ganin gabana sosai, cikin matsanancin tashin hankali da kaÉuwa na faÉa Éakinsa.
Zaune na same shi akan cushion ya miÆe Æafafu kamar ba wanda na fita na bari ya fito a wanka ba, rediyo na kusa da shi yana sauraren tafsir a freedom radio, hannunsa kuma riÆe yake da littafin MuwaÉÉa yana karantawa. A hankali na Æarasa gabansa na tsaya, kallonsa nake yi tun daga tsakiyan kai har tafin Æafarsa, nafi Æarfin minti biyu tsaye a gabansa amma tamkar bai san da shigowar tawa ba, Æafafuna suka gaza ci gaba da Éaukar tsayuwata, na duÆe a gabansa ina dire gwiwoyina a bisa carpet. Sai a sannan ya Éago ido yay min kallo Éaya ya Éauke, can kuma sai ya Æara dubana da kyau sannan ya buÉi baki yace,"lafiya?".
kai na shiga girgiza masa na gaza furta komai. tsaki yaja na takaici yana sakko da Æafafunsa Æasa fuska a Éaure ya ce,"sarai kin san bana son wannan halin ko, mene ya faru?".
Hannuna da ke aikin karkarwa na Éago na miÆa masa katin Éaurin auren ina cewa,"tabbacin wannan na ke son sani Hubbi".
Bai karÉa ba bacin Æwayar idonsa da ya tsayar akan fuskata, kallona yake yi tamkar yau ne ya fara ganina a duniyarsa, kukan da nake ta dauriyar riÆewa ya Æwace min ina haÉa hannayena wajen cewa,"Don Allah, don Allah don Annabi Hubbi ka Æaryata abin da nake gani, don Allah kar ka bar kunnuwana su jiye abin da zuciyata ba zata iya Éauka ba...".
Katin ya karÉa a hannuna ya ajiye a gefensa, ya tari numfashina da faÉin,"raya sunnar ma'aikin shi ne zuciyarki ba zata iya Éauka ba?, Jayayya za ki da lamarin da ubangiji ya rubuta?".
Na zuÆi numfashi ina jujjuya kaina na ce,"ban isa ba, ban kai ba, baiwarsa ce ni ban isa nayi jayayya da lamarinsa ba, kawai ni dai ina so ka tabbatar min ne".
"Rubutun da kika gani a jiki bai ishe ki shaida ba?".
"Bai ishe ni ba Hubbi, sai naji daga bakinka tukunna, sai naji daga bakin da bai taÉa min Æarya ba balle yaudara".
Æakin ya Éauki shiru, bakinsa ya furzar da iska, sautin muryarsa ya fito a hankali da cewa,"Æwarai aure zan yi, zan kawo miki abokiyar zama, na kuma zaÉi Éoye miki ne saboda tsarina ne hakan, dama na faÉa miki ai zan tabbatar da na ba ki mamaki".
Furucin nasa yasa na zabura na miÆe da sauri wanda har ban san yanda aka yi na tsinci hannuna a Æirjinsa ba. Æirjina ya shiga dukan tara tara ina jin zuciyata tamkar ana soyata da dalma, cikin raina ina nanata kalmar AURE da ABOKIYAR ZAMA.
Muryata ta fito cikin sanyi da rauni ina cewa,"da gaske aure za ka Æara?, Hubbi aure ba tare da na sani ba?, ace ban da masaniyar mijina zai aure sai da ya rage saura kwana biyu?, yanzun ma da ban gani ba shikenan sai dai inga ana shigo da amarya?, dama ana haka da gaske?, Hubbi komai nayi maka ban cancanci hukunci ta irin wannan sigar ba, ko Éaya ban cancanta ba, me yasa zaka Æara aure?, biyayyar me na gaza yi maka? duk irin haÆurin da na ke, duk irin kauda kan da na ke yi".
Na Æarasa maganar ina girgiza kaina cikin matsanancin Æunar rai tare da binsa da kallon mamaki matuÆa. Na Æara faÉin,"Don Allah in wani laifi nayi maka ka faÉa min wallahi na Éauka alÆawarin zan gyara amma kar ka hukunta ni ta hanyar yi min kishiya".
Maganar tawa ta katse, na duÆar da kaina Æasa tare da damÆar gaban rigarsa da kyau. "Kayi haÆuri Hubbi, ka yafe min laifin da na aikata maka bisa rashin sani, in ka Æara aure ka zalunce ni, haÆiÆa ka zalunce ni...".
Ya katse ni a tsawa ce,"Dakata!, Æarin aure ba yana nufin lallai sai kin min laifi tukunna zan yi ba, ra'ayina ne in zauna da adadin matan da na ke so, ba'a ce lallai da ke kaÉai zan zauna ba, don haka ka da ki nemi ki haramta abin da Allah ya halasta min...kuma da kike maganar na zalunce ki ta ina na zalunce ki Éin?, ke idan ma ba ki gode min kin ce nayi adalci ba ai kin zama butulu, duk irin haÆurin da nayi na zama da ke a haka tsawon shekaru masu yawa?, amma ba ki ko ji kunyar kallona kina tambayar akan me yasa zan Æara aure ba, to dama ta ya kike tunanin zanci gaba da zama da ke ke Éaya alhalin ina so naga jinina, ke in da na san ma ba kya haihuwa zan aureki ne?, kin zo kawai kin zauna daÉas ban da ci da kasayarwa babu abin da kika sani, komai sai dai ayi miki, sai aukin a baki a baki ko kunya ba kya ji, wallahi tallahi Sa'ida ban da wata darajar ko kaÉan zama da ke ya sire min, shekaru da yawa kin kasa wayewa, kin kasa zama Æ´ar gari ki koyi soyayyar zamani, cikin kanki empty babu turanci, duk da dama ba wani karatun arziÆi kika yi ba...ga matan abokaina nan duk Æ´an boko ko ina shiga su ke da su, amma ni har kunya na ke yi idan na tuna tawa matar satifiket Éin sakandire ne da ita, Éan aikin zamanin nan na zaman office babu sai shiga kitchen Éin banza da wofi, ciki ya iya Éaukar abinci amma ya kasa Éaukar Éa balle har a haife, to ni ba zan iya ci gaba da zama da wadda bata haihuwa ba, ba Éan iska