re min kafin daga bisani kowacce ta Éauke ido tana faman yatsine fuska kamar sunga kashi.
maganar da na riskesu suna yi naji sun koma yi ÆasaÆasa, dama can banji me suke cewa ba balle na buÆaci jin sauran zantukan. to kan me ma suke tsammanin zan damu ba yan ba dani ake maganar ba? Ni Éin kuma ba munafuka ba?.
Sai da zan fita a Éakin kuma naga Ummaa ta fito daga banÉaki, da murmushina na tsuguna ina gaida ita amma itama sai naga tayi min yanda su Yaya suka min, wato dai amsawa a daÆile ba don ta so ba.
kawai sai naji kaina ya Éaure, na farko zuwansu gidan kaf Éinsu kamar za'ai wani taro? na biyu Ummaa ba haka ta saba min ba dan ko satin da ya wuce naje gidan kuma fuskarta sake ba alamun kwai matsala tsakanina da ita.
fita nayi daga Éakin cikin sanyin gwiwa, karo muka yi da su Fati ita da matar Æanin Hubbi Sulaiman, yanda su ka kalleni su ka watsar haka nima na kallesu na watsar, dama ita Zalihan cikin facalolina da ita ne bama wani Éasawa tun can da.
Da sauri nayi gaba dan jikina bani ya ke wannan taron na su kaman da wata a Æasa, ga kuma kallon banzan da na lura duk suna bina dashi, kaman sun yo zuga ne don cin mutuncina yacca aka saba. ina shiga Éaki kawai nayi wankana na shirya na fita, kasa sauka nayi don sam bana so na sauka mu kuma haÉuwa da wani cikinsu, ga dole ma sai na sauka naje na sameshi tunda na ga motarsa tabbacin ya dawo kenan, Allah yasa sun yi girki sun ba shi su hutar da ni.
ni dai addu'ata Allah yasa zuwan na su ba shi da alaÆa da ni dan gaskiya tuni na gama gajiya da wannan tashe tashen hankulan da komai yaÆi ci yaÆi cinyewa, kwanciyar hankali na ke buÆata a yanzu kam. kawai dai na sa a raina yau duk wacca tayi min a cikinsu tabbas zan rama ba zan Æyale ba ko a gaban uwarta ko a gaban Æanin na su.
ko da na shiga Éakinsa yana banÉaki, na zauna jiransa sai ga yara sun shigo suna faÉin za su tafi islamiya. jiran fitowarsa su ka yi saboda kuÉin littafan da za su karÉa. bayan ya fito ya ce na Éauka rigarsa na Éau kuÉin na ba su, sai dai ko da na duba babu hakan yasa shi cewa na Éauka maÆullin motarsa,"cikin wajen da na ke zuba takardu akwai kuÉi ki ba su".
na ce,"nawa?"
su ka ce,"kowa dubu biyu aka ce Abba".
Na miÆe muka fita tare da su, bayan na basu kuÉin na raka su bakin gate su ka wuce kana na dawo motar don Éauko hulunansa da ya ce za'a kai wanki. dama a kujerar baya ya ke ajiye su, na tattaro su gaba Éaya don kusan ya saka su dukka. sai dai ina shirin fitowa daga motar wani abu ya Éauki hankalina da yasa ni ware idona akai gaba Éaya. lokaci guda idanuwana su ka disashe, ganina ya fara ÆoÆarin Éaukewa, haka na daina jin sautin komai a kunnuwana, lokaci guda ÆwaÆwalwata ta tsaya cak da aiki, ganin ina neman gaza shaÆar iska da fitar numfashi nayi saurin fito da kaina daga cikin motar. Sai dai ba ni da wani iko da motsa jikina domin kuwa jini ya tsaya da gudanar da aikinsa balle na sami damar Éaga Æafa na bar wurin saboda tsantsar tashin hankalin da na shiga.
Yanda jikina ke karkarwa daidai yake da kaÉawar guguwa a tsakiyar rana, haka yanda na ke jin dummm a cikin ÆoÆon kaina tamkar saukar tsawa a tsakiyar duhun dare ne, allon Æirjina kuwa girgiza ya ke yana neman barin Æirjina ya tarwatse a Æasa wanwar, ban san ta ya ba, ban san ya za'ai ba, amma tabbas bana tunanin zan iya gasgata abin da ÆwaÆwalwata ta karanta a jikin katin Éaurin auren hannuna, balle kuma har zuciya da gangar jiki su iya Éaukan lamarin.
Idanuwana na rumtse gam na Æ´an sakanni kafin na shiga buÉe su a hankali, har yanzun dai a disashe su ke bana gani sosai, don haka kawai sai na ke kallon invitation card Éin ina Æara kallonsa, na kasa sakinsa ya kuma Æi faÉuwa daga hannuna duk da irin karkarwar da hannayen nawa ke yi. ta cikin ruwan hawayen da su ka Éan taru a idona na ke Æara bin rubutun jiki da kallo, so na ke na aro hankali a wani wajen tukunna in Æara karanta abin da ke jiki, bana tsammani a yanzu akwai hankali a tattare da ni kam, don in akwai ba zan karantowa kaina wannan baÆar musibar ba, Aure fa, Aure guda ba abin wasa ba, auren da ban san da batunsa ba, inaa da sake, ko da mijina zai Æara aure to ba ta wannan hanyar wulaÆantawar ba, rashin darajtawa har ina haka?.
_hasbunallahu wani'imal wakil._, zuciyata ta ambata, tabbas babu Æarya a rubutun da na gani, Aure Hubbi zai Æara, saura kwana biyu Éaurin aurensa, amma ban sani ba, wadda na ke da hakki akan sanin hakan.
wani wahaltaccen yawu ya wuce ta maÆoshina da Æyar, ya sauka a cikina da babu komai face baÆar yunwar da ke ÆwaÆulata tun ranar jiya, kayan cikin nawa suka amsa, na rumtse ido saboda raÉaÉin wahala. wucewar sakan Éaya, biyu, ubangiji ya bani aron Æwari na samu damar Éaga Æafata na bar bakin motar ba tare da ko na maida murfin na rufe ba, haka na bar compound na tafi bana iya