NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 68 of 97

". Iyam ta kyaɓe baki ta ce,"yau tana jin kanta da hayaƙi ina zata yi wani aiki, ai kawai ki kwaɓe ki shiga kiyi da kanki ko kuma ki tattara yara suyi, in ba haka ba kuma a san in da za'a kai a biya kuɗi su girka". Yaya ta kama masifa tana faɗin mene amfanina a gidan da sai an fidda kuɗi an kai wani waje girki, tayi min tatas ta ce in shiga kitchen in ɗora abinci mai sauƙi saboda masu zuwa ɗaukar kayan lefe na kan hanya. kamar mara galihu haka na wuce ina jiyota tana faɗawa Iyam wai Malam ya ce shi ba da yawunsa ba cikin ƙannensa mata wata taje kai lefe, shi ne Iyam ɗin ke faɗin to kar ya barsu suje ɗin itama ai tana da ƙannen kuma ta isa da su kuma sun isa zamewa Nazifi wakilai. Cous cous na ɗora jallof saboda nayi saurin gamawa gudun tashin hankalin Yaya, ba ƙaramin dauriya na ke ba wajen ɓoye halin da na ke neman shiga na azababben kishi. kafin la'asar gida ya cika da mutane, baƙin fuskar ba wasu da yawa ba ne, yawanci ƴan uwan Iyam ne sai ƙannen Malam su biyu Mama Laraba da Anty Huduriyya, sai ƙawayen Iyam da kafatanin ƴaƴanta mata, sai Ummaa itama da nata mutanen, tawagar dai duk ta marasa kirki ce, shiyasa dama tunda na dawo naga wannan gayyar kaina ya ɗaure na ke ta rayawa a raina ina cewa sai kace za'a yi biki, ashe ashe ile sace da ni shashasha ina ta harkokin gabana ban san miji zai danƙaro min kishiya ba. Abincin da na tafe kula da shi sai da suka cinye shi tass masu santi nayi masu kushewa nayi, ni dai ina kammala abubuwan da zan yi a ƙasa na haye sama saboda na daina jin ma habaice habaicen da su ke ta aikin yi tun zamansu falo. Tun da na shiga ɗaki gaba ɗaya na kasa sukuni, yayin da mamaki ya cika ni fal, na kuma kasa gasgata abin da ke faruwa a yau, kuka na ke rabza kamar an aiko min da mutuwar uwata, kukan da nake ba na komai ba ne face kukan abu mafi zafi a duniyata, kukan butulcewar Nazifi da gorinsa gami da ƙarin aurensa ba tare da na sani ba. ban taɓa zaton akwai ranar da Nazifi zai iya ƙaro aure ba, na dinƙa tuna irin yanda Nazifi ya ke matuƙar ƙaunata ada tunanin da kullum sai nayi, da irin gwagwarmayar da muka sha tare wanda zan ce ma na fisa. Na girgiza kai cikin tsananin danasani da nadamar damar da nayi sakaci da, haɗi da gangancin ɗora dukkan yardata akan ɗa namiji, ni sai a yau ma da batun kishiya ya tashi komai na farkon haɗuwata da shi ke zuwar min daki daki, kuma sai a yau naji ashe duk wasu wulaƙancinsa na baya ba komai ba ne ga ainihin wulaƙanci nan, domin akan wannan ne ya iya buɗe baki ya gaggaya min maganganu ma su ƙona zuciya har yana faɗin yana kunyar shigar da ni cikin jama'ar kunyarsa, banda wayewa! Ina zaune daɓas! satifiket ɗin sakandire!, ba zai zauna da mara haihuwa ba! hmmm lallai Nazifi. bayan kukana ya lafa na kwanta jiki a sanyaye, kaina jinsa na ke tamkar zai tsage, cikin tsananin damuwar da nake ciki naji ana ƙwanƙwasa ƙofar ɗakin, na miƙe cike da fargaba naje na buɗe, sai da na sauke wawiyar ajiyar zuciya ganin ba azababbiyar da nake tsammanin gani ba ce. murmushin yaƙe na saki ina cewa da Lubabatu,"to shigo ciki mana kin tsaya". ta girgiza kai tana faɗin,"a'a Anty Sa'ida ba zan ja miki magana ba, Yaya ce ta aiko ni wai ki sakko yanzu ki ga lefen amarya za'a tafi kaiwa". Nace,"ai ba sai na gani ba su kai kawai". Ta kamo hannuna tana cewa,"kiyi haƙuri kawai ki je kar akan wasu banzan kayan lefe a ci miki mutunci a gaban mutane". Kai na kaɗa na juya ciki na ɗauko mayafina na yafa muka sauka tare, lokacin ana ta firfito da akwatunan daga ɗakin Iyam, abin ya ɗaure min kai, ban taɓa sanin da ana haɗa wani lefe a ɗakinta ba, ko da yake sha'anin kuɗi ƙila a rana ɗaya aka haɗa su aka ajiye sai yau da za'a kai aka bani damar gani. Kujera ɗaya mu ka zauna ni da Lubabatu har lokacin tana riƙe da hannuna tana tausata a hankali gudun kar su jita su babbakata da masifa. tana ta min ƴan hira duk dan ƙarfafa min gwiwar in daure in nuna musu abun da su ke ta rawar kai akai ba komai ba ne a wajena. haka aka jere shegun akwatuna guda goma sha shidda kowacce akwatu aka buɗe maƙil take da kaya na alfarma, bakin kowa ya buɗe sai maganganu ake da irin ƙoƙarin da yay wajen haɗa kayan, ita kuma Yaya na faɗa musu ai wadda za'a auro ɗin ba ƴar ƙananan mutane ba ce, mahaifinta me kuɗi ne kuma itama yarinyar tana aikinta a wata babbar ma'aikata, har tana faɗar sanadin haɗuwar tasu a jirgi ne lokacin da ya dawo daga Dubai. Iyam ta ce,"wallahi ai sai yanzu ne Shalele zai yi aure, yarinyar ƴar boko ba cima zaune ba, gata lafiyayya don da suka je wannan gwaje gwajen da ake a asibiti an tabbatar da lafiya ƙalau take, ga kyau kamar ka saceta ka gudu fara tasss da ita, ƴar manyan gida ce fa don Babanta ma ba ƙasar nan yake zaune ba". Furucin na ta yay matuƙar ba ni mamaki, wato duk wanda ya san a yand
🏠