NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 86 of 97

na fuskanci Nazifi cikin tsananin murna da jin daɗi gami da fashewar kukan tsantsar farin ciki ina miƙa masa kuɗin da cewa,"Hubbi ga shi na ka ne halak malak, Allah ya amsa adu'armu Hubbi yaji kukanmu, Allah yasa ƙarshen wahalarka kenan yasa kuma silar ɗumbin arziƙinka ne mara yankewa". Tunanin da na ke ya katse sanda Nazifi ya dawo yana cewa da ni,"me kika yanke? Ko na ƙara miki lokaci nan da anjima?. Dubu ɗari biyar Sa'ida zata iya isarki taimakawa ƴan uwanki, idan ba haka ba kuma na ƙara miki wata dubu ɗari biyar ɗin kinga har Umra za ki iya zuwa abinki". Hannu na saka na goge hawayena da babu su, dan ban san ma sun ƙafe ba. Ina kallonsa fuskata a washe na ce,"Na amince, na baka kwanakina na tsawon wata guda bisa yardata da amincewata, ka kula da matarka yanda ya kamata, ubangiji Allah ya bata lafiya". Murmushi yay na nuna jin daɗi ya ce,"Na gode. sannan ki nemo sabuwar me aiki don Allah saboda kinga Zahra'u ma'aikaciya ce ba zama take yi ba, kinga akwai yiwuwar a sami me tayata aiki a ranakunta". Nayi shiru ban ce masa komai ba kaina na kan cinyata ina kallon kuɗaɗen, na dakatar da shi daga fitar da yake ƙoƙarin yi, na miƙe na isa gabansa na kama hannunsa na damƙa masa kuɗin na ce,"ba na da buƙatarsu ka ƙara a jarinka". Kallona ya tsaya yi ya buɗe baki zai magana na ɗaga masa hannu. "Don girman Allah kar ka ce da ni komai, kaje kawai raina fess ya ke. Daidai ne dai wanda yay ya sani, haka kuma ranar tsayuwa gaban ubangiji na nan tafe". Dogon numfashi yaja ya sauke idonsa akan kuɗin kafin ya juya ya fita ya bar ɗakin hankalinsa kwance. Hawaye ne suka shiga kwaranya a fuskata, sai na duƙe a wajen ina dukan goshina a jikin gado, kafin na ɗago kaina na kalli sama na ce,"Ya Allah dukkan abubuwan da suke wakana kana ji kuma kuna gani, ka fini sanin dalilin da yasa rayuwa ke ta ƙwallo da ni haka, na sani ba don baka sona ba ne, amma ya ubangijina ka sama min mafita nan kusa, ka sawwaƙe min wannan ƙasƙantacciyar rayuwar da na ke ciki, Ya Hayyu Ya Qayyum ka dube ni saboda tsarkakan sunayenka". Sannu a hankali naji ina samun salama a raina, kaina har lokacin ina kallon saman ɗakin na fara tunano rayuwar baya. *WAIWAYE, SHEKARU TARA DA SUKA GABATA.* *MAFARI...* Ta dabo ci gari, garin da ba kano ba dajin Allah, jalla babbar hausa, yaro ko da me kazo anfika, tabbas a duk inda kaji anyi irin wannan kirarin a kaf faɗin duniya, kasan ba da kowanne gari ake ba face garin kano da ake yiwa laƙabi da tumbin giwa, garin da ya amsa wan nan sunan, musamman idan aka yi duba da yawan al'ummar da ke cikin garin, ƴan asali da kuma zuwo daga ƙabilu daban daban, garin da ya tara manyan Malamai, ƴan kasuwa, Attajirai, ƴan siyasa, Dattawan arziƙi, Sarakai, Makarantun boko da na addini, garin da yay shura wajen haɓɓakar kasuwanci da kamfanunuwa. A tarin unguwannin da ke cikin garin kano, unguwar yakasai na daga cikin manyan anguwanni wadda ake kira da Yakasai rabin birnin kano, idan muka tattara zuwa makarantun da suke cikin garin kano da bamu san iyaka adadin su ba, Shekara secondry school na ɗaya daga cikin makarantun sakandire ta gwamnati da ke a cikin anguwar ta yakasai, me ɗauke da ɗalibai maza da mata. Ɗaya ga watan octoba ita ce ranar da duniya ta shaida a matsayin ranar murnar samun ƴanci na ƙasa najeriya, a bisa girman ranar ga ƴan ƙasa yasa hutu ke ta'allaƙa ga dalibai, ma'aikatan gwamnati, kamfanunuwa masu zaman kansu, har ma da wasu daga cikin ƴan kasuwa. A yau da ya kasance talatin ga watan Satumba, daga cikin harabar makarantar sakandire ta shekara, ɗalibai ne ke ta dabdalar shigewa cikin ajujuwa bayan kammala taron asambili da akayi, mafi yawanci fuskokin su ɗauke da farin ciki saboda murnar hutun da aka basu na tsawon kwanaki biyu sakamakon murnar zagayowar ranar ƴanci na ƙasa. tun bayan komawa aji kowanne ɗalibi ka kalla zaka ga zaƙuwa a fuskarsa na son a buga ƙararrawar tashi domin tafiya gida. Ƙarfe ɗaya da rabi dai-dai aka buga ƙararrawar tashi, kuma a wannan lokacin ajinmu SS2 mune muka fara fitowa. Sunana Sa'ida Salman Madobi, shekaruna goma sha biyar a duniya, ina ɗaya daga cikin sabbin ɗaliban da aka kawo watan da ya wuce da na baro makarantar Aisami na dawo nan ta shekara. Ni ɗin ba doguwa ba ce haka kuma ba gajeriya ba ce ina da matsaikacin tsayi me kyau gami da dirarran jiki na jan hankali, ina da cikar halitta ta ko'ina, doguwar fuskata na ɗauke da dogon hanci da madaidaicin baki da kuma irin idanun da ake kira da sexy eyes, ba zan ce ni kyakykyawa ba ce can amma dai ba na cikin sahun munana ina da kyawuna daidai misali, hasken fatata ba irin hasken nan ba ne sosai kuma ba baƙa ba ce ni, sai dai na ɗauko ɗabi'ar mahaifiyata na bala'in haƙuri da sanyi. ban da yawan magana ina son shiru a rayuwata ni kam, dan ina iya zaman minti talatin a wuri ban magana ba duk kuwa irin
🏠