NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 8 of 97

don Allah kar ku saka ya ƙara aure, ba don bana sonsa naƙi haihuwa ba, Allah ne bai kawo lokacinta ba ki duba min Yaya, nayi ƙaranta ace za'a min kishiya yanzu". "Mtswwww". Taja wani dogon tsaki mai muni wanda yay duka har tsakiyar ƙwaƙwalwata. tasa ƙafa tayi fatali da teburin gabanta, lemu da ruwan da suke kai suka zube akan carpet. "Sa'ida kici min mutunci ki tsammaci za ki ci gaba da rayuwa ke ɗaya a wannan tamfatsetsen gidan, kice ke ɗaya za ki mori dukiyar Nazifi?, Bayan kin tauye masa hakki kin hana shi ƴaƴa kice ba zai auro mace mai lafiya ba, ai ƙarya kike wallahi...ni bani hanya na wuce ko in bi ta kanki, banza juya kawai marar amfani". Juya! Kalmar tayi wani tsallen maimaituwa a ƙoƙon kaina, na ɗaga idanuwana nabi ta da kallo har ta fice ta bar parlon. Juya! Juya! Juya!, kalma mafi ciwo da raɗaɗi a duk cikin kalaman da ta gaggaya min, wannan hanyar da suka ɓullo da ita tabbas zata zama hanyar karayata, bana jin zan jurewa gorin haihuwa, duk haƙurina ba zan ɗauki wannan ɓangaren ba. Idanuwana naji su na zugi, duk da ban kallesu ba na san sunyi jajur, sai dai ko kusa ko alama hawaye sun kasa zuba daga cikinsu. Plate da kofunan da ta kifar na tattara na kai kitchen, na dawo ɗauke da tsumma na goge lemun da ya zube kan carpet, ac na ƙaro saboda wurin yay saurin bushewa gudun kar yay ɗoyi. Cikin ƙarfafawa kaina gwiwa na wuce ɗakin barcin Hubbi, ina shiga na gyara ɗakin kaman ko da yaushe da na saba. na hau sama na kwaso kayan abincinsa na sakko da su, akan tebir na ajiye, haka kuma ban canjawa warm coolers ɗin da na tarar ba waje. Ayyuka na daban na tsira duk dan in mance da cin zarafin Yaya, ina ji aka fara kirayen sallar isha'i, ban tsaya da aikina ba naci gaba kasancewar ina cikin jinin al'ada, gyara na musamman na yiwa bedroom ɗin nasa a wannan daren, duk wani kai komo da nake maganganun Yaya ba su bar haska min a cikin kaina ba, sai dai ina ta ƙoƙarin kawar da komai ɗin domin bana son hakan ya tsaya min a rai, don ko Hubbi ba zai san da wannan labarin ba, shiru shiru har ƙarfe tara Hubbi bai dawo ba, kuma bai kirani ba bai tura min saƙo ba. Ɗakina na koma na sake wanka don idan ina cikin jini sam bana sakewa, sai in ta jin kaman jikina duk ya ɓaci, haka kuma kaman ina ta ƙarni. Murmushin takaici nayi da na kalli kaina a madubi, me yasa nayi wannan saken?, ta ya zan bari jikina yay wannan lalacewar?, dududu shekarata nawa?, ni akaran kaina ƙirjina ya daina burgeni balle kuma miji da kansa, ba komai ya lalata ni ba irin saka damuwa a rai, ni da ban taɓa shayarwa ba ai bai kamata ace na bar nonuwana sun zube ba yaraf, bayan na san Hubbi na matuƙar son su, to dole na miƙe tsaye, zan dawo asalina mai cikakkiyar sura ta ko'ina, in kuma fita daga cikin sahun mata masu dugun kai a gidajen aurensu ta ɓangaren shimfiɗa soyayyar aure. Sai da na gama kimtsa jikina tsab tukunna na fito ɗakin na kulle duk ɗakunan sama da kitchen, na sakko ƙasa na kashe fitilun falo tare da kunna karatun ƙur'ani wanda dama da shi muke kwana kullu yaumin. Agogo na kalla naga har ƙarfe goma daidai, tsammanina zuwa lokacin Hubbi ya dawo tun da na jima a ɗakina, sai dai ina shiga ɗakinsa naga babu alamarsa, kenan har yanzu bai dawo ba, take zuciyata tayi zullo na fara jin tsoro, ban san me yake faruwa ba, fatana ɗaya Allah yasa lafiya. Kasa tsaye nayi na kasa zaune, in kai mari in kai gauro saboda kiran lambarsa da nake yi bata ko tafiya. Tunanin in kira office ɗinsa yazo min, sai dai ko da na kira aka tabbatar min da cewa ai tun biyar ya bar office. nan fa hankalina ya tashi, na rasa wa zan kira tun da shi ba wasu abokai gare shi ba, haka yake kamar mace mara son ƙawaye. laluben lambar ƙaninsa na shiga yi, ko da ya ɗaga bamu wani tsaya gaisawa ba na tambayi ko Hubbi yaje gida, yace ba ya gidan tun da rana da yazo gaida Iyam. muna gama wayar na ƙara gwada kiransa, wani sanyi naji a raina da ta fara ringing, sai da nayi kira har sau goma bai ɗaga ba sai daga ba ya message ɗinsa ya shigo. "Ba na son damu akwai abin da nake yi". abin da ya rubuto min kenan, kuma ina gama karantawa na aje wayar jiki a sanyaye, ko ba komai naji dama-dama tun da lafiya yake, sai dai naji babu daɗi sosai, domin kamata yay ace in akwai adalci ya ɗaga wayan ya faɗa min uzurinsa, ko kuma ya rubuta min idan babu daman ɗaga wayar, amma saboda rashin sanin hakkina da girmama aure yana can lafiya ya barni anan cikin damuwa da tashin hankalin halin da yake ciki, ko abinci na kasa ci haka cikina yake fayau tun ruwan safe da na sha. gudun tunanin da ka iya rufe ni na miƙe na kwanta akan gadon. Sai dai me? daga kwanciyar tawa na saki marayan kukan da nayi ta dauriyar riƙewa tun tafiyar Yaya, sautin kukan ya cika ɗakin, kuka nake kamar wadda aka yowa aiken mutuwa don kawai in samu in fitar da baƙin cikin da ke raina. na janyo filo na toshe bakina
🏠