NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 85 of 97

fi cikin hankalinsa ya ke? Me ya ke nufi da wannan maganar da ya zo min da ita? Idan ni ce bai buƙata mene dalilin da yasa yake zaman dole da ni? Ina tarin ilimin addinin da na sani a ƙoƙon kan Nazifi? Dukkan tunanina ya tsaya cak lokacin da Atika ta faɗo ɗakin tana haki, ɗago idona itama Rumana ta shigo kamar an jefota, kafin nayi tambayar lafiya saboda yanayinsu da ke shaida akwai matsala, sai ji nayi Atika na cewa da shi,"Abba ka je Iyam ta faɗi". Maganar Rumana ta kutsa cikin tata itama tana cewa,"Abba Anti Amarya ce ta mari Anti Fati kuma Iyam taje wucewa hannun Anti Amarya ya bigeta ta faɗi a ƙasa tana can ta kasa tashi, Abba ka taso da sauri Anti Fati tana cewa sai sun yi rigima da Anti Amarya ita kuma Anti Amarya ta ce sai ta faffasa mata baki". Da saurinsa ya miƙe ya fita yaran suka mara masa baya, ni dai idona ya maƙale akan ƙofar ɗakin ina tunanin na tashi na bi bayansu ko nayi zamana?. Zuciyata ta hane ni da tashi na fita, na zauna cikin girgizar lamarin da Nazifi ya zo min da shi, siyan kwanana! bai damu da nawa hakkin ba! Jiyo sautin muryar Zahra'u a sama na miƙe na fita, har zan sauka na fasa na leƙa ta saman ina kallonsu. ta na tsaye tasa hannu ta matse bakin Fati wacce ke tsaye a gabanta tana faman matsutsun ƙwacewa. Shi kuma yana tambayar ba'asin abin da ya faru. Ran Zahra'un a ɓace babu sauƙi ta ce,"Honey waɗanna irin gidadawan mutane ka ke bari suna shigo maka gida anyhow? Kawai fa na sakko ne zan je wurin Iyam sai na isketa bisa gaban dining tana buɗe flask na abinci, to ni ban san wacece ba tunda ban san face ɗin nata ba dalilin da yasa na dakata na iskota ina tambayanta, daga tambaya kuma saboda fitsararriya ce unguwar zoma bata mata gashin baki ba shine take da zarran yi min tsaki tana faɗin na raina mata hankali, Honey can you just imagine ƙanwata ta kusan huɗu na min tsaki? Impossible i must teach her a lesson ba na tolerating raini ko kaɗan". Iyam wadda ta miƙe da ƙyar ta ce,"To Zahra'u yi haƙuri ki cikata ai rashin sani ne. kinga kwana biyu bata gidan shiyasa ba ki shaidata ba Amma daga yanzu ki shaida fuskarta ƙanwarki ce ita ce ƴar Autata, nan take tare da mu ai, ranar biki ne ta koma can gida". Iyam na yin shiru Zahra'u ta kaɗa kai tace,"Am so sorry to say Iyam amma wannan ba magana kika yi me kyau ba, ba hanyar gyara kuma a ciki, kamata yay ki dubeta kiyi mata faɗa kice ta bani haƙuri before then na saketa, amma ba in ƙyaleta ba gobe taji daɗin repeating ma wani, ban sani ba ko halinta ne haka kuma wataƙila tana yiwa matar gidan tana ɗauka sai dai ni ba me ɗauka ba ce". Sai tayi shiru tana mayar da kallonta ga Fatin ta ce,"yanzu za ki iyama Yayanki Nazifi tsakin da kika min ko za ki iya yiwa Maijidda(Yaya)? To ki sani ba sa'arki ba ce ni, ke imfact ko da shekaru guda muke da ke tunda har Yayanki ya auro ni na wuci ki min rashin kunya biyayyarki dole garen". Ta ƙyasta yatsu da ƙara cewa,"And just for today zan ɗaga miki ƙafa amma for the next time idan kika ƙara wallahi sai na saɓa miki kamanni". Ta saki bakin Fatin da ke aikin zare ido don da alama ruƙon bakin da aka mata ba na daɗi ba ne. Kana ta koma ga Nazifin tana ce masa,"you just kept silent ka ƙi cewa komai. Anyway ka gargaɗi ƙanwarka, idan ma akwai wasu irinta to ka tara su kaja musu kunne, ba ƴar iska ka auro ba so they have to respect me kaman yanda su ke respecting na ka. Kuma zai fi kyau ku yi shari'a da wadda tayi muku rainonta domin bata yi mata tarbiya me kyau ba ta cuceku". Ta kalli Iyam ta ce,"ki yi haƙuri bana sane na bigeki ban san da zuwanki wajen ba ne". Ta na gama faɗin hakan ta bar wajen, kuma yanayinta kawai zai shaida maka zuciya ta kai nesa, ganin tayo saman nayi saurin komawa ɗaki. Abin da ya dameni shi ya damen balle na tsaya fassara yanayin da naji akan abin da ya faru tskninsu. Na zauna na saka kuɗin da Nazifi ya bani a gaba ina kallonsu, kallon da yay sanadin haska min hoton wani lokaci can baya shekaru uku da suka gabata wanda ya haska tarrr a cikin kaina, ina hasko lokacin da na fita na bar gida kafin sallar asubahi Nazifi na kwance yana bacci, na fita cikin mamakon ruwan saman da ake narkawa ina me bara gurin ubangiji yasa na zama ta farko a layin da zanje na kamawa mijina, nayi tafiyar ƙasa tun daga Yakasai har Nasarawa GRA a ƙafa ba tare da na tsaya ko hutawa ba balle tunanin abun sakawa a baki. Na ƙara hasko lokacin da na ke tsugune gaban Alhaji Fari ina zubar da hawaye ina shaida masa halin tsananin da muke ciki na rashin cin yau balle na gobe, ina mai roƙonsa arziƙi da ya taimakawa mijina da jari ko da na dubu goma ne ko kuma idan da aikatau cikin gidansa ya taimaka min. Na ƙara hasko zuwan Nazifi a lokacin da kuma sanda Alhaji Fari ya ɗauko tsabar kuɗi naira dubu ɗari biyar ya damƙa su a hannuna ya ce ga shi yayi mana domin Allah. Na ƙara hasko lokacin da na juya
🏠