NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 61 of 97

aurin barin wajen ina nufar dining, abincin na zuba mata na ce da ita ga shi nan, kamar bata jini ba haka tayi banza da ni. ina niyyar barin wajen sai ga shi ya fito daga ɗaki, Iyam na ce masa,"a'a da ce tayi ba zata bawa Fati abinci ba na ce to bara na kiraka ƙila taji maganarka tunda ni ban isa ba". kallona yayi yana cewa,"bisa wanne dalili za ki hanata abinci? wai ke ki hora mutum da yunwa daɗi ya ke miki ne? wato abunda na ɗanɗana miki kwanaki bai ishe ki ba?". Iyam ta katse shi,"kaga duk ba wannan ba, Fati dai gata can zaune ma kallonta take, kallon dole don dawowarta kenan yunwa take ji, ka ce kawai ta bata abinci". "ki bata abincinta karnki ƙara hana wani nawa abinci tunda ba ke kike siyowa ba, don kin dafa ba yana nufin kina da iko da shi ba ne". muryana na shaida damuwa na ce,"ban fa ce ba zan bata ba, ce nayi taje ta ɗiba. kuma ga shi na zuba mata na ce ta zo ta ɗauka tayi min shiru". "ohh in magana ki ƙaryata". cewar Iyam "ni ba ƙaryata ki nayi ba amma yanda kika ce ai ba haka ba ne...". maganata ce ta katse dalilin saukar marin da naji a fuskata. "duk ranar da mahaifiyata ta ƙara magana kika nemi ki ja akai sai na mugun saɓa miki, uwata fa tana faɗa kina cewa ba haka ba, me kike nufi in ba ƙaryatata ba". idona ya ciko da hawaye ina dafe da kuncina. na jiyo shi yana cewa da Fati. "ke kuma zo ki ɗauki abincin". ta marairaice tana cewa,"Yaya Ƙarami ƙafata ce naji ciwo bana iya takawa inama shirin ce maka zanje asibiti ne". ya waigo ya kalle ni daidai lokacin da na ke niyyar barin wajen murya a sama ya ce,"na gama magana ne da za ki bar wajen?". na dakata ba tare da na juyo ba. "ki ɗauki abincinta ki kai mata kina ganin ai tana da lalura". na danne kukana na mayar da hawayena, na ɗauki abincin na je na miƙa mata ta karɓa tana ƙunshe dariya, cikin raina na ce Allah ya saka min. Barinsa wajen na nufi bene nima, gaba ɗaya na manta da batun wani wanki, sai munafukar yarinyar ce take cewa da Iyam wai na tafi na bar mata kaya. ita kuma ta ce ta ƙyaleta da ni zamu zuba. ni kam ban tsaya ba nayi ɗaki ina jin babu daɗi a raina, zama nayi saboda raina ya ɗan yi sanyi amma har ga Allah na jima ban ji ɓacin rai ba irin na yau. to ni wankinma bai cin min rai ba kamar zuba abincin in kai mata kuma ta karɓa tana min dariya, in wanki ne dama tunda Iyam ta dawo ta hana badawa da guga tace masa gatan yayi min yawa komai sai a kashe kuɗi ayi min banda aiki sai kwanciya, don haka bisa umarninta kar a ƙara bayar da wanki a gidan, kayan wankin guda nawa su ke da ni ba zan wanke ba sai dai ai ta ɓarnar da kuɗi ni babu tausayi saboda ban san wahalar da yake sha ba kafin ya samesu, to in dinga ƙwarara jiki ina motsawa, haka ma fa firij tasa an ɗauke na kitchen an kai ɗakinta, duk su lemo da nama in ya kawo sai yanda ta bani, duk sona da maltina yanzu sai haƙura na ke yi saboda idan naje karɓa ta dinga mita kenan. Da rana ina cikin wankin sai ga shi ya shigo yana faɗin,"wanne irin rashin hankali ne wannan? Kin bar tukunya zata ƙone kin taho wani aikin na daban, ki bari ki fara kammalawa da ɗaya mana, wannan ai ba dabara ba ce. kin san yanda gas ke kara tsada kuwa, wallahi za ki ja na koma ajiye miki buhun gawayi". Da alama bai san wankin na waye ba shiyasa, Na tsame hannuna a ruwan da sauri, ta gefensa na wuce na nufi kitchen ɗin, ina zuwa na tadda ruwan zafin ko tafasa bai yi ba, ni dai dama nayi mamaki domin kuwa nayi ƙasa da wutar sosai, kai bawa dai da komai kayi sai ya zama laifi, nufinsa da yay maganar in tsaya masa bayani ya hasala ya gaggaya min babu daɗi. ina kitchen ɗin ya dawo ya sameni, ya ce in fito falo na iske shi, sauri sauri na wanke shinkafar na zuba na fita, yana tsaye hannayensa harɗe ta baya, hannun kujera na zauna ina ce masa,"gani". kuɗi ya miƙo min tare da cewa,"akwai abunda ya taso min na ke so a taya ni da adu'a, ga wannan dubu talatin ne, idan kin gama aikin sai ki leƙa gidan Malama Hadiza, akwai buhun shinkafa da wake na bayar akai gidan, idan kin je sai ki tambayeta adadin kuɗin da ake buƙata, jallof ne za'ai da ƙosai da kunu ayi sadaƙa". ina kallonsa na kai hannu na karɓa na ce,"Allah ya karɓa ya biya buƙata". Ko amsa ni bai yi ba, ya nemi kujera ya zauna ni dai na bi sa da kallo don naga kamar yana cikin damuwa. sannu a hankali na ce da shi,"ko wani abu ne ke faruwa?". ba tare da ya kalle ni ba ya ce,"plazar cikin gari gwamnati ke son rushewa wai filinta ne". na ce,"to subhanallahi, Allah ya saita al'amura, kar ka damu insha Allahu zata dubeku ta bar muku abinku, adu'a ce kawai zata yi aiki". ya amsa da,"ilahee ajib". na buɗi baki da niyyar in wata maganar wayarsa tayi ƙara, ido ya ɗago yana kallona bayan ya gama kallon screen ɗin wayar, a hankali yace,"ki bani wuri". tashi nayi na bar masa wajen na koma bakin ayyukana, sai dai tuni na shiga damuwa
🏠