eni sun rushe cikin Æ´an watanni, halinta da Éabi'unta sun sauya, ban san laifin me na mata ba haka kawai ta Éora dukkan fushinta da karan tsanarta a kaina, ko bikin da aka yi watan da ya wuce cewa tayi kowa ya zauna ya huta ni a tattara min duka ayyuka, haka na zama kamar wata Æ´ar aiki ko baiwa, nayi ta fama da uban wanke wanken kwanukan taron biki, shara kuwa har sai da na ranÆwafa saboda mugun riÆewar da bayana yay, da an tashi rabon abincin zata kira sunana ta yarfo min zagi tace in Éauka in bi mutane in raba musu, ban da damar zama ko na sakanni, hatta kashin Æ´aÆ´a da wankan yaran baÆin kunya duk ni ce, haka tasa aka wareni a gefe wai banda amfani, ta mayarni kaman wata jaÉa, na sha baÆin ciki da takaici a bikin nan, har sai da na dinÆa jin kaman in gudu gidanmu, sai dai ban isa ba YaShaik tsab zai takeni idan yaji cewar nayi yaji.
Su kan su Æ´an bikin sai da suka Éinka tausaya min wasu na cewa ya kamata a barni in huta, in huta tunda surukan gidan gamu nan fal, to amma ban isa ba, zaman hutawata daidai yake da zaman hutu a gidan iyayena tun da har Yaya na fushi da ni. To ni kam yanzu mugun tsoron Yaya nake yi, Wallahi a baya da zarar ta ganni take washe baki ta buÉe min hannaye in tafi jikinta ta rungume ni, amma yanzu har gwara naga hukuma su ce kamani suka zo yi akan ganinta, ganin ma ace a gidana.
Harar da ta banka min ita tasa na razana na Æarasa gaban kujera cike da furgicin ganin fuskarta babu annuri. haka na rakuÉe tsugune kamar an jijjiga Éera a buta, ji nayi gaba Éaya ta cika falon saboda irin matan nan ne zabga zabga masu Æiba, duk da idona a Æasa yake amma ina jin irin banzan kallon da take jifana da shi, tana aikin kyaÉe baki kamar taga amai, ganin na buÉe baki cikin fusata ta katse ni.
"LumÉu-lumÉu wutar ÆaiÆayi, tsiga tsiyau kazar matsiyata, wato saboda ba ki da mutunci, ba ki da tarbiya, ba ki da Éa'a, ba ki san darajar na gaba da ke ba, ni kike jira in gaishe ki...me kika taka da har kike ganinki daidai da ni?, ko saboda an Éauko ki daga tsiya an rufa asirinki cikin daula shiyasa kike ganin kinfi kowa?, aikin banza shafa lalle a Éuwawu uban me ma kika aje a gidan da har za ki gadara. to ko shi me gidan yayi kaÉan in zo gidansa ya wulaÆanta ni wallahi, ke ga Æ´ar iska kina so ki nuna min dangin mijinki mutanen banza ne a wurinki, shiyasa har kina ji ina kwaÉa sallama ki ka barni a shanye, wato in gaji in bushe in kama gabana, to idan ba ki sani ba ki sani, ni mai sakawa ya sallameki ne kuma kin sallamu wallahi, ko idan danginki ne za ki wulaÆanta su har haka?, wato sai ni Yayar mijinki Æ´ar banza tazo miki gida ba za ki amsa sallamarta ba ko?".
Jiki na rawa na girgiza mata kai alamar a'a ina faÉin,"duk ba haka ba ne Yaya, don Allah don Annabi kiyi haÆuri, wallahi sam banji sallamar ba ina aiki...".
Daka min tsawa tayi tana katse sauran maganata, cikin faÉa sosai take cewa,"dalla rufe min baki munafuka algunguma makira mara tsoron Allah, aikin uban me kike yi a gidan nan banda kici ki kwanta, to idan ma aikin ne fina yayi da ba za ki iya katse kome ne ba, ballantana babu aikin da kike kina kwance sharaf kaman kayan tsinuwa, rashin mutunci dai irin na matan yau shi ya hanaki fitowa".
Na haÉiye abin da ke tokare a maÆoshina ina karanto hasbunallahu, cikin sadda kai Æasa nace,"don Allah kiyi haÆuri hakan ba zai Æara faruwa ba in sha Allahu, ki yafe min Yaya don Allah".
Sai na miÆe tsaye jiki babu Æwarin kirki na shiga gyara kan kujerar da yake a gyaransa nace,"Bismilla Yaya ki zauna".
Ta maimaita,"in zauna?...Sa'ida saboda raini da cin fuska ni kike kallo kina ce min in zauna saboda ga jarababba ta isheki da hayaniya, Yo Sa'ida har wacece ke a gidan nan da sai kin ban izini akan abu, ko tunaninki umarninki nake jira shiyasa nake tsaye har wa yanzu?, Ehh lallai yarinyar nan kin riÆa, wuyanki ya isa a yanka, raini da cin fuska mai muni har haka?, ina Yayar mijinki za ki wulaÆanta ni?, to uwar me kike gadara da shi a cikin gidan nan?, tun da aka auro ki wacce tsiyar kika aje?, shekara takwas babu Éatan wata balle Éari, kin kasa ajiye ko tsinke sai aikin ci da kasayarwa, kuma a hakan kike neman gadara da gida, to ke a wa?".
Sai tayi shiru tana bin ko ina na cikin falon da kallo,"ina Nazifin yake?".
"Ya fita".
"Ya fita ina?, Æarya za ki min, shi dama yana fita ne ya wannan lokacin?"
Nace,"ai in ya fita magriba sai anyi isha'i yake dawowa, kuma yauma da mota ya fita ba lallai nan kusa zai dawo ba".
Zagayowa tayi ta zauna kan kujera, ta Éora Æafa Éaya kan Éaya tana girgiza su, tana ta kaÉa kai. Na wuce kitchen na Éauko ruwa da lemu na kawo mata, a kofi na tsiyaya ina ce mata ga shi, na duÆa gefen Æafafunta, cikin taushin murya nace da ita.
"Yaya don Allah ina neman afuwar laifin da nayi".
Ba ta dai ce min komai ba har wucewar wasu sakanni, kafin ta kalle ni cikin zafin rai tace,"walla