasa key na kulle ƙofa duk da zuciyata na faɗa min komin dare zai dawo, bai da wani wajen kwana a daren nan sama da nan ɗin dai da yake ƙauracewa, tsakin ƙasan maƙoshi nayi, to ina ruwana da dawowarsa, raina ɓace na fita falo na bi duk ƙofofi shigowa na saka musu maƙulli, zanga ta in da zai shigo, ai sai dai yay kwanan ɗakin mai gadi, ba abar banza ba ce ni, auroni yay don yana so ba cusa masa aka yi ba, kuma a gidan iyayena ya ɗauko ni ba gidan marayu ba. kamar ma in koma ɗakina amma sai na dawo ɗakin nasa, na murza key na kashe fitila me haske na bar mara hasken wacce ke kan durowar gefen gado. Bacci nake ta so nayi amma gaba ɗaya na kasa, sai juyi da nake ta faman yi, zuciyata kuma cike da saƙe saƙe, kaina kuwa ya cika fal da tunani daban daban. Ni dai lafiya ƙalau muke da mijina, sai dai tun bayan dawowarmu nan gidan da wata bai fi biyar ba komai ya canja na daga yanda muka saba rayuwa, ni da shi kamar abokai haka muke, amma yanzu ya zamar min wani horo har tsoronsa nake yi, magana ma shakkar masa na ke, komai nayi ban iya ba, saɓanin a baya duk abin da nayi ko da bai masa ba zai yaba min kuma yace nafi kowacce mace iyawa, yanzu abu kaɗan zan yi ya zama laifi, zama da shi ban isa ba in ba haka ba ya dinƙa ƙunci kenan ni kuma bana son ƙuncinsa, hatta makarantar tahfeez ɗin da nake zuwa yanzu nema yake ya kashe zuwanta, don duk san da zan tafi sai yayi ƙorafi akai, sai yace ai tunda na iya karatun sallah na san wankan tsarki na kuma san zaman aure ya ishe ni, da nayi magana sai yace ai shi ke biyan kuɗin ba wani ba saboda haka yana da ikon ya hana zuwan. Na kau da tunanin matsalata da mijina, na koma tunanin furucin Yaya na za su sa ya ƙara aure, tabbas na sani ƙarin aurensa tozarcin da nake sha sai ya ninku, don sai na ƙwammaci ina ma ban auresa ba, Allah ɗaya ya san irin wulaƙancin da matarsa zata dinga min, balle ta san don manufar da aka aurota, zata goranta min fiye da yanda dangin miji za su min, kuma daga zarar ance ta sami ciki ta haihu shikenan tawa ta ƙare, zaman auren sai ya ishe ni, takaicin da zan sha ba daga wurinta ba kaɗai har da shi uban gayyar. ni kaina na sani Hubbi yayi ƙoƙari, ba kowanne namiji ne za'a kai wannan lokacin ace bai yi ƙorafi ba, kamar yanda Yaya ta faɗa shekara takwas ban taɓa ɓatan wata ba balle azo ga maganar ɓari, kuma ko da wasa Hubbi bai taɓa min magana ba, balle ya nuna min damuwarsa ko ƙorafi, ni ce ɗin ma na ke damuwa, don sau tari har kuka na kan yi, sai yay ta min nasiha yana ƙara faɗa min lokaci da rabo ne, idan na ɓata masa rai akan nuna masa kar a fara cewa bana haihuwa ya dinƙi faɗa kenan, yace min duk wanda ya fasa faɗar hakan ba ya ƙaunar Allah, kai duk wanda ma yay min gorin haihuwa in sanar masa hukuma ce zata raba su, watarana kuwa da nace masa muje asibiti a duba ni bai ci abincina ba. yanzu kuwa yanda muke zaman babu daɗi da shi ai nayi kaɗan in kai masa ƙarar Yaya akan cin mutuncin da tazo ta min, kuma ko da ace shima wannan ne dalilin samun matsalarmu ba zanga laifinsa ba, a yanzu kam yana da buƙatar magajinsa, wanda zai ɗora akan kasuwancinsa ya kuma mallakawa kadarorinsa. sai dai fa ya tuna ana barin halak don kunya, ko mai zai yi min banda wulaƙanci, don ni na sha gaban ya wulaƙanta ni a rayuwa, domin na masa abin da ko ƴan uwansa basu masa ba, ya kuma san hakan, sai dai in ya butulce, kuma shi butulci dama ai ba sabon abu ba ne a wajen ɗan adam musamman wanda ka yiwa rana. Haka dai a wannan dare nayi ta tunane tunane, in raya wancan in saƙa wancan, in lissafa wancan, sai dai na kasa warware komai, haka duk na ƙosa gari ya waye, ni ba sallah ba balle in yi nafilfili, a haka dai har ɓarawon bacci ya ɗauke ni a lokacin da ban san ko ƙarfe nawa ba. Washegari ban farka ba sai wajen ƙarfe tara da rabi na safe dalilin bacci da wuri da ban samu nayi ba, sai dai Alhamdulillahi isassan baccin da na samu yau ɗin da ya kaini har wannan lokacin sai ya zamana ban tashi da ciwon kai da zazzaɓi kamar yanda na saba tashi da su ba a ƴan kwanakin nan. Sai da na gyara ɗakinsa tukunna na fita na wuce ɗakina, kafin na haura saman kuma sai da na tsaya na buɗe ƙofa saboda zuwan mai yi min wa
🏠