NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 66 of 97

ba ne ni wanda bai san ciwon kansa ba, ba zan mutu a haka ba bayan nayi aure tun da ƙuruciyata, ina son ganin jinina ɗa na cikina". Ya ƙarasa maganar yana jifana da wani irin kallo na wulaƙanci da nuna tsana. Sosai maganganunsa suka sosa zuciyata, ashe har akwai ranar da Nazifi zai wanke ni da irin munanan kalamai haka?, ashe har Nazifi zai iya ci min mutunci haka?, duk irin tarin sadaukarwar da na yi akansa a baya?, kuma har yana da bakin cewa banyi karatun arziƙi ba?, har yana da bakin ce mini ban da aiki sai in miƙa hannu a bani a bani?. Tunanina ya katse dalilin jin maganarsa a tsakar kaina yana sake cewa,"shekaru da yawa ba ki tsinana min komai ba, sannan ki sawa ranki cewar da ke kaɗai zan zauna tsabagen son kai irin na ki, wacece ke da har za ki ce ba za'ai miki kishiya ba, marar haihuwa ko wacca mijinta ke kunyar shiga da ita manyan wurare?, to ki sani dole zan auro mace ƴar boko, wacce ta waye, wacce zata haifa min yara, wacce zata taimaka min ba wai ni in ƙare a ɗaukar nauyinta da na ƴan uwanta ba...". "Kai Nazifi!". Na katse shi ta hanyar kiran sunansa kai tsaye, abin da ban taɓa ba. idauwana suka firfito waje cikin ɗaga murya na ce,"na gaji da cin fuska da rashin mutunci da gorin da ku ke min kai da ƴan uwanka a cikin gidan nan, ba kuma zan ci gaba da ɗauka ba, an kawo gejin da haƙurina ya ƙare, nima zan fito in ɗaga murya tamkar kowacce mace mai ƴanci, dama na sani ba don komai aka ƙulla munaƙisar wannan auren ba sai don a ƙara samun hanyar cin zarafina, to kuwa kun yi kaɗan gaba ɗayanku, kawai! akan ban haihu ba?, akan bani da aikin yi?, akan ka taimaki ƴan uwana?...ehen haihuwa ni ce zan bawa kaina?, karatun kuma ta silar wa nayi asararsa?, to idan ka manta bari na tuna maka, ban da ƙaddarar da ta haɗa aurena da kai sanin kanka ne da yanzu na zama abar kwatance fiye da kai ɗin nan. kuma har kana faɗin ban da wayewa, kai ɗin yaushe ka waye Nazifi?, sanin kanka ne ko a shiga aji na fika, kai ina naka satifiket ɗin da ka ke da zarafin raina na wani?, har yaushe ka fara jin turancin?, Ohhh laifina shi ne kawo maka ƴan uwana da nayi akan ka taimaka musu da jari?, Ko kuma fifita aurenka da nayi akan ilimin bokona?, karatun da iyayena suka ci burinsa akaina, amma nasa ƙafa na shure duk don saboda kai da farin cikinka, har yanzu akwai ciwon rashin karatuna a zuciyar mahaifina, ka sani ba wai baka sani ba, taimakon mene ban maka ba a sanda ƴan uwanka suka kasa taimaka maka, amma daga ƙarshe in rasa sakamakon da zan samu daga wurinka sai na tozarci da gori? In kasa sanin za ka ƙara aure tsabar bana da mutunci a idonka...to Nazifi ka ƙara aura, ka kawo duk wacce za ka kawo, kuma ba zaka taɓa burgeni ba sai ka auro ɗiyar mangofak, sai ka auro ɗiyar masu kuɗin duk duniya, sai ka auro wacce zata cika maka gidan nan da ƴaƴa, sai ka auro wacce ita take rabawa dukka ma'aikatan duniyar nan office tukunna in san da gaske kayi aure". na ƙyasta yatsuna na ce,"amma ka rubuta ka ce na faɗa maka wataran, wallahi da sannu za ka girbi abunda ka shuka, domin sai na kai ƙararka wurin Allah". Hankalinsa kwance, a nutse ya ke kallona yace,"kin gama haukar taki?". yay dakiyar faɗa don shi kansa ya san baida gaskiya ya kuma matuƙar mamakina ayau kamar yanda ni kaina nayi mamakin kaina. kuma saboda ya ƙara ci min fuska ya ce,"Idan kin gama sai ki shirya gobe dangin matata za su zo suyi jeren kayan arziƙi, iyayenta su ne suka siya mata kayan ɗaki ba da na mijinta zata yi amfani ba, kuma kar inji kar in gani, idan ba haka ba kuwa za ki sha mamakina...za ki iya fice min daga ɗaki". Na tsaya kallonsa babu ko ƙifce, lallai masu iya magana sun yi gaskiya da suka ce mutum mugun ice, mutum butulu, Namiji Ƙayar Ruwa, Namiji ƙanin ajali, Namiji rigar ƙaya. wato Nazifi ya manta duk wani faɗi tashi da nayi da wuya ba daɗi duk akansa kafin zuwan matsayin da yake kai yanzu, ina tare da shi tun baida ko sisi, na zauna da shi cikin tsananin talaucinsa ban guje shi ba, kullum cikin ƙoƙarin in faranta masa na ke in kwantar masa da hankalin damuwa da yake yi, amma shi ne yanzu saboda dukiya ta samu zai juya min baya, har da ƙaro aure yana min gorin kayan ɗaki da iyayen aba su siya min ba a sanda zamu dawo sabon gida, kai jama'a anya duniya da amana?, kai babu!, domin in akwai da ruwa bai dafa kifi ba. Na danne zuciyata ina ɓoye bala'in raunina da ke neman karkaryewa a gabansa, naja dogon tsaki na juya zan bar masa ɗakin saboda zuciyata ingiza ni take yi akan in aikata ba daidai ba. Ina shirin fita mahaifiyarsa ta danno kai, na yi saurin komowa da baya domin bata hanya, haka ta tsira yanzu duk sanda ta so shigowa take kai tsaye babu neman izini balle shayin a yacca zata shigo ta tarar da mu. Na sa kai zan fita tayi saurin dakatar da ni da cewa,"korar ki na yi?". Nace,"a'a Iyam da ma zan fita ɗin ne". "To dawo". Na dawo na
🏠