za'a je da mu Kaduna ba, kinga yanzu na sami dama tun da dai monday ba makaranta".
Tayi maganar cike da farin ciki.
Haka suka yi ta maganganunsu har sanda muka fito bakin gate. Maimuna na kallona tace,"Yau me zamu siya?".
Sanyayyan murmushi me faÉi nayi kafin na ce,"abin da aka saba mana".
"Mayyar rake, to ni kam yau siyan rake ba da kuÉina ba, sai dai kowa ya siya abin da ransa ke so". cewar Safiyya tana min harar wasa.
Na harareta da manyan fararen idanuwana, ban ce mata komai ba naja hannunta muka nufi titi muka tsallaka. Sai da muka je daidai wajen me rake tukunna muka tsaya, sallama muka masa ya amsa mana, daga yanayin yanda mu ke gaisawa da shi zaka fahimci mun saba da cinikayyar yau da gobe, yana zuba mana raken a leda Safiyya na ta zuba masa zance, shi kuma yana ta biyeta da yake yana da baki kamarta, irin hirar ta su ba zaka ce a wajen siyan raken suka saba ba, Ni da Maimuna dai sai um da um da ke itama irina ce wajen rashin son magana.
"Ka biyewa zancenta kana ta zuba raken da yafi Æarfin na kuÉin da aka baka".
Maimuna tayi maganar tana Éora hannunta a kafaÉata.
"Æila sai ya kwashe raken gaba Éaya kafin ya ankare". cewata wadda nayi maganar da zolaya kuma lokacin ya Éago ya kalle ni.
Dariyar da Safiyya ta saki yasa muka zuba mata ido, raken ne a hannunta tana kaiwa baki tana ce masa,"Yaya Nazifi kaga waÉannan Æawayen nawa haushi su ke ji saboda ina sha su basa sha, kuma fa daga yau kafin na Æara samun rake me kyau da zaÆinsa har sai nan da kwana huÉu. Don haka Yaya Nazifi rabu da su ka cika mana leda".
Na girgiza kai nace da ita,"ke dai ba ki da tausayi"..
Kallona tayi tana Éaga gira irin eehh taji Éin. Maimuna tace da me raken,"Yaya Nazifi to kaji mara Æaunarka da rashin tausayinka".
Ba tare da ya Éago ya kalle mu ba yaci gaba da zuba raken fuskarsa na washewa da murmushi. gaba Éaya yaran jinsu yake tamkar Æannensa, shiyasa sau tari idan sun zo siya baya basu da wuri sai yay ta laÆai-laÆai don yana jin daÉin hira da su, akwai tarbiya, kama kai da girmama manya. Sai bayan ya Éaure ledar tukunna ya Éago duk ya kalle mu kana yace,"ga shi Æannena asha rake lafiya, yau na san har dalalar yawu za'ai saboda zaÆinsa na daban ne, ai dai sha a hankali kar zaÆin yaywa haÆori illa".
Yay maganar da Æawataccen murmushi kuma cike da zolaya.
Ina kallonsa sosai na Éan waro ido waje na ce,"Naira sittin fa muka baka, wannan kuma ai ya kusan na dubu ko ma yafi".
Maimuna ta ce,"wannan sudar ce ai duk taja, ka rage don Allah".
Annuri ya Æara wadatuwa a saman fuskarsa sannan yace,"kar ku damu Æannena, idan ban baku ba zai zama asara ne, saboda dama da makarantar taku na ke ciniki, ga shi kuma kunyi hutu, kuna ta murna abinku ni kam ina ta fargaba domin zan rasa kasuwa, ko cinikin kwana guda bana so na rasa".
Tausayinsa yay matuÆar kama mu, tun ma daga yanayin yanda maganar tasa da ke tattare da damuwa tsantsa. Safiyya tasa hannu ta karÉi ledar tana ta zuba masa godiya. Maimuna ta warce ledan daga hannunta tana faÉin,"ke ba ki da tausayi sam wallahi, hankalin ma ba shi ne da ke ba".
Sannan ta dubi me raken ta Æara cewa,"gaskiya ba za'a yi haka ba, idan ka barsa za'a samu masu siya ko ba'a nan ba".
Haka muka yi ta fama da shi akan ko yane ya rage amma sam yaÆi, dole muka haÆura muna zuba masa adu'a da godiya. san da muka juya za mu tafi muka ce ya gaida Antin mu ya amsa mana da tabbacin zai isar da saÆonmu. Tare da Æara cewa,"Mahaifiyata bata da lafiya don Allah ku sakata a adu'arku ta kullum".
"Subhanallah Allah ya bata lafiya yasa kaffara, Allah ya tashi kafaÉunta nan kusa, Allah yasa zakkar jiki ne".
Muka haÉa baki wajen faÉar hakan, yaji daÉin adu'ar na mu sosai, ni dai sarkin tausayi har da Æwalla ta taru a idona, muka masa sallama muka wuce, yayin da shi kuma ya Éaga bindi(jelar saniya da ake kore Æuda) yana kore Æudajen da ke neman kawowa raken hari, gefe guda kuma yana Æara Éaga murya da faÉin,"Asai rake, azo a siya rake me zaÆi, ga arha ga daÉi".
Cikin waÆa yake ta faÉin hakan domin janyo hankalin abokan ciniki.
Ai kuwa abin kamar almara, nan da nan sai ga sauran Æ´an makaranta sun zo sun siye shi tas, a lokacin babu abin da ya tuna sai maganar Sa'ida da tace za'a siya insha'Allah, murya a hankali ya ce,"Na gode da adu'arki". Ya faÉa kamar a gabanta, bayan ya gama tattara kuÉin cinikinsa ya tura baron raken ya tafi.
*MANDAWARI ROAD, KANO.*
Daga cikin baÆar mota Æirar Rolls-Royce, wata dattijuwar mata ce fara Æal zaune a bayan kujera yayin da driver ke tuÆata, kallo Éaya zaka yi mata ka gano tsantsar hutu, natsuwa, kwanciyar hankali da jin daÉi a jikinta, ka kuma san lallai naira ta samu wuri ta zauna. kunnenta zuwa wuyanta da tsintsiyar hannunta da Æafarta sanye su ke da gwalagwalai na gasken gaske, ga walwalin adon stones na tsadadden less Éin jik