a bi maganar Safiyya da ban tarar da wannan wulaÆanci da cin fuskar ba, dama ai ba wata tsiyar naje yay min ba bangajiya zan masa na kuma tayasa murna, daren nan kam duk iya satar bacci bai yi nasara a kaina ba, haka nayi ta faman juyi da saÆe saÆe cikin raina har aka yi asuba, kuma sai bayan sallar bacci me nauyi ya kwashe ni.
Bani na farka ba sai Æarfe goma da rabi, ina tashi nayi wanka na shirya cikin shiga me kyau, sai dai ko mai ban shafa a fuskata ba. Fita nayi na je Éakin Iyam na gaisheta, Æ´aÆ´an nata duk sun wuce sai Yaya kawai da sauran baÆinta na Æauye don ko Ummaa ban gani ba, shi kuwa dama ban ma nufi hanyar Éakinsa ba don gwara na kama kaina kafin ya kuma yaga ni. Yauma kamar jiya ni na gyara falon da yay mugun kaca kaca ka rantse bai taÉa ganin tsintsiya ba, a kaÉan Éin lokaci wuri yay fes fes, na shiga kitchen dan Éora abun kari shima nan na taradda shi an kaca kaca da shi an Éata uban kwanuka, Allah ya gani sam ban iya Æazanta ba balle na Éauke kai na ce zan barwa waÉanda suka Éata su gyara, balle na san ba gyarawar za su yi ba. Na tattara su duka na wanke su, sai bayan na gama na Éora jallof na cous cous yanda zai isa har dare ban Éora wani abincin ba, dan ba lallai idan na hau sama ba na sakko yau za su kawo amaryarsu bana son abunda zai ja min Éacin rai.
Kammala aikina yay daidai da zuwan Safiyya kamar yanda tayi min alÆawari jiya cewar zata dawo yauma ta Éebe min kewa. Tana ta hararata saboda na sakko nayi aiki muka hau sama, murnar ganinta a yau kam sai yafi min na jiya, saboda tafe take da takardar sakamakon gwajin da aka yi min jiya, wanda ya tabbatar da cewa lafiya Æalau na ke bani da wata matsala, haihuwa lokacinta ne kawai bai zo ba.
Wannan albishir yasa naji kamar anyi min bushara da aljannah, sai lokacin hankalina ya kwanta don ko sanda Nazifi ya faÉa min cewar lafiya na ke ban yarda ba. Ai kuwa take na kira Ummani na shaida mata itama tayi murna tayi murna tare da adua to Allah ya kawo nan kusa.
Safiyya ce ta zaunar da ni gaban madubi tayi min kwalliya irin ta zamanin nan da ake yi, kasancewar ban taÉa shafa irin su foundation Éin ba sai nayi wani kyau na masifa hancina ya Æara tsayi, kayan da ta siya jiya ta damÆa min tace nawa ne, ba rasa suttura nayi ba haka ba rasa suttura masu tsada nayi ba amma sai naji kyautar ta zamar min ta musamman kuma tafi min dukkan sutturun da na ke da, nayi murna sosai, shaddar na saka wadda ta min masifar kyau, tayi min Éauri na ture kaga tsiya, ni dai duk sai na rasa ma bakin magana don dawowa nayi tamkar bani ba, ashe ban sani ba haka na ke da masifar kyau, dama an ce in kana da kyau ka Æara da wanka, ai kam adu'a iya adu'a nata zambaÉawa Safiyya tare da fatan Éorewar amintarmu. Ta kira min Ummansu mu ka gaisa wacca itama ta Éauki lokaci tana ce min,"Sa'ida kina jina".
Na ce,"Ehh Umma".
Ta ce,"Yauwa to ki buÉe kunne da kyau kiji ni, zama da kishiya ya banbanta da zamanki ke Éaya da mijinki, duk yanda ki ka kai da danne kishinki wataran sai ranki ya sosu kin bayyana shi, haka sai kin matuÆar kauda kai daga kan rawar kansa, abin da zan Æara maimaita miki shine ki riÆe adua, kyautatawa, girmamawa, ladabi da biyayya tsakaninki da mijinki da mahaifiyarsa. tsafta da caÉa ado gami da iya narka soyayya kar ki bar wata tayi miki zarra, idan kika riÆe waÉannan abubuwan ba boka babu Malam Sa'ida za ki kama miji a tafin hannu ki bar wata ta sakakken baki. Ina kuma shawartarki da yin tsafatataccen kishi bisa sunna ba tare da kin bi hanyar saÉawa mahallicinki ba, zaman kishi zaman gasa ne don kowaccenku so take tayi abin da zata fifita a wajen miji, don haka ki zauna ki karanta hanyar tattaro hankalin mijinku gare ki a ko da yaushe. Tsakaninki da kishiya gaisawa banda zaÆewar shiga lamuranta ko bata fuskar shiga naki lamuran, da zarar kin bada fuskar hakan rainin wayo zai samu mafaka, Ki kama mutuncinki da darajarki ta yadda cacar baki ko faÉa ba zai haÉaku ba don ba ajin mace da kimarta ba ne yin faÉa da kishiya, faÉa da kishiya shine babban abun kunya ga mace ki kuma janyo miji ya ke miki kallon mara wayewa. iya abin da zan ce miki kenan Allah ba ku zaman lafiya kema kuma ya azurtaki da haihuwa me albarka, ki kwantar da hankalinki komai lokaci ne, kar ki saka damuwa tunda har bincike ya tabbatar da baki da matsalar komai kina da lafiyar da zaki Éau ciki har ki haife".
Na ce,"in sha Allah Umma za ku sameni mai aiki da nasiharku ba zan bada kunya ba, Na gode Allah Æara muku lafiya da tsawancin kwana".
Na faÉa ina share hawayena.
Ta ce,"amin yasa na Éauki jikina wataran. Idan kunyi waya da Mamar taki kyace ina gaisheta".
Muna zaune da Safiyya tana bani labarin irin wahalar da ta sha a karatu ban san ya akai ba kuka ya Æwace min ba tare da na shirya masa ba, ina faÉa mata ni yanzu ban san ya zan Æare ba a cikin gidan nan idan har Amaryar ta zo tunda har yana min gorin ban