da aikin yi kuma ilimina ba na kawo azo aji a gani ba. ga shi yau ina jin na gama karaya akan zan haihu duk da Æarfafa zuciyata da na ke yi da Æwarin gwiwar da kowa ke bani, amma ji na ke kaman na tsinke da lamarin don sai na ke ganin binciken likitocin ba haka ba ne. Ta dafa kafaÉata ta shiga kwantar min da hankali akan na daina damuwa sam, shi duk abin da ya faÉa min ya faÉa ne kawai don son ransa da kuma cin zarafi, haihuwa kuma zan haihu lokaci ne.
Turo Æofar Éakin yasa muka kai dubanmu ga wajen, Nazifi ya shigo cikin kwalliyarsa da alama fita zai yi, kuma da shigowan nasa kamar dama Safiyya a shirye take sai gani nayi ta Éauki waya ta kara a kunne tana wayar Æarya da juya baya karma ta nuna ta san ya shigo, shi kuma ya Æame kamar an danna masa pause idonsa ko Æifce babu akaina yana kallona tamkar bai taÉa sanina ba ko kamar yaga sabuwar halitta.
Murya a hankali na ce da shi,"ina kwana".
Maimakon amsa gaisuwar sai ce yay,"baÆuwa muka yi?". Ya faÉa da sigar zolaya saboda adon da yaga na ci.
Na kalle shi naga still kallona ya ke ya kasa sauke idonsa, ba sai ya fito fili ya faÉa ba amma har cikin ransa na yi masa kyau ta yanda ko bai faÉa ba fuskarsa ta faÉa.
"Kin yi kyau sosai, ashe kin iya kwalliya haka".
Hmm kawai na ce ina ce masa,"akwai wani abun ne?".
buÉar bakinsa zai yi magana sai ta maÆale, idonsa ya koma kan Safiyya yana kallonta da matuÆar mamaki kamar yanda nima mamakin ya cika ni ina dubanta laÉÉa a sake, na kasa gane wayar gaske take yi ko dai ta Æaryan ce.
"Maimuna kema kin girgiza ashe, ni fa sai da na zo na ganewa idona sannan na tabbatar. Ke banda ma dai jaraba irin ta Éa namiji banga abun da ya gani ya liÆewa wannan abar ba, ina ga farin bleaching ne ya ruÉe shi abinki da Éan Æauye da babu wayewa, ko kuma kuÉinta kin san butulu akwai son abin duniya. amma wallahi ba wai don Sa'ida tawa ba ce na rantse da Allah tafi Amaryar komai, indai fagen tsarin kyan halitta ne da cikar surar da namiji zai so to Sa'ida ta mata fintinkau. Sai dai kawai na gaya mata ta dage da adu'a Allah kawai zai saka mata tsakaninta da Nazifi, ke ni na taÉa ganin mutum mara halacci ma irinsa, baiwar Allahn nan ta aureka tun baka da anini kana yawon tura baro haka ta zauna da kai cikin tsanani amma da ya ke dai namiji Æanin ajali ne kinga ai da yay kuÉi ya juya mata baya har yana Æaro aure kuma yana faÉa mata haihuwa yake so na ce bar baÆin munafuki Æarya yake yi algungumi, banda ma zanen Æaddara ai wallahi Sa'ida ba ajin aurensa ba ce, matar manya ce ba ta Æanan Æauyawa da su ka fito gari kwanan ba shima ya sani, sai dai son zuciya irin nasa na butulalle...".
Nazifi yay mutuwar tsaye kawai yana kallon Safiyya da adadin mamakin da ba zai Æirgu ba, ya sani dama ita tun farkon haÉuwarsa da Sa'ida Æ´ar adawarsa ce, amma bai tunanin Æiyayar da take masa har tayi tsamarin da zata dinÆa faÉar maganganu irin haka akansa ba, shi kaÉai ya san me yake ji a game da kalaman nata kamar yanda bai san me zai iya cewa ba don baya da wani kalami a baki.
Ita kam hankalinta kwance take ci gaba da wayarta, tana kallon yanda Sa'ida ta haÉe rai tana hararta ta gefen ido tare da zungurinta amma tayi fiÆi taci gaba da maganarta ba zata yi shiru ba kam sai Nazifi ya harzuÆa ya nemi magana da ita tayi masa da hujja ko kuma ya bar Éakin.
"Bari ke dai Maimuna ai ganin Allah ya haÉa shi da mace me haÆuri ne banda haka wannan iskancin ai bai isa yayi shi ba, to ita Éin ce haÆurinta yay yawa, wallah ba ki ga duk yanda baÆin cikinsa da na Æ´an uwansa yasa tabi ta rame ba, shi kuwa wannan shafaffen tumjin nasa ya Éago, ni so na ke ma zuciya ta zugata ta tayar da aljanun Æarya ta rufe butulalle a Éaki tayi masa shegen dukan da ba zai kuma moruwa ba, kuma ta tursasa ya saketa sai ta barwa Éaya matar ta zo tayi zaman jinya....".
Ransa Éace ya juya ya fita fuuu kamar tashin iska, sai bayan fitarsa kiransa ya shigo wayata da cewar inje in sameshi, ban sami damar maganar da zanwa Safiyya ba na fita cikin hanzari cike da tsoron abin da zai faru. lokacin da na sakko Yaya da su Iyam na falo a zaune ganina yasa suka bini da ido hirarsu ta tsaya, Ko ba su faÉa ba na san sun kaÉu da yanda su ka ganni cikin kwalliya ta kece raini ga shi kuma shi ya sauko daga wajena dole lamarin ya jijjiga su. ina shiga Éakinsa ya kama balbaleni da faÉa yana cewa in yi gaggawar sallamar Safiyya ta tafi ta bar masa gida idan ba haka ba kuwa ba zai kaffara ba minti goma ta Æara sai dai na bita mu tafi tare. Ko da na dawo Éaki na iske har ta miÆe tana ta dariya ranta fess ta ce ba sai na gaya mata saÆonsa ba ta tafi sai wani jiÆon kuma, nima dai na nuna mata bana son ta na magana irin haka akansa tace yanzu ta fara har sai Nazifi ya ÉaiÉaice zata sarara, haka ta wuce ta bar ni raina babu daÉi kuma cike da kewarta.
Da la'asar Æ´an uwan