NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 82 of 97

Amarya su ka fara cika gida, ashe a al'adarsu ana zuwa gidan Amarya kafin a kawota yin wasu shagulgulan. lokacin ne nayi sabuwar kwalliya irin ta burgewa nasa danƙareren less ɗin wajen Safiyya, kwalliyar ɗaukar hankali da shaidawa miji da duk me farin ciki da auren ba gabana aurensu yake ba, har sai da nayi hoto na turawa Maman Yasmin na ce ta aika a nunawa Ummani. Haka na kame kaina natsuwa ta shige ni, babu alamar damuwa tare da ni, ga wani daɗi da naji duk ramata sai ta ɓoye a kwalliyar da nayi, ɓangarensu kam sunata shagalinsu na rawar kiɗan ƙwarya da guɗe-guɗe da rawar al'adunsu. Da ƙarfe shida aka kawo Amarya, kamar yanda al'ada take na kai Amarya ga Uwargida don bada amana haka aka buƙaci da naje na ce da wadda suka aiko a hayo sama nan ne ɗakina, Iyam ta ƙara dawo da me aiken in sauka na ce da ƴar aiken kar ta ƙara zuwar min, haka aka kaɗa aka raya naƙi sauka sai gasu don kansu sun hayo anata faman guɗa, dama na san Iyam ce zata ce dole sai dai ni na sauka na samesu tunda ai su sun san abin da ya dace duk da ban san waɗanna kalar mutane ba ne. Aka shigo da ita ɗakin ina daga zaune kan gado su kuma suka zauna ƙasan carpet. ganin duk iyaye ne na gaida su cikin ladabi suma kuma suka amsa min fuska a sake, ganin da arziƙi da mutunci su ka zo na ba su fuska, nan wata dattijuwa ina ga ita ce Yayar Babanta suka shiga mana nasiha suna cewa ga amanarsu. Cikin sanyi jiki na miƙa mata hannu muka yi musabaha ina cewa,"ina fatan za ki bani haɗin kai wajen ganin mun zauna lafiya tare da zama kan huɗubar da aka mana yanzu ni da ke". Ta bani hannu muka gaisa tana shaida min zata ba ni haɗin kai. Da haka su ka yi sallama kuma suka tafi. Kafin wani lokaci kuma gida yay tsit kowa ya kama gabansa sai bayan isha'i da abokansa da ƙawayenta suka wuce bayan an gama siyan baki. *Ƙarfe tara na dare.* Yayan Shago shi Malam ya wakilta a madadinsa na uba akan ya zo yay mana nasiha ni da abokiyar zamana. Haka kuma a gabanmu Malam ɗin ya kira Nazifi yay masa faɗa sosai akan ya kwatanta adalci kar yay saken da ranar lahira zai tashi sahun maza masu shanyewar ɓarin jiki. Bayan tafiyar Yayan Shago ni da ita da Nazifi muka shiga ɗakin Iyam inda itama tayi nata daidai gwargwado duk da yawancin maganganunta togaciya ne ake yi min. sai dai fa anan na gane tabbas za su janyota jikinsu su mayarta da ita ƴar lele ta gaban goshi, don haka sai abin da na ji na gani kawai amma zan jure sai dai ba zan ɗauka komai ba kamar a baya. Sanda na koma ɗaki Ina shirin kwanciyar bacci wayata ta ɗauki ƙara, ban waiwayi kanta ba sanin me kiran daga sautin ringtone, bayan wasu mintuna sai ga shi da kansa ya shigo. Kallo ɗaya na masa na mayar da kaina ƙasa ina ci gaba da cire yari da sarƙar jikina. ganin yanda na bawa iska a jiyarsa a ƙufule ya kama masifa yana faɗin,"Wanne irin wulaƙanci ne kina jin kirana ba za ki ɗaga ba?". Na kalle shi na ce,"ikon lillahi to ai ban sani ba wayar na silent". Ya ƙara hawa,"to ban hanaki saka waya a silent ba, kika san wa zai nemeki ko abin da za'a faɗa miki". Nayi shiru ban ce komai ba, don na ƙudirci ni kam na daina basa haƙuri akan wani laifi dan na lura hakan ne ke basa damar ƙara cin mutuncina son ransa, ya gama faɗan kana yace,"ki fito ki sameni a ɗaki". Yana juyawa zai fita na ce,"zan kwanta ne fa". Wani wawan kallo ya yarfe min tare da cewa,"ranki zai yi mugun ɓaci". "to wanne ɗakin?". "zan kai sabuwar matata ne tsohon ɗaki? Malama nan ɗakin sama za ki sameni". Ƙasa da murya na ce,"Daga baya kenan anyi sadaƙa da karuwa, baka ajeta sabon ɗaki ba ai ka ajeta tsohon gida ko". Ya jini sarai don ina kallon yacca ya watsa min mugun kallo, na harari bayansa kafin na mayar da ɗan kunnayen na yafa gyalena na bi bayansa. Bakina ɗauke da sallama na shiga, na samesu kan kujera ɗaya ita tana daga gefen hagunsa, na wuce na zauna kan kujerar da ke gefen damansa. lokacin ta ɗago kai muka haɗa ido da ita, sai sannan naga fuskarta don ɗazu da aka kaita wurina fuskarta na lulluɓe cikin lafaya, ba laifi kam tana da kyau amma ba yabon kai ba tabbas na fita kamar yanda Safiyya ta ce. kallon kusan minti guda tayi min kafin ɗauke ido daga kaina, in da na kasa gane manufar kallon nata don har motsa baki tayi ina ga gaisawa zamu yi sai kuma ta fasa, nayi ta kallonta ta gefen ido ina so na karanci yanayin da ke saman fuskarta, a raina na ce Allah ya tura miki aniyarki in har bada nufin alkhairi kika min wannan kallon ba. Shima ina kallonsa yay min wani kallo, ni na kasa gane musu ko kwalliyar da ke jikina ne ya janyo hakan oho, tunda dai ya san ba shi ya siya min abin da yake jikina ba tun daga sama har ƙasa, ko kuma yanda na watsar da shi da lamarin bikin ne ya dame shi ohon masa dai, ga yaga kwana biyu yana faɗa ina mayar masa babu kuma tsoronsa ko shakkarsa tare da ni. Ya tashi ya koma kan k
🏠