inta na matuÆar Éaukar ido.
Waya ce kare a kunnenta Æirar Iphone 6plus a lokacin ita ake ganiyar tashe, hankalinta ya tattara gaba Éaya ga maganar da ake yi ta cikin wayar, da dukkan alama waya ce take yi da mutum me muhimmanci a rayuwarta, saboda yanayin tsantsar farin cikin da ya nuna a tare da ita, tun fara wayar bata furta komai ba, sauraren shi kawai take yi cike da annashuwa, a karo na barkatai fuskarta ta Æara washewa da sanyayyan murmushi me faÉin gaske, take kuwa haÆoran makka guda huÉu dake a bakinta sama da Æasa suka bayyana, inda asalin kyawun fuskarta ya Æara fitowa.
"Tom shikenan, amma ka sani ina kewarka sosai ya kamata kaji tausayina ka dawo haka".
Shiru ya gimla na Æ´an sakanni tana ci gaba da sauraron maganar cikin wayar kafin ta sake cewa,"ni dai ba na son wayo".
Siririyar dariya ta maye gurbin murmushin da take yi sannan ta Æara cewa,"To ya zanyi da kai, yanda kaso haka zan so, fatana shi ne ka dinÆa kulawa kaji ko, a tsare mutunci ka kuma ji tsoron Allah a duk inda kake".
Ta numfasa tana lumshe idanuwanta tare da cewa,"Allah yay maka albarka, Allah ya kiyaye min kai. Ka kira Madam ku gaisa tana ta min sababi baka ganinta da gashin ido".
"Oak to bye bye, i love you so much my son".
Wayar ta yanke sa'ilin da take sauke gwauron numfashi tare da kwantar da kanta jikin kujera still idanunta a rufe, yanayinta kuma na canjawa, kamar dai tana Éauke da wata Éoyayyar damuwa da ke maÆale can Æasan zuciyarta, yayinda a gefe Éaya ta Éan takure hannunta cikin mayafi kamar me jin sanyi. Kuma kamar a mafarki Mrs Abubakar Jadda taji tayar motar su ta bada sautin Æara Æuuuuuuu, Æarar da ta shiga har can cikin dodon kunnenta, lumsassun idanuwanta suka buÉe a sanda Driver ke furta kalmar Innalillahi wa'inna ilihi raji'un.
"Me ya faru MuntaÆa?". tayi tambayar a ruÉe idanuwanta na firfitowa waje, tashin hankali na farat Éaya na bijiro mata.
"Ranki ya daÉe mutum na buge...".
Bai Æarasa maganar ba Mrs Jadda ta Æwalla Æara sakamakon tozalin da idanuwanta suka yi akan uban jinin da ya wanke rabin gilashin motar, bata san lokacin da ta fiddo da hannuwanta da ke Éoye cikin mayafinta ba ta Éora su aka tana biyo kalmar innalillahi wa'inna ilaihi raji'un. Tun driver bai Æarasa bayaninsa ba ta buÉe murfin motar ta fita a sukwane, lokacin jama'a har sunyi cincirundo a wurin, cike da tsantsar tashin hankali ta raÉa ta tsakaninsu, ganin yarinya kwance cikin jini yasa ta Éora hannu aka tana salati tare da zube gwiyoyinta a Æasa.
"Wayyo Allah na, jama'a ku taimaka min mu shiga da ita cikin mota". maganar take cikin bala'in tashin hankali mara misaltuwa.
"MuntaÆa mu wuce asibiti". ta Æara faÉa tana kamo yarinyar jikinta.
"You are under arrest". taji sautin muryar wani babban mutum a saman kanta, tana Éaga ido taga Æ´an sanda guda biyu suna ÆoÆarin sanyawa Driver ankwa. hankalinta ya kuma kaiwa Æololuwar tashi, nan da nan ta shiga roÆonsu akan su yi haÆuri su bari tukunna a isa asibiti koma meke da akwai sai ayi. Kuma take anan hannu na rawa ta Éauko waya ta kira mijinta ta sanar masa halin da ake ciki wanda ta mance da ya ba ya Æasar ma, da kanta ta Éauki Sa'ida da ke kwance cikin jini ta sanya a mota, har lokacin salati kawai take yi ganin kamar yarinyar ta rasa ranta, driver yaja motar a miliyan yayin da motar Æ´an sanda ta mara musu baya.
Babu wanda ya lura da Safiyya da ke ta ruzgar kuka sai a yanzu, tsoro da fargaba da tashin hankalin da ya risketa yasa ta duÆe a wuri Éaya ta Éoye kanta a tsakanin cinyoyinta, jikinta gaba Éaya rawa yake yi tana kiran sunan Sa'ida, ba ita kaÉai ba duk wani me zuciyar imani in yaga mummunan haÉarin sai hankalinsa ya nemi ya gushe. Wani dattijon mutum ya Æaraso wajenta, yana taÉata ta Éago a furgice, idanuwanta har sun yi luhu-luhu, bakinta na rawa tace masa,"Sa'ida tah kar ta mutu Baba don Allah kar ta tafi ta barni".
Sai kuma tayi shiru tana Æara fashewa da sabon kuka. "Ya Allah? Ya Allah". iyakar abunda take faÉa kenan ta kasa yin aduar da take son yi.
"Kinga kwantar da hankalinki ina ne gidan ku?".
Sai ta miÆe a rikice tana girgiza kanta,"ba zani gida ba, ba zani ba hankalin Abbaa zai tashi Ummani zata yi kuka".
Kai da kaga yanda take maganar kasan ba'a hayyacinta take ba, tsohon ya riÆeta da kau aka tari me napep suka shiga don nufar gidansu ko na su Sa'ida
*YAKASAI B, LAYIN KWALE-KWALE.*
Æarfe takwas na dare a lokacin, unguwar ta Éan yi tsit ba kamar da rana ba, gajiyayyen gida ne madaidaici daga Éarin dama cikin tsakiyar gidaje biyar Éin da ke jere, irin ginin gidan daga waje jar Æasa ce sai ciki kuma aka yi Éan gyare-gyare da bulo sai dai babu filasta, da zarar ka shigo dogon soron gidan guda biyu zaka ji warin daddawa na tashi, soron farkon duhu dunÉum baka iya ganin ko da yatsanka, a soro na biyu kuma zaka yi karo da m