NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 76 of 97

a wata lambar ta kirasa don sai bayan ya ɗaga ne ya ke cewa,"wannan numbern fa ina na ki wayan?". da haka kuma ya tashi ya fice yayin da na ke jin zuciyata kamar zata yi bindiga. Ya jima kafin ya dawo ciki, kuma sai lokacin ne ma yake kashe wayar don ina ji yana ce mata,"Kishiyar Iyam ce sai Yayyuna biyu da ƙanwar Malam. Sai dai mun ƙaraso ɗin nan da sha ɗaya jirgin namu zai ta so". Idona ya cika da ruwan hawaye inda na ke kallon fuskarsa da ke bayyana annurinta. da ƙyar na mayar da hawayen idona da ke son zubowa, na rufe ƙur'anin da na ke karantawa na tashi tare da ninke sallayar duk na mayar da su ma'adanarsu. na zauna gefen gadon ina cewa da shi,"ina kwana". "Lafiya lau". ya amsa a gajarce. Tun daga haka ban ƙara magana ba, kuma kamar jira ake gari ya waye sai ga kira na ta shigowa wayarsa, ba ya numfasawar minti guda wani kiran zai ƙara shigowa, har sai da shima ya fara gajiya da hakan don dama tun daren jiyan na lura a gajiye ya ke sosai. Fita nayi na bar masa ɗakin na kama hidimar gyaran gidana, sun yi kaca kaca da falon har ƙarni yake yi kuma an rasa me gyarawa duk uban ƴan matan cikinsu, gidan dai tsit ina ga sunji kashedin Yaya Babba sun kama gabansu, cikin ƙanƙanan lokaci na kimtsa falon na tashe shi da ƙamshi, kana na koma sama nayi wanka na shirya tsab abina na ci kwalliyata ina ta yin iya ƙoƙarina wajen basar da lamarin bikin nan, kuma Allah sai ya saka min natsuwa a zuciyata, duk da babu ƙunshi babu gyaran kai amma fess na fito nayi kyau da ni, ban baro ɗakina ba sai da na gyara shi na sanya karatun ƙur'ani. Lokacin da na sakko ƙarfe takwas da rabi, na leƙa ɗakin ina ce masa,"Zan ɗora abinci ne da kai?". Wani kallo yay min kafin yace,"Da sai kin tambayeni?". "Yau ɗin kamawa tayi na tambaya". "Kiyi duk yanda yay miki". Kafaɗa na ɗaga na fita, kunun tsamiya na ɗora da soyayyar doya babu ƙwai, ina ga ƙwan sun cinye shi daga shekaranjiya zuwa jiya, dama kiret uku ne yay saura yana cewa za'a kawo ba'a kawo ba. Ban ɗora da yawa ba, daidai cikina da na Iyam da na yaran ne, yanda na ke ta abuna kamar ba wadda za'ai wa kishiya ba. na zuba doya a flask ɗin zan kai mata sai ga shi ya shigo kicin ɗin sanye cikin dakakkiyar shadda fara sai uban ƙyalli da ɗaukar ido take yi, an yiwa babbar rigar azababben ɗinki irin na sarakai, fuskarsa sai fidda annuri yake irin na sabbin angwaye masu ɗoki, ƙamshi kuwa la'ila ha'ilallah ban taɓa dai jin ƙamshi me irin wannan daɗin ba. Kibiyar kishi ta soke ni naji hannayena sun shiga karkarwa, da ƙyar na iya saita kaina. Muryarsa a tausashe yace da ni,"Zamu wuce can wajen ɗaurin auren, a Abuja ne na san kin gani a katin, ban san lokacin da zamu dawo ba amma ba zama zamu yi ba ana ɗaurawa zamu taho. Amarya sai gobe za'a kawota, babu wani abu da kika buƙata zan iya tafiya?". "Babu komai". Na faɗa a sanyaye. "Don Allah Sa'ida kar inji wata fitina. ko Iyam ba wani taro zata yi ba duk ƴan uwa ne". Na ce,"fitina ai sai fitinanne, ni da banda matsala da kowa". Ya ce,"Na tafi to". Na ce,"Allah ya kiyaye ya tsare hanya, a dawo lafiya". Ya amsa da amin kana ya juya ya fita ni kuma na rakashi da ido, babu yacca ban ba hawaye karsu zubo min amma ina marayan kuka na saki ina durƙushewa a kicin ɗin. Ubangijin da ke da iko da zuciyar kowanne bawa shi kaɗai yasan irin zafi da raɗaɗin da zuciyata ke yi a wannan lokacin. Haka na ci kukana na gode Allah kafin in miƙe da ƙyar in wanke fuskata a cikin sink ɗin kicin, kaina kuwa kamar zai tsage saboda azababben ciwo, ga jikina da ke karkarwa kamar me shirin kwancewa zazzaɓi. Abincin da na gama haɗawa na kwasa, sai da na haɗe har da nawa na juye a ciki don sam bana tunanin a yau dai wani abu shi abinci zai shiga cikina, ai ko yawun bakina jinsa na ke tamkar maɗaci. Ina shiga ɗakin Iyam na aje mata abincinta, kallo ta bini da shi da mamakinta na ganina fess kamar ba wadda miji ke ƙara aure ba, kuma saboda an fi son ganinka a ƙuntatace har ce take to Allah sa ba mugun abu na ƙulla ba don ita bata taɓa ganin wacca za'a kishiya na harkokin gabanta ba rai fess a ranar biki. Na fito ina ƙwala kiran su Rumana Iyam ta leƙo tana shaida min ai da su aka tafi jiya, ta faɗa tana ta ƙare min kallo gami da ƙara cika da mamakina, kicin na koma na aje abincin na su kana na koma ɗaki, ina shiga kuwa na tarar da wayata na ƙara da sauri naje na ɗauka sai dai ganin sunan da ke kan screen ɗin yasa ban ɗaga ba. _"zan yo hayar ƴan daba mu zo gobe"._ Maganar ta Safiyya a jiya ta haska min cikin kai, don haka kawai na mayar da wayar na ajiye, na sani Safiyya me matuƙar damuwa da damuwa ta ce, tana kira ne don taji a wanne hali na ke, to sai dai raunin da ke tare da ni ba zai iya ɓoye halin da zuciyata ke ciki ba wanda ko da na faɗi akasin hakan don ɓoyewa za'a ƙaryata ni, kuma ina tsoro
🏠