nta da ta Æara tambayar adireshin gidana don Safiyya na daga cikin mutanen da ke tabbatar da maganarsu idan sun faÉa, ko bata zo da Æ´an daba ba to tabbas zuwanta sai ya haifar da rashin daÉi. Sai bayan kiran ma ya katse na ga ashe tun kusan da na fita ne ta ke kira miscalls goma haka ta bar mini, na shiga message ina duba saÆon da ta turo.
_"Beb na kasa yin breakfast, zuciyata taÆi yarda da cewa Nazifi ne zai yi miki kishiya, don Allah ki Éaga kirana ko ki turo min da address na gidanki, yanzu haka ina shirin baro legos nan da awa Éaya da mintuna zan shigo kano jirgi zan biyo, kuma don girman Allah ki daina kuka na sanki sarai, am on my way to na zo nayi haukar da zata sa a fasa auren nan yau"._
Girgiza kaina kawai nayi ina sauke numfashi a fili na furta Allah ya sanyaya miki. Ina kwance nayi nisa cikin tunani Ummani ta kira ni, Allah sarki uwa muryarta kawai ya shaida min cikin damuwa take, bayan mun gama gaisawa ta tambayeni babu dai wata matsala ko na ce mata ehh babu komai har ma na shaida mata masu tada hatsaniyar basa gidan jiya Yaya Babba ya zo duk ya kora su sai dai ban sani ba ko sai anjima za su zo amma dai yanzu daga ni sai Iyam ne sai baÆin Æauye mutum uku da suka zo. Sai sannan naji natsuwa ta samu a muryarta tana aduan Allah yasa ma su tsaya a can gidan su yi bikinsu, haka tayi ta min hira duk dan ta Éebe min kewa, katin wayarta ma ya Æare kuma babu jimawa ta Æara kira wai har ta bayar an siyo mata katin Éari biyu, haka muka ci gaba da wayarmu na shagaltu a labarin rayuwarta da take bani, har sai da taji an fara yi mata warning kana ta ce to ko ta turo min Hindatu da Sa'adatu su tayani zama zuwa yamma sai su dawo na ce mata a'a kar su zo a sami matsala tunda duk suma zuciyarsu a wuya take. Nan ta shiga nanata min da cewa in Æara haÆuri da kauda kai cikin maganganunta na kwantar da hankali da sa natsuwa da haka mu ka yi sallama.
Wajen sha biyu na rana gida ya fara cika da mutane, ashe biki sosai Iyam ta shirya matsayinta na uwar ango dan har sai da ta kai an wangale gate, waÉanda su ka fara zuwan duk Æ´an uwa ne irin na nesa sai jama'arta na tsohuwar unguwarsu, kan kace kobo gida ya Éinke da hayaniyar jama'a kace auren fari ne ko kuma zata aurar da Æ´ar autarta ne. Da kanta ta zo har Éakina karon farko tun zamanta a gidan tace na sauko na tayata karÉar baÆi kafin Æ´aÆ´anta su zo, bayan fitarta na daÉa gyara jikina tukunna na fita, tunda na sakko ido yayo kaina ni kuwa na mayar da komai ba komai ba kamar yanda mahaifiyata ta ce da ni, don haka cikin fara'a da mutuntawa muka gaggaisa da mutanen da na samu a falo sannan na wuce Éakin Iyam, can na sameta sunata hidima ita da muÆarrabanta, na ce mata gani me za'ai, tayi min nuni da kulolin abinci tace in ke zuzzubawa ga plate ina kaiwa baÆi. Kamar na juyawata na koma Éaki ganin an raina min hankali amma haka na daure kawai na shiga buÉe kulolin ina zuzzuba abincin, alala ne da dambu aka yi sai lemon zoÉo da na jinja, idan na zuba kamar faranti biyar sai in Éauka in je in raba kana na dawo, hidimar baÆin nata dai ta dawo hannuna gaba Éaya kuma ko kaÉan ban bar wani shaida da za'a karanci Æunci da kishin da ke danÆare a zuciyata ba balle aji daÉin yaÉa min magana amma a haka ma ban taira ba, don ina jin ÆusÆus Éin wasu na cewa ko dai ba na son mijin dama ko kuma akwai abunda na Æulla don haka banza dai ba zan ke wannan sabgogin ba.
Sai da lokacin sallar Æarfe Éaya kana na yakice na koma Éaki, sallah nayi na kishingiÉa ina hutawa don na gaji kam. Lubabatu su ka shigo Éakin ita da baÆi wanda ta rako, matan abokansa ne da suka yi tasowar yarinta kuma ban yi mamakin ganinsu ba dan dama da su ne mu ke ma'amala ta mutunci tun a tsohuwar unguwarmu, na tarbe su cikin mutunci nasa Lubabatu ta kawo musu abinci duk da ina fargabar kar Iyam ta hana, to da yake taga baÆin sun shafi Éanta sai ga uban abinci kuwa an hayo da shi, mun yi hira da su sun nuna min kulawa kusan zan ce don su taushe ni ma shi ne maÆudin zuwan nasu ba kamar yanda nayi tunanin Æ´an taya murna ba ne kamar yanda na san mazajensu za su taya shi.
Bayan tafiyarsu Iyam tace na zo mu ci gaba da aikin raba abinci ni da Lubabatu, lokacin Æarfe biyu da rabi a sannan ne Lubabatu ke labarta min ba'a jima da Éaura auren ba yanzu haka wasu har sun kamo hanyar dawowa, furucin nata yasa gabana faÉuwa da Æara jin matsananincin kishin Nazifi. ina tsaka da rabon lemo sai ji nayi anwa hannuna muguwar damÆa, na kaikato kaina wajen ganin waye don har ga Allah zatona ma ko su Anty Aisha ne Æ´an neman bala'i da hana kwanciyar hankali suka dawo, sai dai me! ware idon da zanyi sai ganin Safiyya na yi, ban san lokacin da na watsar da kayan hannuna ba na Éago gaba Éayana na rungumeta cikin murna da jin daÉi sai kuma kuka kamar dama jiransa na ke yi.
Bata Éago kaina daga kafaÉarta ba ta kama hannuna zamu bar wajen