tsaya daga gefe, ta kalle ni da fuskar nan tata ta marasa mutuncin uwar miji ta ce,"hayaniya na jiyo tun daga Éakina lafiya?".
Ban yi magana ba nayi shiru saboda gaba Éaya sun mayar da ni banza wadda bata san abin da take ba. cikin raina na ce,_"hmm ko ba komai ana barin halak don kunya dai, kuma insha Allahu da sannu za ku gane kurenku"._
Æan nata ya ce da ita,"ki zauna".
Ta gama fahimtar abin da ke faruwa hakan yasa ta juyo gareni tana faÉin,"yauwa ki kwashe tarkacenki na Éakin kusa da matakalar bene, saboda baÆi za su fara zuwa gobe za su sauka anan, taron biki za'a fara a gidan ban sani ba ko kin sani, na san dai duk kinga ai na kusa da abun".
Ina jan yatsuna na ce,"na sani, amma Iyam Éakunan gidan da yawa ai da sai a duba wani, wancan Éin har yaushe na gama kwashe kayan cikinsa".
Ta jijjiga kai ta ce,"zan sa a fito miki da su tsakar falo in ya so kya kwashe su anan. Ai dama na san ke dai sai kin yi baÆin ciki da auren nan, to ba'a aure ke aka auro ki?, ko ba'a zama da kishiya uwar ubanki ta zauna da ita?, Ni fa dalilin mugun halinki yasa na ce kar a bari ki sani don ban san irin malaman da za ki bi ba, to koma dai menene Sa'ida aure Nazifi zai Æara ko za ki mutu sai dai ki mutu, akan me zai ta zama da juya irinki wacce ba'a san ranar haihuwarta ba?, kina zaune jaÉar sai cinye masa kuÉaÉe ki ke ba aikin fari balle na baÆi, kina Éauko dangi da Éai Éai kina a taimaka musu da abinyi, to dukiyar Éana ba zata lalace a taimakon Æ´an uwanki ba kawai, na san wannan dalilin ne ma yasa kika sha abin da zai hanaki haihuwa, kai muguntar Éan talaka ma bata yi ba wallahi".
Tayi shiru tana jan tsaki, ta mayar da kallonta ga Éanta ta ce,"kai kuma lusari ka bari mace zata Éaga maka hankali akan zaka Æara aure, ba ka gaya mata da izinin mahaifiyarka zaka Æara, mata nawa Allah ya halasta ma ka zama da su?, in ba zata iya ba ta kama gabanta mana wani ya riÆe mata Æafa ne ko akwai wanda ya rufe mata Æofa. ina dalili a hanaka auren mace mai ilimin zamani da wayewa wacce take haihuwa ba juya ba...".
Ba zan iya ci gaba da tsayuwa ina jin waÉannan bakaÆen kalaman ba, da sauri na fice a Éakin cikin fashewar kuka, ina zuwa parlo na tarar da Yayan Shago tsaye, da alama ya shiga Éakin Iyam ne ya tarar bata nan ya fito. Dauriyar tsayar da hawayena nayi ina gyara natsuwata na duÆa na gaida shi cikin girmamawa, ya amsa cikin tausayawa yanayin da ya ganni.
Murya a sanyaye nace da shi,"ka zauna mana yanzu zata fito".
Zama yay ni kuma na shiga kitchen na kawo masa ruwa da lemu. ko da na duÆa wajen ajiye tray Éin hannuna kasa Éagowa nayi kawai naji sabon kuka ya Æwace min, bakina na rawa na furta,"Yayan Shago yanzu abin da aka min anyi min adalci kenan?".
Shima cikin rashin jin daÉin faruwar lamarin ya ce,"ko kaÉan ba'ai miki adalci ba Sa'ida, ba Éoye miki auren kaÉai ba hatta kishiyar kanta da za'a miki wallahi ba'a kyauta miki ba indai kan dalilin da suke faÉa ne, babu irin shawarar da ban bawa Nazifi ba akan auren nan yaÆi jina sam, Æarshe ma kada baki yay ya faÉa min shawara kowacce iri ce in dai daga gareni ne ba ya so in riÆe girmana kawai. to kin san sha'anin mu maza in muna son abu idonmu rufewa yake musamman aka ce aure...amma kiyi haÆuri kinji dama ke Éin me haÆuri ce, ki barshi yayo aurensa ke kuma ki riÆe adu'a ki kuma tsarkake zuciyarki a zamantakewarku, kar ki taÉa bari zugar shaiÉan ko ta Æawaye su canja tunaninki, ki kama aurenki ki riÆe kar kishiya tayi silar rasa igiyoyin aurenki, idan da son samu ma Sa'ida ki Éan nemi sana'a za ta Éebi miki kewa".
Ya Æarasa maganar cikin alamar rarrashi, cikin Æ´aÆ´an Iyam Yayan Shago da Lubabatu na daban ne, su na da kyawun zuciya, duk abubuwan da ke ta faruwa su kaÉai ne abun duniya bai sauya kyakykyawan Éabi'arsu ba. Na sa hannu ina goge majinar hancina sannan na ce,"babu komai in sha Allahu zanyi haÆuri, zan jajirce kuma zan daure, na gode Yayan Shago".
Na miÆe daidai da fitowar Iyam, ta taho tana faÉin,"wani abun ta kitsa maka kenan, to Rabilu me za ka iya yi?, kai kam ai sai dai kallo, batun aji maganarka ma ai bata taso ba".
Maganganun da Iyam ke faÉa masa su ka taÉa zuciyata, tausayinsa ya kama ni, cikin yaranta maza shi ne babba amma saboda ba shi da kuÉi ya zama abin banza, babu ruwanta tai ta yaÉa masa magana, ta mayar da shi Æarami a cikin Æannensa, an mayarshi tamkar wani bare.
Allah ya kyauta na faÉa a raina ina barin wajen. "Keeee!". muryar Yaya ta faÉi hakan wanda tsakiyar kaina ma sai da ya amsa, na rumtse ido ina juyowa in kalleta cikin tsananin jin haushinta, yanzu sam sunana ma ta daina kira sai dai kee. Shiru nayi ta wurga min harara tana cewa,"me za ki je sama kiyi a wannan lokacin?". kafin na bata amsa ta kalli Iyam ta ce,"wannan yarinyar bata san da zuwan baÆi ba ne?, Na duba kitchen na ga babu abincin da za'a ba su