ce ya gaida su Yasmin da Ajmal sannan na ajiye wayar daga gefena. Har na aje wayar sai kuma na Éauka na kira Ummani, itama hankalinta ba Æaramin tashi yay ba da ganin kiran nawa, musamman da ta jini ina kuka sosai.
"Sa'ida me yake faruwa ne? Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un".
"Ummani aure zai Æara kuma bai faÉa min ba tsabar bai Éaukeni da daraja da Æima ba a cikin gidan nan, Ummani na gaji ni kam na gaji ba zan iya ci gaba da zama ba don ban san da manufar da ya Æullo auren ba, ki cece ni Ummani kar su kashe miki ni da baÆin ciki".
Daga Éangaren Ummani ta jinjina kai tayi shiru domin ita kanta lamarin ya taÉata, Æarin aurensa ba abun mamaki ba ne, kawai ta yanda ya Éullo da lamarin wajen Æin shine abin takaicin da Éacin rai. To ya za'ayi ita uwa ce, bata da wani kalami da zata faÉawa Æ´arta wanda ya wuci nasihar dai da ake yi kullum, sai kuma ta kwantar mata da hankali, in ace ma Abbaa ya sauko ne sai tace to da safe ta taho gida ta zaune ta rage zafi in suka gama bidirin bikinsu ta koma in Æ´an uwan nasa sun bar gidan, amma tabbas Nazifi bai kyauta ba ko kaÉan, ita tsoronta ma kar su illata zuciyar Æ´arta amma babu komai adu'a bata bar komai ba, tana yi mata za kuma ta Æara dagewa akan hakan.
Da kalamai masu daÉi da tausasawa mahaifiyata taita lallashina tana bani baki tana nusar da ni fa'idar haÆuri da Éauke kai da miÆa dukkan lamura ga ubangiji, da sannu komai zai shuÉe ya zama tarihi.
Tun bayan gama wayarmu da Ummani na kwanta babu abunda na ke sai hawaye, hawayen da sai da ya jiÆa filon da na ke kwance, ban san dalilina ma na damuwa akan lamarin auren nan ba, ai tun ranar farko da Yaya ta zo taci zarafina na sakawa raina muddin ba haihuwa nayi a gidan nan ba ba fa zan huta da gori da cin mutunci ba, aure kuma kamar Nazifi ya riga yayi ne na san da wannan don da hankalina ai da tunanina take takensa kaÉai sun isa su sanar da ni hakan, to da yake dai kishi halitta ce a jikin tsokar zuciya babu yanda zanyi sai dai nayi ta adu'a Allah ya sauÆaÆa min, sabon tozarci ne dai na san zan fusance shi idan matarsa ta zo, haka nayi ta faman lissafin yanda zan fara gudanar da sabuwar rayuwata a cikin gidan daga gobe.
Kaman yanda na saba cikin dare nayi sallolina na kaiwa Allah kukana, karatun Æur'ani tunda na fara sai da na sauke izu goma ina karatun ina kuka, kuma kaman Éaukewar ruwan sama haka hawayen idona ya Æafe babu ko saura da ke son fitowa daga zuciyata, wani Æwarin gwiwa na shigana wanda ban taÉa jina a cikinsa ba dangane da abunda na Æudurta a raina.
Washegari da safe ban farka ba sai wajen Æarfe goma na safe duk da ba baccin daÉi nayi ba, Lubabatu dai ta leÆo wajen takwas tace Rumana ta fito za'a kaisu Æunshi da kitso to tunda na mayar da Æofar na rufe ban Æara buÉewa ba duk da naji an zo an buga nayi biris.
Shi kuwa dama yau ban shirya zan leÆa wurinsa ba sam balle tunanin abunda zan shirya masa ya ci. Na yi wanka nayi shirina nai zamana a Éaki na kunna data na hau online don Éebe kewa amma duk da haka can cikin zuciyata na Æarayin babu daÉi, ina cikin tunanin abunda zai faru tsakanina da su idan na fita sai kawai ganin Yaya nayi ta shigo cikin Éakin babu sallama tana banka min uwar harara, ban san garin ya aka yi na mance ban saka maÆulli ba don ni Æudirin da nayi yau cikinsu babu me ganina.
Æirjina ya buga na sauke dogon numfashi, kafin tayi magana cikin sanyin jiki kuma a tsorace na ce,"ina kwana".
Ta zuba min ido wajen kallona ta ce,"da ban kwana ba za ki ganni ne tsaye gabanki, wato ke ba ki da mutunci ko, wuyanki har yay riÆar da gari zai waye ki Æi sakkowa ki dafawa mahaifiyarmu abinci saboda ba ki da tarbiya ba ki san darajar iyaye ba, idan uwarki ce za ki hanata abinci ko da ita ta saka aka yi miki kishiyar?".
Kaina a Æasa na ce,"don Allah kar ki Æara sako mahaifiyata kiyi komai akaina ni Éaya".
Ai kuwa ta fusata tayo kaina zata mareni na riÆe hannun da Æarfin da ban san ina da shi ba, a hankali na sakko na tsaya gabanta ina kallon cikin idonta na ce,"Kin bani shekaru sama da sha biyar, a haife kuma kin haife ni, ba iya aurar da kamata kika yi ba har jikoki kina da. Bai kamata ace da girmanki kina dabi da Æ´ar cikinki ba kuma matar Æanin Æaninki, kamar hakan abun kunya ne, don haka na roÆe ki kija sauran guntun mutuncin da nake ganinki da shi kar kiyi saken da zan bi ta kai in taka na wuce, bana saurin rama abu ina da haÆurin shanyewa amma duk ranar da tura ta kai bango babu wanda zai ji daÉina, ba zan so in gwada miki a yanzu ba saboda darajar Æ´arki da ke hannuna".
Kallona take yi cikin tsananin mamaki, sai kuma ta harzuÆa ta Æwace hannunta da na ke riÆe da shi tana faÉin sai tayi min duka taga wanda ya tsaya min. Hargaginta ya janyo hankalin Æ´an Æasa sai ga su yuya guda kamar za'ai yaÆi. Suwaiba matar Yaya Babba ce ta riÆeta tana bata haÆuri, it