NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 74 of 97

fiyya". "Shi wa?". "Mijin nawa mana". Wani zabura tayi daga kan gadon da take kwance tare da faɗin,"A'uzubillahi". Sai kuma ta danno ashar ta ce,"kina nufin kishiya aka yi maki?". Na ce,"za dai ayi gobe in Allah ya kaimu". Yadda ta daki ƙirjinta da ƙarfi ina iya jiyo sautin dukan ta ce,"kuma sai kike mene ke yanzu?". Yanda tayi maganar kaɗai ya sakani sakin murmushin da ban shirya ba ina ƙara haskota da yanayin al'amuranta a cikin idona. "Beb na ce sai kike mene yanzu da za'ai miki kishiya?". Na ce,"sai na ke zaune mana gani muna waya da ke ina jin daɗi". Ashar ta ƙara lailayowa ta yarfa min. "Sa'ida Salman Madobi bura'ubanki na ce, za'ai maki kishiyan kike gaya min kina zaune miji da amayarsa na can hotuna na yawo a media ba ki tafi kin bankawa ƴan iska wuta sun babbake ba, kai Allah ya tsinewa sanyin halin da na sanki da shi. Kar dai ki ce min babu wani mataki da kika ɗauka kan lamarin, na wawoo i cant imagine wai Nazifi ne zai miki kishiya, hey duniya ba tabbas wai yau Nazifin Sa'i zai haɗata da wata, hewoo ni ko ina zan taɓa yarda da namiji". Na ce,"Wai ba zamu gaisa ba ne Safiyya kina ta faman magana". "Ba za'a gaisa ba ɗin, za ki hanani magana saboda na taɓa zuciyarki. Kin san yanda na kaɗu da lamarin kuwa? tukunna ma! kuɗi ku ka yi ne don naga ba shigar tsumma yay ba, kuma yay ƙiba ya murmure abunsa har da tumbi, if i guess right Nazifi Mai Kalwa yay kuɗi ya juya miki baya shine har zai ƙara aure. Ke kuma shashasha Sauna kina kallonsa you didnt take any worst action. Wait let me drink cold water becoz ina jin numfashina na seezing kar in faɗi in mutu lokacina bai yi ba". Ina jiyo yanda take kwankwaɗar ruwa, bayan ta gama sha tace,"Na fi kowa saninki, ba ki komai ba akan lamarin auren nan, ba kuma za ki ba, kina nan kina kuka idan kika gama ki kama kiran sunan Hubbi. To Hubbi ya ci bantan bura'ubansa ɗan shegiya annamimi butulu mara halacci. Kinga kina jina ba, just give me your address ina lagos yanzu haka na zo wata seminar, zan yi hayar ƴan daba mu zo gobe, sai na sa an karairaya Nazifi Sa'ida kinji na faɗa miki, ita kuma shegiyar da ke ƙoƙarin shairing miji da mijin Ƙawata zan yanke mata nonuwa duka don uban babanta, lamarin Nazifi wasa ne. Kinga gida guda za ku zauna?". Shiru ban ce da ita komai ba, gwara na barta ta gama zazzaga masifar sai muyi wayar arziƙi. jin shirun na wa kuma yasa ta cewa,"kai Allah ya kwashewa Nazifi albarka kasa ya ɗaiɗaice, ya rasa wadda zaiwa kishiya sai ke Sa'ida, Allah ya isana ban yafe masa ba wallahi, ina ma mota tabi ta kansa ya mutu dama ai ba son aurenku na ke ba". Nasa hannu na goge hawayena, sai kuma kukan yaci ƙarfina na kasa riƙe shi. Nan hankalina Safiyya ya tashi ta sassauto ta shiga lallashina har sai da nayi shiru. Na bata labarin komai da ke faruwa, tayi shiru kiran yana ta tafiya sai da na kira sunanta kana ta ce,"na suma ne bari na farfaɗo tukunna, ai ban san abun yay tsamari haka ba, ke kuma duk kika manta kina da ni, ko da ya ke ba wani sona kike ba dama kin fi son wannan gantalallan mijin naki". Nuna mata nayi bana son tana zagar min miji, hakan yasata cewa,"Am sorry Beb amma zan shigo kano just becoz of you indai ina da rai da lafiya. kin san ina jin magananki so nayi shiru da zage zagen, Nazifi ne yaje da halinsa amma wallahi ba zan fasa tsine masa ba kuma Allah yasa matan ta kwashe kuɗinsa duka ta gudu ta barsa da paralyzed, kuma ba zai taɓa haihuwa ba ko zai auro mata ɗari, ina ma abun nasa ya ruɓe in ga ta inda shi zai haihun". Kai na girgiza kawai na ce,"kinga mayi wayar wani lokacin". Na faɗa ina kashe kiran don ba zata daina wannan mugggan adu'an da maganganun nata ba, bata san zata iya faɗa a bakin mala'iku ƴan amin ba. Da Yamma ina kwance ɗaki abun duniya ya ishe ni Hajjo ta zo ita da yaranta biyu Amina da na ke kira Mamana da kuma Muslimata. bayan mun gaisa na kawo musu abun sha tana kallona tace min,"Nazifi ya kira ni ya karanta min duk halin da ake ciki, faɗan da kika ji ina yi miki ɗazu nayi ne saboda fuskantar yana wajen. Mahaifiyarki ta faɗa min gaskiyar komai dan ko da muka yi waya da shi ba yarda da zancensa nayi ba, namiji me kai ƙara ba abin yarda ba ne. Daga can gidan naku na ke yanzu, itama mun yi magana ni duk sai yau na ke jin komai, tana ta faman nanata min kalmar haƙuri kin san hali, na ce mata ai shiyasa mata da yawa ake wayan gari zuciyarsu ta buga sun mutu saboda baƙin cikin ɗa namiji, to ƙilan kema so take ki mutu ina jin dai sun gaji da ke ne. anji haƙuri ba ya yawa kuma me haƙuri shi ke da riba amma irin haƙurin da ke kike yi ba komai ba ne sai cutarwa Sa'ida, kawai saboda kina da haƙuri sai aka ce kike ɗaukar kowanne cin kashi, bama na miji ba kawai har da ƙanne da Yayye, anji mahaifiyarsa idan ta miki anan ki kauda kai, amma banda ƴan uwansa saboda haka ki takawa kowa burki Sa'ida kina jina, ko matarsa ce ta shigo karki wa
🏠