NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 72 of 97

a kuma cikin huci take faɗin,"barni Suwaiba in daki yarinyar nan ta gane Annabi ya faku, ƴar cikina tayi min rashin kunya in ƙyaleta, idan ban sa Yahya ya ɓaɓɓalata ba shegiya na ke sai dai muyi shari'a. Kamarta fa na shayar da wannan Nonon". Ta faɗa tana nuna nononta da kuma juyawa ta kalli Fati ta ce da ita,"ke sauka kira min su Mardiyya ni ba zan yi da ita ba sai dai Ƴaƴana". Ko ɗar ban nuna mata tsoro ba, ina tsaye yanda na ke ƙam su ko sai faman haƙuri suke bata, ni dai abu ɗaya kawai na sani ba zan daku ba kuma ba zan yi duk abunda za'a saka ni ba sai idan naga dama. Nazifi ne ya shigo duk kuma sai suka ja da baya suna ba shi wuri, ya kalli Yayan yana ce mata,"me yake faruwa?". Daga tambayar kuma sai ta kama balbale shi da masifa, ai ya barni duk na raina su bana ganinsu da ƙima, ƙarshema rashin mutuncin nawa har ya kai ga kan mahaifiyarsu, shi kuma da bai san darajar uwarsa ba ya bar matarsa na barinta da yunwa, to ko ya ɗau mataki ko kuma ita ta ɗauka da kanta. Shi kuwa cikin girmamawa ya shiga bata haƙuri kana ya juyo gareni nima yace na bata haƙurin, ba don raina ya so ba na ce tayi haƙuri kana suka fita a ɗakin su ka barmu. Tun bayan fitarsu ban kalle shi ba na nemi wuri na zauna. Ina jin kallonsa a jikina wanda na ke hango fuskarsa ta cikin madubi na shaida tsananin ɓacin ransa. Can yay nisa ya ce da ni,"me ya hanaki yin girki?". Kai tsaye na ce,"saboda bana jin yunwa". "Idan ke ba kya ji sauran mutanen da ke cikin gidan fa?". "Wanda nauyin dafa masa ke kaina ma ban dafa na ba shi ba". "Kina nufin me kenan Sa'ida?". "Ina nufin mijina ma ban dafa na ba shi ba balle wasu da hakkin ci da su ba a kaina ko na me gidan yake ba, wanda ya damu da yaci ai ya san hanyar kitchen". "Har da mahaifiyata?". Nayi shiru ban ce masa komai ba, ya ɗaga murya da ke shaida ɓacin ransa ya ce,"tambayarki na ke yi har da mahaifiyata ma sai dai ta shiga ta dafa da kanta?". Shiru na yi na ƙi cewa komai. Yay ƙwafa yana jijjiga kai kafin ya ɗauko waya a aljihu, bayan wucewar sakannin da ba su wuce goma ba na ji yana faɗin,"Kiyi haƙuri Hajjo zan takura ki, kamar yanda na faɗa miki ne dai a ɗazu na kasa yin shiru kan abubuwan da Sa'ida ke min a gidana saboda bana so azo ga matakin da kowa ba zai ji daɗinsa ba, ta san me ya faru a baya to ina tausaya mata shiyasa ba zan mayar da ita gaban su Kaka ba don har yanzu ta kan hukuncin Abbaa da ya yanke mata na rashin zuwa gida, amma hakan bai sa ta gyara ɗin ba". Ai yana cewa Hajjo na zuba masa ido, idan nasa mamaki a matsayin kallon da nake masa tabbas na yiwa kalmar rashin adalci. "Tom shikenan gata". ya miƙo min wayar na karɓa ina kallon screen ɗin da ke ɗauke da sunan Yayar mahaifiyata Hajjo, ƙirjina ya buga na runtse ido nasa wayar a kunne, ina ga dai hankalinsa ba zai kwanta sai ya shiga tsakanina da kowa nawa tukunna, ita kuma ko me haɗa ya faɗa mata oho, kai Namiji Ƙayar ruwa baka san da ita ba sai ka taka, kamar yanda ban san da wannan ɓoyayyan halin na Nazifi ba sai a yanzu da duniya ke gara masa. Hajjo ta katse Sallamata da ce min,"ke kuma mijinki yay ta kai ƙararki hakan kika zaɓarwa kanki ko Sa'ida?". Na rumtse ido ina jin zuciyata na bala'in matsewa, muryana a hankali kuma a raunane na ce,"ba haka ba ne Hajjo kiyi min alfarmar tsayawa kiji ta bakina kar ki yanke irin hukuncin su Kaka...". Murya ta ɗaga wajen dakatar da ni,"dalla can rufe min baki, wanne irin iskanci ne da rashin sanin darajar iyaye yasa za ki ƙi dafa abinci ki bawa uwar mijinki, dan ubanki da bata haiifa ba har kya ganshi ki so ki aure, wawiya kawai idan ba ki bi uwar miji ba ta ina za ki kama mijin naki a tafin hannu, ko haka kika ga matan yayyunki na wa mahaifiyarki, ba gida guda su ke ba amma kullum da kwanon abincinta a gidan matar Sa'id. Kishiya kuma akanki a ka soma? kaf cikin mu biyar da mahaifiyarmu ta haifa wa kike gani tana zaune ita ɗaya banda mahaifiyarki? Kuma ƴan uwanki Samira da Husna duk ba kishiyoyin ne da su ba, kin taɓa zuwa kinga wacca kishiyarta ta zauna akanta? Ko kin taɓa jin wata cikinsu mijinta ya kai ƙararta akan kishiya, sai ke saboda sakarci da shashanci za ki ɓata rawarki da tsalle, to ki shiga taitayinki wallahi, kar na ƙara jin makamanciyar magana irin haka ta kin hana uwar mijinki abinci, ita kam ko ce tayi ki kwanta tabi ta kanki ki kwanta biyayya dole, Saboda haka yanzu muna gama wayar da ke ki wuce ki girka abinci ki kai mata tare da bata haƙuri kina jina". Na ɗaga kai kamar ina gabanta na ce,"zan bi umarninki in yi yacca kika ce in sha Allah". Sai kuma ta kama yi min faɗa sosai akan rashin bashi hakkinsa da na ke, shi ko kunyar kai mata wannan ƙarar ma bai yi ba. Tana faɗan tana haɗawa da aya da hadisi har ta gama kana mu kai sallama da ita bayan ce min da tayi tana tafe nan da anjima zata zo in gwada mata kalar iskancin da nake yi tunda har an iya aka
🏠