a na auri Nazifi da yanda ahalinsa su ke a baya, la shakka sai anyi rubutun babban littafi na butulci akansu.
Ni dai duk Éage Éagen kayan da su ke yi kaina na Æasa, na Æagu su tattara su kwashi kayansu nima in tashi in bar wajen. Æawar Iyam ta kira sunana tana cewa,"Uwar gida ba ki ce kaya sun yi ba".
Iyam tayi caraf ta ce,"tana baÆin ciki ai bata faÉa ba, wa ya san me ke zuciyarta yanzu. Kuyi kuyi a rufe su kafin ta cinna musu wuta".
Ni dai ban Éago ba kuma ban yi magana ba, banda kuma niyyar cewa Æala, duk da irin shewar da suke yi na daÉa Æona zuciyata, kuma dama na san an kira ni na zo Éin ba don komai ba sai don a Æuntata min. Ummaa har faÉi take yi wai to duk irin hidimar da Nazifi yay min har na yi baÆin ciki da aurensa ko hidimar da yaywa matar da zai aura in dai ba rashin halacci irin nawa ba, kuma banda abuna Éan miji ai Éanka ne, idan ta zo ta haifa duk tsiya nima nace Éana. A wannan lokacin ne Anty Aisha ta shigo, sallamarta ce tasa na Éaga kai, taci kwalliya ta caÉa ado tana taunar cingom kamar wata Æ´an mata, ni ban lura ba ma babu ita a wajen ba sam, yaran da suka shigo da kuloli ta kalla ta ce,"ku kai can ku ajiye".
Sai ta Æara cewa,"Iyam yamma tayi fa kar dare yay mana a hanya, kin san sun ce a yau za su wuce da lefen can Abuja wurin Kakarta. ga kulolin kayan garan can a mota, kajin kuma da aka soya gaba Éaya kula uku ne na Éebarwa wannan Æ´ar a ciki gashi nan a leda, dublan da alkakin ne dai ga kula guda nan an bar mata".
Haka suka Éunguma gaba Éayansu su ka tafi, tsabar yawansu motocin gidan biyar aka Éiba, bayan fitarsu na tashi na bar wajen ban ko bi ta kan kulolin da aka ce na Éauka ba, ina jin Iyam na Æananun maganganu akan na raina abun da aka bani, itama ban kulata ba nayi gaba abuna, kaza dai ba zan Éauka ba don ba yunwarta na ke ba, dublan da alkaki duk ba na ci sune mayunwatansu.
Da daddare ina kwance sai ga Nazifi ya shigo Éakina da munafukan akwatinansa guda biyu wai na faÉar kishiya, baÆin ciki ya tokare ni, to ai ko lokacin da zai auren sanda baida uwar komai akwati biyu ya shaÆo min da kaya da Æaramar jakar bakko Éaya. don haka ko kallo bai isheni ba shi da kayansa na juya masa baya, ina jin yana faÉin wai ko na raina ne, ban ce masa kanzil ba nayi ma kamar bacci na ke yi, ya gaji da tsayuwarsa ganin banda niyyar kula shi ya ce,"Allah ya gani na fita hakkinki, ga su nan ki Éauka ko kar ki Éauka ruwanki. Kuma idan akwai abunda kike buÆata sai ki faÉa min".
Ya faÉa yana juyawa ya fita ya bar min akwatunan, ai kamar an finciko ni haka na miÆe na duro a gadon, Æafa nasa na dinÆa tura akwatunan har na kaisu bakin Æofa kana na cilla su waje, kallona ya tsaya yi da mamaki da takaicin jefa masa kayansa a gaban Æafafunsa, na kalle shi na banka masa harara tare da jan tsaki na danna Æofata na rufe tare da sanya maÆulli, babu yanda bai da ni ba akan na buÉe Æofar na Æi, har da min barazanar zai kira Abbaa a waya yanzu ya faÉa masa rashin mutuncina gaba gaba ya ke yi, ni inda zai kira Éin ma ai daÉi zan ji, don ko banza Æila sanadin rabuwarmu kenan, don na lura ba zan tsani Nazifi ba in ba rabuwa muka yi ba.
Wai duk yanda na kai da ÆoÆarin danne abinda ke tasowa daga can Æuryar zuciyata amma hakan ya faskara, ban taÉa tsammanin cin fuska irin wadda Nazifi yay min yau ba, kawai na fashe da azababben kuka mai Æaramin sauti saboda Rumana da ke Éakin, babu abunda na ke buÆata a wannan lokacin irin na samu kafaÉan da zan kwanatar da kaina in zubar da hawaye har a lallasheni, sai dai bani da kowa cikin wannan gidan, Allah ne kawai gata na, yau in ace ka haifa ma ko a wannan kafaÉar Éanka kayi kukanka duk da hawayen uwa rauni ne ga Æ´aÆ´anta. na jima ina kuka sosai kafin na iya rarrashin kaina. Nayi kuka, kukan da ban taÉa irinsa ba tun bayan da abubuwan su ka canja a gidan nan, ban san a dalilin auren nan kuma ya rayuwata zata ci gaba da tafiya ba.
bayan na idar da sallar isha'i na yi jugum ina ta faman tunani iri iri na game da rayuwar aurena, ya kuma zamu Æare zama da wacca zata shigo? Itama irinsu ce? Me aka faÉa mata game da ni? Na san dai ba zata taÉa zama irina ba. Rumtse ido nayi ina ji anata knocking Æofa na Æi tashi na buÉe kuma da alama aiken zuwan gayyar tsiyar ne ban san ko uwar da zan yi musu ba, ba zai wuce zancen abinci ba tunda naji ba su jima da dawowa ba, ni kuma a yanzu dai in ba uwata da ubana ba wallahi babu wanda ya isa ya sakani shiga kitchen na dafa masa abinci, don ko me gidan yau sai dai yaci a inda yake zuwa zance, ko in ya rage na rana ya ci.
Knocking Éin Æarshe ne ma Rumana tace,"Anty ni ce please ki buÉe min".
Ba zan iya Æin buÉe mata ba don Allah ya sani yarinyar ta shiga raina musamman da Allah yasa ta gane hanyar daidai, duk da ba wani yarda na gama yi da ita ba tunda jinin Yaya ne ke yawo a jikin