da lamarin plazar da ya faÉa min, tabbas aka rusheta ba Æaramin asara zai yi ba, don duk ita ce jagaban kasuwancinsa. nayi nisa a wankin sai ga Fati da kaya a hannu, tana zuwa tsabar rashin mutunci ta watso min su cikin ruwan wankin, raina ya Æuntata na waiga a fusace sai zuciyata ta taushe ni kawai na Æyaleta, don yanzu ina magana tashin hankali zai biyo baya.
"ki wanke min fuskar da hannayen da kyau".
ta ce da ni cikin gadara da nuna rashin kunya, ban ce mata komai ba har ta fita. kafin na gama wankin har na gama girki dama saboda haka nayi dabarar haÉa aikin biyu, kar in kai dare ban gama girki ba Iyam ta Éaga min hankali da cewar na bar yara da yunwa, tayi nata mai gidanma yay nasa.
Nayi sa'a kayan su ka bushe da wuri. na Éebo shanyar na linke na ajiye su akan kujerar falo, ina jiran nayi wanka na Éan huta sai na zo na goge, kafin na bar wajen sai ga Iyam ta fito ta zo tana cewa,"gugar kuma fa bayan ga wuta nan kika wani linkafesu kika yasar da su anan koma ki kai min Éaki. Ko ajiye min kika yi na zo na goge da kaina?".
"A'a Iyam dama ina so ne zuwa Éan ajima sai na goge".
"mene wani anjima saboda dai ki bar min kaya da Æura, dama ai ba so kike ba kika wanke, saboda Fati ta kai miki hijabi biyu shine har da yi mata tsaki ke da ba kya Æaunar zaman lafiya, ai ba ita ta saka ki wankin ba ni ce nan, me kike yi a gidan Sa'ida in ba a saka ki aiki ba nufinki sai dai kici ki kasayar ki kwanta? kuma yarinyar nan kina gani daga makaranta ta dawo tana so ta huta ta ina zata yi wanki, anfanin duk wata hidimar gida na matar gida ne. don haka Malama zauna ki goge su kar nefar su Éauke wutarsu, gugar solar nan ba wani kyau take ba, ko kuwa haka kike so na dinÆa saka kaya a yamutse ana zagar min Éa, gwara ma ni akan yaran".
Tunda na zauna gugar ban tashi ba sai da aka yi kiran magriba, na Éebi waÉanda na goge na kai Éakinta na ce mata zan yi sallah tukunna sai in ci gaba. ba dai ta ce min Æala ba na fito na wuce Éakina, sai alokacin nayi wanka na shirya cikin doguwar rigar atamfa. jikina banda ciwo babu abunda yake yi min, na kwanta ina ta aikin nishi, na manta rabon da na ce na huta na minti biyar tunda Iyam ta zo. Rumana ta shigo Éakin zatonta bacci na ke yi don sai da ta zo daidai kaina kana ta shiga taÉani a hankali tana cewa,"Anty Abbaa yana kira".
Na kalleta da gajiyayyun idona, zama tayi kusa da ni tare da taÉa wuyana tana cewa,"Anty ba ki da lafiya?".
na murmusa kuncina na ce,"lafiyata lau Rumana, gajiya ce kawai".
kanta ta kwanto bisa kafaÉata tare da riÆe hannuna. "Anty don Allah kiyi haÆuri da duk abunda muka yi miki, ni dai wallahi na daina, yanzu tausayinki na ke ji kuma ina sonki".
Na shafa kanta ina cewa,"Anty ba ta fushi da yaranta, nima ina sonki Allah yay miki albarka".
tashi nayi na kama hannunta muka fita, tana min surutun in ce Abbansu ya kaini asibiti idona baya da lafiya kuma duk na rame, hmm ni yanzu na masa magana ma ai ce zai yi je ki chemist.
Æakinsa na iske shi, ni sai da ya kira ni ma na tuna da saÆon da ya bari. wani kallo ya watsa min yana cewa,"ke ba kya taÉa son a zauna lafiya, ya za'ai na bada saÆo tun Éazu sai yanzu muyi waya da mata tace min ba a kai mata ba".
"kayi haÆuri ba wai haka kawai ba ne. kaima ce kayi idan na gama aiki kuma har yanzun da kake faÉan ba gamawa nayi ba".
"Sa'ida wai mene matsalarki? Me ya ke damunki ne da kika bar Éaukar maganata da muhimmanci? na fa gaji da wannan banzan halin na ki da kika tsira".
"Na ce kayi haÆuri ko, gugar Iyam zan Æarasa babu yawa ina kammalawa sai in je, ba zai yiwu na aje nata aikin akan naka ba".
bai ce min komai ba ya sadda kai Æasa yana duba wasu takardu da ke gabansa, soyayyarsa na ji ta cika min rai, bana so yay zaton ko daina sonsa nayi, Æaunarsa na nan yanda take a raina, duk irin baÆin ciki da Éacin ran da ya Æunsa min tuni na cire a raina na yafe masa, duk da shekaranjiya naji zafin zagin da yay min a gaban Æ´an uwansa akan sun zo ban san da zuwansu ba ni kuma na kulle store, da kuma abunda yay min akan Fatin Éazu. shi dai ko rantsewa nayi ba zan kaffara ba a yanzu ba ya min ko da kwatan son da yayi min a ba ya, rabonsa da faÉa min wani kalaman soyayya tun ranar da buÆatar kansa ta kawo shi kafin ya kai Æarata gidanmu. ni kam nayi alkawari nayi sai na rama ko da kaso Éaya ne cikin kason Éacin ran da ya saka ni ciki, kuma na lura ta banzatar da shi da lamarinsa kawai zan rama don hakan na masa ciwo ko bai faÉa ba.
"kayi haÆuri kaji Hubbi". na faÉa ina tsugunawa a gabansa ganin yanda fuskarsa ta nuna tsantsar Éacin rai.
bai kalle ni ba ya ce,"no kar ki damu zan yi maganin abun, idan kina ganin hanyar da kika Éauka ita ce daidai a gareki nima zan san abun yi, kije kici gaba da Éaukar zugar duk me zuga ki, kiyi yacca kike so Sa'ida amma zan tabbatar da na matuÆar ba ki mamaki wallahi". ya faÉa yana jijjiga kai.
ts